Monday, December 28, 2009

SHEKARA DAYA BAYAN KISAN PALASDINAWA: INA AKA KWANA?

Harin bama bamai da israela ta kaddamar a karshen watan disamban shekarar 2008 zuwa farkon shekarar 2009 a yankin zirin Gaza ya cika shekara daya yanzu haka ba tare da an gurfanar da wadanda suke da hannu a cikan wannan mummunar ta’asar ba a kotun hukunta masu laifukan yaki na duniya. Wannan fitina da ta afku abin ayi tir da kuma Allah wadai da ita ne. Domin kuwa yakin ya jefa palasdinawa cikin halin kaka nakayi na rashin abinci, ruwan sha, wutar lantarki da dai sauransu baya ga hasaran rayuka da dukiyoyi, duk a sakamakon amfani da makamai masu kazamin guba da bani yahudun sukayi. Hatta harkar sadarwa ta yanke a lokacin saboda rashin wutan lantarki, wadanda kuma suka jikkata a lokacin basu samun cikakken kula a asibiti ba, wanda hakan yasa suka mutu daga karshe. Wannan danyen aiki da Isra’ila ta aikata a Zirin Gaza ya kai intaha, domin kuwa yayi sandiyyar maida yara da dama marayu, wasu matan sun rasa mazajensu, a wani bangaren kuma maza sun rasa matayensu da ‘ya ‘yansu, gidajen jama’a sun salwanta da kuma dukiyoyi inda jama’a da dama suka rika gararanba a gari suna neman wajen tsugunawa duk a sanadiyyar wannan kazamin fada.
Wani abin ban haushi da takaici shine yadda majalisar dinkin duniya ta nuna halin ko inkula ga mummunar ta’adin da Isra’ila ta aikatawa palasdinawa, tayi gum taki cewa komai. Hakan kuwa bai dace ba domin kuwa majalisar dinkin duniya tana da cikakken ikon tsawatarwa Isra’ila don dakatar da lugudan wuta da harin bama bamai da takaiwa palasdinawa, amma taki yin hakan. Yanzu ya fito fili kuma kowa ya fahimta, musamman ma ganin yadda yar sandan duniya wato kasar amuruka taki cewa uffan a lokacin da Isra’ila ta rika yima palasdinawa kisan kiyashi, da kuma halin ko oho da majalisar dinkin duniya ta nuna cewa suna da ra’ayi akan lamarin. Domin kuwa, hakkin majalisar dinkin duniya ne ta sasanta kasashen cikin lumana da diflomaciyya, amman taki yin hakan ta zurawa Isra’ila ido ta ci karenta ba babbaka a Zirin Gaza. Akwai bukatan majalisar dinkin duniya ta sake salon yadda take tafiyar da lammuranta, ma’ana ta rikayin adalci da kuma cin gashin kanta ba sai ta jira wata kasa ta bata umurni ba. Kodayake, kin daukan mataki da majalisar tayi a kan Isra’ila wani umurni ne daga Amurka a karkashin mulkin kama karya na George Bush. Domin kuwa Amurka ce ke tafiyar da harkokin majalisar dinkin duniya, har ila yau hedkwatar majalisar na kasar Amurka, don haka shiyasa Amurka ke taka rawar da taga dama sakamakon sake da nuna rashin iya aiki da majalisar dinkin duniya tayi.
Yin biris kuwa da kasashen larabawa sukayi kan wannan lamari, suka ki taimakawa palasdinawa don tsoron kada Amurka tasa masu takunkumi ko ta kirasu yan ta’adda wallahi yazamo babban abin kunya da kuma hasara garesu. Domin kuwa Isra’ila ba ita kadai ta aikata wannan kisan kiyashin da tayi a zirin Gaza ba, tasamu taimako amma su larabawa sunkasa taimakawa yan uwansu don neman suna a gun Amurka. Tabbasa dole a jinjinawa kasashen masar da faransa kan namijin kokarin da sukayi lokacin da yakin yaki ci yaki cinyewa, domin kuwa sune sukayi kokari wajen ganin an kawo karshen wannan zibda jini da akayi. Hakika kiran dakatar da ruwan bama bamai a zirin Gaza da kasashen biyu sukayi a lokacin da Isra’ila ke faman lugudan wuta a yankin zirin Gaza, dakuma kiran a zauna a teburin shawarwari abin a yaba masu ne matuka gaya.Domin kuwa hakan ya haifar da da mai idon inda Isra’ila ta tsagaita wannan danyen aiki data kwashe kwana da kwanaki tana aikatawa a zirin Gaza. Babban abin ban mamaki shine yadda majalisar dinkin duniya da kuma wadanda ke da alhakin gurfanar da masu laifin yaki a kotun duniya sukayi kememe sukaki sammacin wadanda suka jagoranci wannan ta’asa a Zirin Gaza, amman sai gashi a watan maris na wannan shekarar ta 2009 kotun masu laifukan yaki dake birnin Hague tayi sammacin shugaban kasar Sudan Omar Hassan Al-bashir ya gurfana a gabanta don amsa laifukan kisan kare dangi a Sudan da ake zargin wai yana da hannu dumu dumu a cikin. Sanin kowa ne, sai dai aki fadin gaskiya, rikicin kasar Sudan bakowa ya haifar dashi ba illa kasar Amurka, sakamakon rashin samun damar ta taka rawa kan al’amurar man fetur da allah ya albarkaci kasar Sudan dashi.
To babbar ayar tambaya itace, shin majalisar dinkin duniya da kotun kasa da kasa dake hukunta msau laifukan yaki na tsoron cafkewa da kuma gurfanan da wadanda suka aikata kisan kare dangi a zirin Gaza ne? ko kuwa su ‘yan lele ne baza a yi sammacinsu don su fuskanci shari’a ba? Wani hujja suke dashi nakin gurfanar da wadannan azzalumai a gaban kuliya? Shin ta hakane za a rika kawo karshen rashin jituwa tsakanin kasashen masu gaba da juna ta kin ladabtar da mai laifi don ya zama darasi ga ‘yan baya? Wani mataki majalisar dinkin duniya take dauka a halin yanzu kan ci gaba da shiga yankin palasdinawa da bani yahudu keyi don ganin wannan mummunar rikici tsakanin bangarorin biyu bai sake afkuwa ba? Wadannan kadan ne daga cikin dimbobin tambayoyin day a kamata majalisar dinkin duniya ta amsa don sanin matsayin al’ummar palasdinawa a idonta dama duniya baki daya.
Hakika al’ummar palasdinawa sun shiga wani hali na kunci, rashi da kuma tausayi duk sakamakon wannan bala’in da Isra’ila ta jefasu ciki. Don haka muna tayasu addu’ar allah ya dada karesu da karewarsa, ya tsaresu da tsarewarsa, ya kuma fidda su daga cikin wannan halin kunci da suka samu kansu a cikin skekara daya da ta wuce tare da fatan Allah SWT zai mayarmasu da dukiyoyin da sukayi asara a wannan lokaci.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.

Friday, December 18, 2009

FOUR YEARS REMEBRANCE...

December 18, 2005 will remain unforgettable to our family. It was on the early hours of that fateful day that our beloved father Justice Abdul-Hadi Dabo left this sinful world to rest in the bosom of Allah. Four years has gone now, but you are still fresh in our memory as if it was just yesterday you departed.
You came to earth with nothing and left with nothing, but rather left a legacy that others resisted. You triumphed over hard work which has been our watchword.
The eyes cannot see you, the nose cannot sense you, the mouth neither can talk to you, but what about the ears, they both cannot hear you...
Prayers cannot awaken you from the deep slumber you have fallen; it will only elevate you to the most high and bury your past earthly mistakes.
It's our prayers that the Almighty Allah will have mercy on your soul, together with all the muslims who died before you right from the time of prophet Adam (A.S). May He afford us the will and patience to pray for them and bless us with those who will pray for us when we die...
May Allah's infinite mercy shower you an infinitum forgiveness of your past mistakes. May He also grant you the eternal rest. Ameen... Continue to rest in peace till we meet in ALJANNA FIRDAUSI...

Friday, December 4, 2009

YABO GA RUNDUNAR YAN SANDAN JIHAR KADUNA

Yabon gwani akace ya zama dole, kuma kowa yayi aiki na gari dole a yaba masa. Hakan yasa ya zama dole a jinjina ma hukumar ‘yan sandan Jihar Kaduna karkashin jagoranci kwamishinan ‘yan sanda agogo sarkin aiki Alhaji Tambari Yabo Muhammed, ganin yadda jami’an shi ke aiki tukuru ba dare ba rana don ganin sun fatattaki miyagun da ke addabar jihar Kaduna dakuma kare rayuka da dukiyar al’ummar ta jihar Kaduna.
Murkushe shirin fashi da makami a jajibirin sallah da ta gabata a hanyoyin Kaduna zuwa Birnin Gwari da kuma Kaduna zuwa Zaria da ‘yan sanda sukayi abin a yaba masu ne matuka, domin kuwa baicin daukin gaggawa da jami’an suka kawo da Allah kadai yasan irin barnar da ‘yan fashin zasu yi a hanyoyin ganin cewa jama’a da dama na ribibin komawa kauyukansu don yin sallah tare da iyalansu dakuma ‘yan uwa da abokan arziki. Harkar tsaro dai a jihar Kaduna kullum sai kara karuwa takeyi saboda kyakkyawar kulawa da maigirma gwaman jihar Alhaji Namadi Sambo yaba fannin tsaro tare da samar da kayan aiki. Domin kuwa jihar Kaduna ta zarce sauran takwarorinta a fannin tsaro, don haka ya zama dole a yabama wannan hubbasa da mai girma gwamna keyi don ganin tsaro ya inganta a jihar Kaduna. Suma ‘yan sanda dole a dada yaba masu ganin yadda suka dage wajen dakule duk wata hatsaniya da shirin aikin ‘yan zauna gari banza da bata gari keyi don ganin Jihar Kaduna ta zama abin koyi ga suaran jihohi.
Don haka ya kamata hukumomin da abin ya rataya a kansu su dada samar da kayan aiki ga jami’an tsaro don suji dadin sauke nauyin daya rataya a kansu a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, kuma a ci gaba da basu horo tare da turasu kwasa kwasai cikin gida da kasashen ketare don dada gogewa a aikinsu da kuma yin gogayya da takwarorinsu na waje. Sukuma jama’an gari suci gaba da ba ‘yan sanda hadin kai a duk lokacin da bukatar hakan ta taso tare da basu muhimman bayanai kan duk wani mutum da basu gamsu da take takensa ba. Da fatan sauran jihohi zasuyi koyi da jihar Kaduna don samar da cikakken tsaro a jihohinsu.

Sunday, November 22, 2009

Hukumar EFCC: Ba girin girin ba....


Shugabar hukumar EFCC madam faida waziri ta fito tayi wasu maganganu da suka ja hankalin ‘yan kasar nan da dama kan malam Nuhu Ribadu, ciki kuwa hardani. Duk da cewa banso cewa komai ba kan maganganun da tayi, amman ya zama dole don ganin yadda ta rika hawa tanasauka gami da kushe duk wani irin nasara da malam Nuhu Ribadu ya samu lokacin aikinsa. A sanin ‘yan Nijeriya dai babba da yaro, tsoho da matashi ya san cewa hukumar EFCC na yaki ne da masu almubazzaranci da ta’annati da dukiyar kasa ne. yaki da masu wawushe dukiyar talakawa zuwa aljihunansu yana daya daga cikin ayyukan hukumar na EFCC kamar yadda kowa ya sani. Don haka yin aiki akasin haka ya sabama manufofin wannan hukumar.
Amma da dukkan alamu wannan hukuma ta EFCC a halin yanzu bata aikinta yadda ya kamata, domin kuwa shugabar hukumar tayi wani maganganu wadanda suka bada mamaki matuka, domin inda wani ne yayi wannan Magana ba ita shugabar EFCC dinba, to a iya cewa saboda baisan aikin hukumar ta EFCC ne yasa haka. Madam Farida Waziri ta fito fili ta shaidawa duniya a wani shiri da akayi da ita a sashen hausa na muryra Amurka mai suna sai bango ya tsage, ranar 19-11-2009 cewa “ muna neman malam Nuhu Ribadu ne saboda ya je yana bata min suna da sunan Nijeriya a kasashen waje saboda yanajin haushina, kuma yace duk shugabannin Nijeriya masu rashawa ne……..” wannan dalilai ne yasa a cewar madam Waziri ya zama tilas ga hukumarta ta damke malam Nuhu Ribadu in har sunyi tozali das hi. Amman da akayi mata tambayar cewa mai zaisa baza su tuhumi Ibrahim Lamorde ba, tsohon shugaban hukumar ta EFCC daya gaji malam Nuhu Ribadu kafin zuwan ita madam Waziri, gogar taku sai ta sake kada baki tace “ ai shi Lamorde ba za mu kamashi ba ko mu bincikeshi ba domin yayi shiru bai zagi kowa ba, shikuwa Ribadu sai bata min suna kawai yakeyi domin an bani mukaminsa” wadannan kalamai na Madam Waziri cike suke da ban mamaki, domin kuwa bai kamace ta a matsayinta na wacce tasan aikin taba (in harta sanin ma kenan) ta fito tana irin wadannan maganganun cewa hukumarta zata kama Nuhu Ribadu ne kan wai yana bata mata suna! Wannan bayanai nata na nuni da cewa kenan zasu kama Ribadu ba kan yana da laifin cin hanci da rashawa ba ke nan. To, abin tambaya a nan shine, shin hukumar EFCC ta daina yaki da cin hanci da rashawa ne ta koma farauta masu batama Nijeriya suna a kasashen duniya? Lallai wannan tambaya ne da madam Waziri ya kamata ta amsashi don ‘yan Nijeriya su san alkiblar da EFCC ta nufa yanzu idan ta canza ne daga damkewa da cafko masu karya tattalin arzikin kasa.
Har ila yau, madam Waziri tayi ikirarin cewa malam Nuhu Ribadu ya shirya manakisan hanasu yin wani taro da sukayi a can kasar Amurka. Don Allah jama’a kuji irin wannan Magana fa, ta yaya mutumin daba dan kasar Amurka ba zaiyi tattaki zuwa Amurka har ya tara yan zauna gari banza don su hana madam Waziri da sauran tawagarta gudanar da taronsu? Amurka fa bata da ‘yan zauna gari banza kamar yadda ake dasu a Nijeriya, idan ma akwaisu ta ya Ribadu zai iya tarasu domin su hana wannan taron da madam Waziri tayi ikirarin cewa yayi makarkashiyar hanawa?
Ya kamata madam Waziri taji tsoron Allah tayi aiki tsakani da Allah, idan mutum baici ba bai shaba, to kada a rika yi masa bita da kulli. Kada a dauki tsanan duniyannan a daura masa idan anga yana samun ci gaba a rayuwarsa. Ba zai kyautu ba in har madam Waziri tayi amfani da kujeranta don musgunama malam Nuhu Ribadu kan laifin da baiji ba bai gani ba. Gaskiya dai daya ne, kuma daga kinta sai bata. Kowa a kasarnan yasan irin yadda wannan bawan Allah Ribadu ya sadaukar da kansa ya bautawa kasarna, don haka in har baza’a sakamasa da alhairi ko a yaba masa ba, to bai kamata a tsine masa ba ko a musguna masa ba. Wallahi kasarnan na bukatar irin su Ribadu don kaiwa ga tudun mun tsira, amman saboda yanayin azzaluman shugabannin da muke dasu wadanda basa son gaskiya hakan yasa da wuya a yanzu a sake ba Ribadu dammar ya zo yaci gaba da bautawa kasarnan kamar yadda yayi a baya don samun ci gaba. Domin kuwa tun bayar barinsa hukumar EFCC, har yanzu babu wasu kwararan nasarori da aka samu kaarkashin hukumar kamar yadda aka samu a lokacinsa.
Hakika ya kamata madam Waziri ta zauna tayi ma kanta karatun natsuwa ta kuma rika banbance tsakanin gaskiya da karya a al’amuran aikinta na shugabar EFCC. Dan gane kuma da bayanin da tayi cewa Ribadu na da matsala da hukumar da’ar ma’aikata, to ai wannan ba lamari ne da ya shafeta ba domin ba’a hukumarta abin yake ba, don haka shiru shine nata ta barshi su karata da hukumar da’ar ma aikata. Har yanzu ‘yan Nijeriya na kaunar Ribadu saboda yadda ya sadaukar da kansa yayi aiki tukuru, kuma suna fatan watan wata rana gaskiya zatayi halinta, duk wannan bita da kulli da akeyi masa zata kare. Fatarsu shine kasarnan ta samu shugabanni na gari masu son gaskiya wadanda tafiyarsu zatayi daidai da irin tafiyar su malam Nuhu Ribadu adali kuma haziki, kuma Allah ya kubutar da shi daga azzaluman mutanen da suka sashi a gaba.
Allah yayi mana jagorancin a dukkan ayyukanmu na alhairi. Kuma yaci gaba da karemu gami da tsaremu dayi mana Katanga ga dukkan abin da muke shakkunsa na zahiri da badili, amin.

Friday, November 20, 2009

NADA GWAMNA IBRAHIM SHEKARAU A MATSAYIN SARDAUNAN KANO: RIBAR SIYASA?


Tuwon girma akace miyan nama inji masu iya Magana, kuma yabon gwani akace ya zama dole. Nadin mai girma Gwamnan Kano mallam Ibrahim Shekarau a matsayin sardaunan Kano da mai martaba sarkin Kano Alhaji Dakta Ado Bayero yayi masa ya jawo ce-ce-ku-ce a ciki da wajen jihar inda wasu ke alas an barka da wannan saraudar da kaba limamin adaidaita sahu, wasu kuwa akasin hakan ne ke fitowa daga bakinsu.
Alal hakika mai girma sarkin Kano Alhaji Dakta Ado Bayero yayi kyakkyawar hange wajen zaben Mallam Ibrahim Shekarau a matsayin sardaunan Kano kuma a lokacin daya dace, musamman ma ganin yadda shi sardaunan na Kano ke ci gaba da ayyukan raya jihar gami da gina al’ummarta ta fannoni daban daban. Alal misali gina madatsan ruwa na tamburawa da akayi wanda duk nahiyar afrika babu kamarsa ya sawwake radadin azabar rashin ruwa da mutanen Kano suka dade suna fama dashi na shekara da shekarau, samar da aikin yi ga matasa, bada tallafi ga nakasassu, ga kuma fadada hanyoyin jihar da akeyi a halin yanzu don rage cunkoso a titunan garin da kuma inganta hanyoyin sufuri, sai kuma uwa uba wutar lantarki wanda yanzu haka a makwanni uku da suka wuce jihar Kano tafara samun cikakken hasken wutar lantarki a ko wane rana ba kakkautawa wanda hakan zai dada karfafa aikin masana’antu, da dai sauran ayyukan ci gaban jihar da dama.
Sadaukar da kai da yin aiki tukuru ba tare da gajiyawa ba da mai girma gwamna Mallam Ibrahin Shekarau keyi tare da baiwa kowa hakkinsa ba tare da nuna banbancin addini, siyasa ko kabila ba, gami da gina al’umma tare da yin ayyuka don ci gaban jihar Kano dama Kasa baki daya sune suka kai ga baiwa limamin adaidaita sahu sarautar sardaunan Kano. Domin kuwa, hatta jihohin kasar nan sun yaba da ayyukan gina kasa da mai girma gwamna Shekarau keyi wanda hakan yasa aka bashi sarautar Onwa Na-Etiri oha 1 na Ehaalumono a kudancin kasar nan. A zahirin gaskiya, mai girma gwamnan kano kuma limamin adaidaita sahu ya cancanci a kirasa da magajin sardaunan sokoto, domin kuwa kyawawan halayensa na kishin jama’arsa da son ci gabansu yayi daidai dana marigayi sardaunan sokoto Alhaji Sir Ahamadu Bello.
Sanin kowa ne Jihar Kano tun bayan kirkirota bata samu cigaban da ta samu a shekaru shida da suka wuce ba karkashin jagorancin adalin gwamna Dakta Ibrahim Shekarau. Wannan kuwa wani babban nasara ne da al’ummar jihar Kano ya kamata suyi tunkaho dashi, kuma suyi godiya ga Allah madaukakin Sarki daya tarfawa garinsu nono ya albarkace su da gwamna mai son cigabansu musamman ma ganin yadda a kullum sai kara kwasan ribar dimokuradiyya sukeyi ba kakkautawa. Don haka babu abinda mai girma gwamna Mallam Dakta Ibrahim Shekarau limamin adaidaita sahu, garkuwan Ilimi, sardaunan Kano, Onwa Na-Etiri oha 1 na Ehaalumono, kuma magajin sardaunan sokoto ke bukata face ayi masa addu’ar Allah yaja kwana kuma ya biya masa dukkan bukatunsa na alkhairi da yasa a gaba kuma ya basa ikon sauke nauyin da ya rataya a kansa tare kuma da Addu’ar ALLAH YA KAI DAMO GA HARAWA! Amin.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.

Wednesday, October 7, 2009

BETWEEN ASUU AND THE FEDERAL GOVERNMENT


The continuation of eye lingering between the federal government and ASUU is very annoying, because governments on their own part are not showing any concern about the issue. It’s quite unfortunate that education sector is not given all the necessary attention and this is due to the fact that the children of UNE (United Nigerian Elite) are schooling abroad, and only the less privilege ones are suffering from this strike. Imagine our counterparts that go to Dubai, Malaysia, India and so on are acquiring a degree in just 3 to 4 years while here in Nigeria you spent almost 6 to 7 years to acquire the same degree due to this kind of strike and so on. It’s high time for this government to look into the needs of these people so as to bring an end to this long term strike in order to allow students continue with their studies. Also they (government) should know that any country that lacks qualitative and standard education, that country will never develop in any way….Allah ya sauke!

Thursday, October 1, 2009

NIGERIA @ 49: WHO'S TO BLAME?


I wonder why many nigerians are celebrating the 49th years of independence when things in the country are getting worst day by day. foristance, our universities are on strike for the fast 3 months and govermnent are not showing any concern about it, imagine our president going to saudia to commission a university as a special guest while his own universities are closed over a minor issue wchich can be solved within a week.it is better we celebrate 49 years of power failure, insecurity (becouse kidnapping is becoming rampant in this country), fallen standard of education, unemployment, collapse of industries,poor medical facilities,...to mention but few. no hope for the masses, everything is getting out of hand. but do we fold our hands and keep watching for things to continue like this? what devidend did nigerians derived from the so called 49 years of independence? up to now we can not differentiate between yestarday and tomorrow, for God sake is there any cause for celebration? our leaders have totally failed in all round. it's high time now for our leaders to wake from their deep slumber before it becomes too late for them to cry

Sunday, September 27, 2009

BIRNIN KANO YA DAUKI BAKUNCIN TARON GIZAGO KARO NA FARRKO


A jiya asabar ne 26/9/09 akayi taron gizago karon farko na kasa baki daya a birin kano. Assalamu alaikum yan uwa maza da mata na wanna dandali, ina mai mika godiya ta da farinciki gareku baki daya da kuka sami damar halartar babban taron wannan kulob namu na GIZAGO SOCIAL AND CULTURAL. hakika yadda maza da mata mambobin wannan kungiya suka amsa kira tareda masu mata fatan alahiri sukayi cincirondo zuwa wannan taro kwansu da kwarkwatansu daga sassa daban daban na kasar nan, wata kila ma harda makwabta abin farin cikine kwarai da gaske, kuma wata alamace ta cimma burinmu.
godiya ta musamman ga Dr. Bala Muahammed, sheik aminu daurawa, malam bashir yahuza malumfashi, aburrahaman haruna(dodo) da sauran manayan baki maza da mata da sukaa sami zarafin halartar wannan taro duk kuwa da irin aikin da ke gabansu. bani da ingantacciyar kalmar da zan iya gode maku illa ince allah yasaka da alhairi kuma yabar zumunci amin. Suma wadanda suka gabatar da shirin, Ado ahmad gidan dabino da Mk Adam muna jinjina masu sosai. haka shima malam nura adamau yayi namijin kokarin yadda ya rinka kaiwa da komowa, ga su shafi'u imam, da dai sauran mutane da dama.
haku suma manbobin kungiyar nan kun cancanci yabo, musamman ma malam Mk Adam, agogo sarkin aiki, buldoza, aiki ga maiyinka, hakika yayi kokari domin tun kwana uku kafin buki ya iso kano don ganin shirye shirye ya kankama yadda ya kamata. itama shugabar mata ta kasa hajiya aisha lawal, da mataimakiyar ma'aji haiya huawa ahmed sunyi aiki kwarai da gaske, Allah ya saka da alhairi. sauran mambobi maza da mata daga dukkan jihohin da suka iso wanna taron ina maku godiya ta musamman da fatan kowa ya koma gidansa lafiya.
ina mai farin cikin shaida maku cewa in Allah ya yarda taro na gaba kamar yadda nayi bayani tun farko, za'ayi sane na garin gwamna, cibiyar ilimi, kasar balaraben sarki, bugu da kari sarkin sarakuna.
nagode Allah yasaka da alhairi, ya bar zumunci. wassalam
MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
NATIONAL CHAIRMAN,
GIZAGO SOCIAL AND CULTURAL CLUB
080-36397682
http://anguwarfatikaonline.blogspot.com

Tuesday, July 28, 2009

TABARBAREWAR ILIMI A NIJERIYA.



TABARBAREWAR ILIMI A NIJERIYA.:ummul aba isin yajin aikin jami'o'i



Yau a Nijeriya, harkan Ilimi ya shiga halin ko in kula da kaka ni kanyi saboda irin rikon sakainar kashi da rashin bashi muhimmanci da wadanda alhakin abun ya rataya a kansu.Akwai abin takaici kwarai da gaske idan mutum yayi la'akari da irin halin kuncin da wasu mutane suke ciki wadanda rayuwarsu ke da matukar tasiri ga kasarmu, amma aka kyalesu cikin bakar wahala sakamakon wani tsari na mulkin mallaka da ba kowa ke cin gajiyarsa ba. Wadannan mutane sun kasance tsani da mutum kan taka har ya kai ga wani matsayi a rayuwarsa. har ila yau wadannan mutane suke dasa harsashin ganin fadi-tashin da mutum keyi a rayuwarsa har ya cimma wani matsayi ko nasara a rayuwa.



wadannan mutane ba wasu bane illa malaman makaranta wadanda dan abin da suke samu bai taka kara ya karya ba in aka kwatantashi da irin aikinsu na sadaukarwa. Matsayin malaman makaranta ga ginin kasa da al'umma al'amari ne da ba ya misaltuwa. Komai matsayin mutum, duk yadda ya kai da daukaka a rayuwa sai da yabi ta hanyar malamai kafin ya cimma wannan matsayi.



yajin gama gari da malaman jami'o'in kasar nan keyi abin kunya ne ga wannan gwamnatin karkashin jagorancin Alhaji Umaru Musa Yar'adua, wanda shima tsohon malamin makaranta ne amman yayi biris da bukatunsu, yaki yaji kukansu balle ayi tunanin share masu hawayensu.

yau a kasarnan, dalibai kan shafe shekara takwas suna karatun da ya kamata ace anyisa a shekara hudu saboda yajin aiki da malam kanshiga lokaci zuwa lokaci, yayinda takwarorin karatunsu da kanje kasar malaysia ko Amurka kan share shekara uku kacal don samun digiri daidai da na nijeriya da akan kwashe shekara takwas ana yinsa sakamakon yajin aikin. malamin makaranta ba'a dauke shi a bakin komai ba a Nijeriya, bashi da daraja a idon shugabanni da su kansu daliban, duk kuwa da cewa duk wani shugaba dake tun kaho a kasar nan dama duniya baki daya malamin makaranta shine tsanin farko da yabi har ya kai ga wannan matsayi da yake.





Wannan karara ya nuna hujjar da malaman jami'o'i ke da ita ta shiga yajin aiki saboda irin halin ko-in-kula da gwamnatocin da aka yi a kasar nan suka rika nunawa game da batun kyautata rayuwar malaman. Don gwamnatin 'Yar'aduwa ma tafi kowacce nuna halin ko-oho game da mummunan matsayin da malaman jami'o'i ke ciki, sai tafi mayar da hankali ga biyawa 'yan majalisu burinsu na wasoso akan dukiyar jama'a. Yayin da aka yarjewa dan majalisa ya rika kwasar Naira miliyan goma (N10,000,000) a kowane wata, wani malamin jami'an idan kaji albashinsa sai ka rike baki kana salati, don kuwa abin ba'a cewa komai. koda yake ba komai ya haifar da rikon saikanar kashi da shugannin keyiwa harkar ilimin kasar nan ba face cewa 'ya 'yan su basa karatu a kasar nan, sun turasu kasashen waje suna biyamasu kudin karatun nasu da dukiyar al'umma.



Ilimi dai shine kashin bayan ci gaban al'umma, amma wadansu na kokarin gurguntashi saboda tsabar keta. Ya kamata Gwanmatin Yar'adua ta gaggauta daukan mataki don kawo karshen wannan yajin aikin gama gari da jami'o'in kasar nan keyi don baiwa dalibai samun zarafin kammala karatunsu a kan lokaci.

Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukanmu na alhairi, amin.

YAWAN MUTUWAR AURE: WAKE DA LAIFI?

HAKIKA

Monday, July 13, 2009

CE-CE KU CE KAN ZIYARAR OBAMA ZUWA GHANA

Tun bayan da shugaba Barack Obama na Amurka ya bayya aniyarsa ta kai ziyara zuwa kasar Ghana, al'ummar Nijeriya keta ce-ku-ce kan wannan ziyarar ganin Obama bai zabi Nijeriya ba duk kuwa da dimbin tattalin arzikin da kasar keda shi fiye da Ghana, sai kuma uwa uba kallon da akeyima kasar (Nijeriya) a matsayin uwa maba da mama a nahiyar afrika.



Sanin kowane bawai wani abu yasa obama ya zabi zuwa Ghana ba face yadda suke mutuntawa da kuma girmama dimokuradiyya. Hakan ya fito filine bayan halastacce kuma tsarkakakken zaben gama gari na kasar, inda jam’iyar hamayya ta sami rinjaye kan jam’iyar dake mulki kuma aka tabbatar mata da nasarar da ta samu (lamarinda yasha banban da Nijeriya). Rashin yin magudin zabe da satar kuri’u da Ghana batayi ba shi ya kara tabbatar mata da mutunci a idon duniya da kuma nuna yadda kasar ta rungumi akidar dimokuradiyya ta ingantacciyar hanya. Wadan nan sune manyan dalilan da yasa shugaba Obama ya zabi zuwa kasar Ghana bai dauki Nijeriya ba (kasar da magudin zabe, satar kuri’u, zaben kaci-baka-ciba ,baka-ciba-kaci,,cin hanci da rashawa da rashin baiwa yan kasa hakkokinsu ya zama abin ado). Don haka, banga dalilin da zaisa al’ummar Nijeriya musammanma mukarraban gwamnati su rika tada muryoyinsu kan wannan ziyarar da Obama ya kai Ghana ba, domin kuwa kamar yadda Obama yace “amurka zata dada karfafa zumunci da kuma taimakon ta ga kasashen da suka rungumi dimokuradiyya ta halastaccen hanya”. Abin tambaya a nan shine,musamman ma ga wadanda suke korafin cewa Obama yaki zuwa Nijeriya- wai mulkin dimokuradiyya akeyi a Nijeria?



Hakika wannan ziyarar da obama ya kai Ghana ya zama kalu bale ga Nijeriya, kuma hannunka mai sanda ne ga sauran kasashe irin Nijeriya wadanda suka maida mulki kamar gadon gidansu da kuma hawa madafun iko ta ko wani irin hanya. In har Nijeriya na son Obama ya kawo irin wannan ziyarar daya kai Ghana to saifa ta inganta hanyoyin zabe ba tare da yin magudiba, rungumar dimokuradiyya ta halastacciyar hanya, baiwa yan kasa hakkokinsu, sakinmara ga jam’iyyun adawa da kafofin yada labarai masu zaman kansu da dai sauransu. Tabbas yaU Ghana ta zama farin wata sha kallo kuma zakaran gwajin dafi a nahiyar afrika. Ghana ta ciri tuta wajen cigaban al’ummarta duk kuwa da cewa kasar tana daya daga cikin kasashen dage baya wajen tattalin arziki a nahiyar afrika, amma saboda da shugabanni masu kishin ci gaban kasar da take dashi yasa a yau sunfi Nijeriya ci gaba ta ko wani hanya amman banda hanyar magudin zabe da satar dukiyan talakawa. Kalu balenku shugabannin Nijeriya.

Allah yai mana jagoranci a dukkan ayyukan mu na alhairi, amin.

Monday, June 8, 2009

ELEVEN YEARS REMEBRANCE OF LATE GEN. SANI ABACHA.


Today June 8,2009, is exactly 11years that Almighty Allah deemed it fit to take back the life of Gen. Sani Abacha.

The death of General Abacha is a great lost not only to his family, but to the entire nation-because he was a great patriot and a brave general who dedicated himself to the service of his country.

history will always remember general Abacha as a hero who did his best for his country. we pray to Almighty Allah to continue to give the family, friends and well wishers the fortitude to bear the irreplaceable lost.

We also pray that your gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.

Abacha we are still with you in spirit and we love you, but God loves you more.

Thursday, June 4, 2009

HEART BREAK !!!


I've been thru hell
Trying to get you out of my life
But after all this time
I can't help myself but miss you.

Now, all alone
Thinking of my life once again
My past is passing me by
I feel a lot of pains
I shed a lot of tears
As I remember all we’ve been through.

You’re once a dream that came true
An illusion that turned to reality
But suddenly, things turned differently.

You give me sleepless night
Coz you keep staying on my mind
I can’t stop crying
Coz I’m missing you…

My life will never be the same again
Now that you’re gone
I will be trapped in this loneliness forever.

I thought this was a poem I would never have to write
I hope my tongue was something I could bite
But realized it’s just something I cannot do
I’m still so in Love with you, after all this time.

Your heart is now with someone else
I’m so jealous
I can’t bear these bullets anymore
The pain of losing you is still fresh in my brain
Every day my heart feels the pain
Will things ever be same again?...

I want you to know I’m heartbroken
I want you to know I’m hurt
But please….
I don’t want you to look at the tears in my eyes as I cry…

Wednesday, May 20, 2009

TEN YEARS OF CIVILIAN RULE..


Its now exactly ten years since the return of civilian rule in Nigeria, but Nigerians have not witness any development over these years. things are even getting more worst than before: no constant electricity power supply, poor roads,falling standards of education, our hospitals are in critical conditions, economic meltdown, nigerian stock exchange is not looking good and there is a problem of unemployment in the country. this adminstaration is nothing but a set back, becouse one of the so called 7-points agenda have not been actualised.
Yar’adua should as a matter of urgency address these issues once and for all to avoid further escalation of the problem. It is very unfortunate that despite the vast natural resources that God in his infinite mercy endow Nigeria with, the resources are mismanaged by a very few and the masses are left in squalor and poverty. The national cake is being looted and squandered by few out of Whims and Fancies to the detriment of the majority.
Anyway, Nigerians, happy ten years of civilian rule not democracy!

Thursday, May 7, 2009

Jang Vs Fula

FULANI SUMA YAN NIGERIA NE:

Budaddiyar wasika ga gwamna Jonah Jang
zaman lafiya da ci gaban ko wace kasa ko al'umma ya dangana ne ga yadda shugabanninsu ke tafiyar da mulkin su ba tare da nuna banbanci kabila, addini ko siyasa ba. Yin hakane kawai zai kawo ci gaban kasa da kuma al’umma. Hukunci da gwamnatin jihar filato ta dauka na Koran Fulani a jihar wani mataki ne da ka iya tada zaune tsaye, musamman ma ganin yadda jihar tayi kaurin suna kan rikice-rikice kama daga na kabilanci, addini, siyasa da dai sauransu.
Sanin kowa ne dokar kasa taba duk dan kasa damar zama inda yake so ba tare da tsangwama ba. Don haka ya kamata gwamna Jang ya gane cewa fulanin filato na da ‘yancin zama a ko ina cikin kasarnan kamar yadda sauran kabilu ke zaune a jihar ba tare da an takura masu ba. Har yanzu dai matsalar dan kasa da bako bata mutu a filato ba, don kuwa in ba haka ba babu dalilin da za’ace za’a kori fulanin dake filato a halin yanzu. Filato, jihar da ake yi mata take da jihar zaman lafiya, yawon bude ido da shakatawa yanzu ana iya cewa ta koma jihar rashin zaman lafiya sanadiyyar shugabanni marasa kishin ci gabanta da take dasu, sai dai kuma yawon bude ido da shakatawan ko yananan ko babu Allah kadai ya sani.
Ba komai ya kawo wannan gurguwar mataki da gwamna Jang ya dauka na Koran fulanin jihar ba illa rashin daukar kwakkwaran mataki da gwamnatin tarayya takiyi kan shi gwamnan bisa rikicin da ya faru na baya bayan nan a jihar inda aka rasa dimbin rayuka, wanda hakan shi ya sake ba gwamnan karfin guiwar kawo wata sabuwar salon da ka iya haifar da rudani a jihar da ma kasa baki daya. Alal hakika, tilastawa Fulani barin filato wani babban lamari ne da ka iya haifar da komai matuka mahukuntan da abin ya shafa basu sa baki ba. Abin bakin cikine yadda gwamnatin tarayya tayi bakan taki cewa uffan kan wannan lamari wanda barazana ne ga zaman lafiya ta fanin tsaro. Wai ma abin tambaya shine; me yasa irin wadanan matsaloli basa faruwa a sauran jihohin kasar nan sai jihar filato kawai? Shin itace kadai jihar da take da kabilu masu dimbin yawa? Tabbas akwai bukatar shugaba yar’adua ya dauki matakan ladabtar da gwamna Jang don ganin bai wuce makadi da rawa ba in har ya dage kan wannan danyen mataki da ya dauka na korar Fulani, domin babu wanda ya fi karfin doka, kuma duk wanda ya nemi yin karan tsaye ga dokokin kasa, la shakka yana bukatar ladabtarwa don ya zama darasi ga ‘yan baya.
Lokaci yayi da shugabanni ya kamata su rika mulkin adalci ga al’ummar da suke mulka ba tare da nuna banbancin addini, kabila, siyasa, fifita wasu bisa wasu, ko asali ba, tayin hakane kawai za’a samu zaman lafiya, ci gaba da daurewar shugabanci na gari.
Alal hakika, akwai bukatar gwamnatin tarayya ta gaggauta daukan mataki kan wannan kazamin aiki da gwamna Jang keson aikatawa don dakile duk wata hargitsi daka iya kunno kai don samun zaman lafiya a jihar da ma kasa baki daya. Watan wata rana kowa zaiyi bayanin yadda ya tafiyar da shugabancin talakawansa a gaban mai duka, don haka kalu balen ku shugabanni.
Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukanmu na alhairi, amin.

Friday, April 17, 2009

ZIYARAR MU ZUWA MALUMFASHI.

Da sanyin safiyar ranar alhamis ne 16-4-09 na bar zariya zuwa katsina don halartar taron karawa juna sani da wayar da jama'a kan yawan mutuwan mata masu juna biyu da kananan yara wanda sashen hausa na muryar amurka ta shirya. Dayake bansan inda za'ayi taron ba a birnin na dikko , hakan yasa na tsaya a malumfashi don tuntubar yan uwa kamar su kabir sakaina, Mohammad dandattijo da dai sauransu. isana keda wuya sai naci karo da Zaidu Bala wanda dama tuni akasanar dani cewa ya iso malumfashi don zuwa wannan taro. nan muka hadu muka sada zumunci tsakanin mu mukayi dan raha da ba'a rasa ba, wanda daga baya muka dunguma da ni da zaidu bala da usman adamu aleiro zuwa katsina don halartar wanna taro. hakika mutanen malumfashi sun karbe mu hannu bib-biyu, sunyi mana shatara na arziki tamkar munsan juna tun kafin wanna rana, koda yake zan iya cewa munsan juna amman ta hanyar waya kawai, domin kuwa ranar ne a iya saninan muka san junanmu fuska da fuska.
Alal hakika irin wanna karamci da Mohammed Usman dandattijio, Kabir sakaina, Abdurra'uf Abdulkadir da sauran yan uwa suka nuna mana abin yabawa ne matuka, domin kuwa hakan ya dada donkon zumuncin tsakani mu dasu, kuma ina fatan zata daure har muddun rai. suma mutanen garin katsina ba a barsu a bayaba, domin kuwa Comm Bashir Dauda, Ali jauro mai gidan wanka, tare da sauran tawagarsu suma sunyi mana babban maraba , domin kuwa da muka tashi dawowa basu barmu hakanan ba saida suka saya mana kayan tsotse tsotse, kamar dai yadda mutanen malumfashi sukayi mana da zamu tafi. Gaskiya nayi farin ciki da wannan rana matuka da irin wannan tarba da mutanen garin malumfashi da katsina sukayi mana, domin kuwa sun nuna mana kauna kwarai da gaske, hakika katsinawa sun amsa sunan su na 'dakin kara' domin kuwa mun gani kuma mun shaida hakan. Bani da in gantaccen kalmaomi da zan yabamasu ko gode masu saidai in ce Allah ya saka masu da alheri kuma ya barmu tare.
Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukan mu na alheri, amin.

(Engr.)MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
ANGUWAR FATIKA, ZARIA
080-36397682

Tuesday, April 14, 2009

GWAMNA ISA YUGUDA: KAZA NE TA JA ZAKARA!


kace kuce dai ta kare a batun ko malam isa yuguda (gwamnan jihar bauchi) zai koma jam'iyar PDP ko a'a. domin kuwa a yau ne 14-4-09 ya bar jam'iyar ANPP da ta kaishi ga mukamin da yake zuwa PDP wanda a wancan lokaci ta kwance masa zani a kasuwa. Alal hakika malam isa yuguda yaci amanar talakawarsa, musamman ma ganin yadda sukayi ruwa sukayi tsaka a lokacin zabe suka hana kansu barci har saida aka tabbatar masu da nasarar dan takararsu wato malam isa yuguda bayan abinda su 'yan jihar suka kira mulkin kama karya na PDP ya ishesu shiyasa suka kawo canji.
wani abin ban haushi da ke tattare da wannan lamari shine, yadda malam isa yuguda yace "na koma jam'iyar PDP ne don samar da ci gaban jama'ar bauchi" kuma ya kara da cewa wai zai iya barin kujerarsa don kare maradu tare da ciyar da jama'ar bauchi. ko kusa wadanan kalamai nasa ba abin a duba bane, musamman ma inda yace wai komawarsa PDP zata taimaka wajen gina asibitin koyarwa da madatsar ruwa ta kafin zaki da samun manyan ayyuka daga gwamnatin tarayya, wadanda acewarsa, idan bai koma PDP ba, saidai suci gaba da zama a takarda baza su tabbata ba, hakanne yasa ya bar ANPP ya koma PDP don ci gaban talakawan jihar bauchi. to ayar tambaya anan shine sauran gwamnoni dake ANPP basa iya aiwatar da nasu ayyukan kenen tunda basu koma PDP ba? ko kuwa kana yin tallane ga suaran takwarorinka na ANPP da su dawo PDP domin suma su samu damar aiwatar da ayyukan da zasu kawo ci gaban al'ummar su?
a fili yake kowa yasan cewa komawar gwamna yuguda bata da wani nasaba da cigaban al'ummar jihar bauci saidai kawai don biyan bukatar kansa. abin kunya ne yau a kasarnan yadda 'yan siyasa ke canja jam'iyyu don kawai neman abin duiya wanda suka maida shi gaba da bukatun talakawan da suka zabe su. domin kuwa canjin sheka ya zama ruwan dare a kasarnan. wai ma abin tambaya anan shine, shin malam isa yuguda ya mance da irin cin zarafin da jam'iyar PDP tayi masane karkashin jagorancin gwamna adamu mu'aza a wancan lokaci? gaskiya ya kamata ace koda kamshin wannan jam'iya malam isa yuguda yayi, to yayi Allah wadai da ita sakamakon irin wulakanta shi da akayi ba wai ma yayi tunanin komawa cikinta ba. koda yake komawarsa baizo da mamaki ba, don kuwa yanzu munsan kusan 'yansiyasar namu sun koma yan jari hujja, don haka wanna ba abin ayi mamaki bani ganin yadda wasu lamura suka faru a baya,sai dai kawai muce kaza ne ta ja zakara.
yanzu dai ta riga ta kare, amman saura da me? malam isa yuguda sai kajira sakamakon ka, domin Allah sai ya sakama talakawanka da suka baka amana amma kaci amanarsu.

MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
ANGUWAR FATIKA, ZARIA
080-36397682

Monday, April 6, 2009

DEMOCRACY @10: Success or Failure?


A DECADE SINCE THE RETURN OF DEMOCRACY IN NIGERIA : Success or Failure?

Day in, day out, a wise man says that a year is just akin to (like) a day. It is now a decade for the return of civilian and democratic rule or government in Nigeria and simultaneously the incumbent president, Alhaji Umar Musa Yar’adua, is now in his second year in office after stepping into the shoes of the former president Mathew Aremu Olusegun Obasanjo who spent a complete good eight years steering the mantle of leadership in Nigeria as its number one citizen from 1999 to 2007.

It is now desirable for Nigerians, especially those at the grass roots level, to look back and cogitate over this period of decade of democratic rule in Nigeria on what dividend or developments do they achieve or experience. Though they have since expressed their dismay over the catastrophic conditions they had found themselves during the eight years of draconian rule of Mr. Obasanjo.Those conditions/situations of unemployment, high cost of living, melting down industries and factories, e.t.c during those eight years of Obasanjo were some of the reasons that necessitated Nigerians to come out during the 2007 General elections (in order) to bring changes and thereby find a lasting panacea to their worries. Unfortunately for them that dream and wishes has just ended a mirage.

Few Nigerians expect that there could be a meaningful change on the ground of the mannerism of leadership of Yar’adua at the inception or assumption of office by trying to legitimatize his government to the Nigerians in particular and the whole world in general. This is clearly because he is fully aware that the election that brought him into office was characterized by an unprecedented election malpractices in the history of Nigeria . Respect for the rule of law, independence of the judiciary, unity government, zero-tolerance to corruption, and the like, are some of the reasons why some Nigerians welcomed the Yar’adua’s government. He (Yar’adua) actually delivered the goods with respect to the independence of the judiciary. This is corroborated from the fact that he remained mute when the election Tribunals and Courts were busy nullifying the elections of P.D.P candidates at the various level of government on the ground of electoral malpractices. Yar’adua has, without any iota of doubt, shown a sense of maturity in that respect which was not obtained in the Obasanjo’s era.

The recognition of the autonomy of the judiciary and that of the other branches of government by the Yar’adua’s administration had crucially changed the minds of many Nigerians from expecting to the hoping that a new messiah has come to save Nigeria and Nigerians from the shackles of squalor and poverty which they found themselves in during the Obasanjo’s era. Up to now, one out of the so-called 7 points agenda has not been actualized, despite the fact that he has been in the mantle of leadership for two years the problem of incessant power failure which has been plaguing the country for quite a long time and which is one of the 7 point agendas is getting from bad to worst by day and many businesses have collapsed simple because one cannot cope with fuelling a generator. During Obasanjo’s regime, many committees were constituted to address the issue but with little to show. Billions of Naira have been spent fruitlessly. Yar’adua’s administration has also constituted the committees for the same purpose but with little or no success at all. Many problems are still deeply rooted in the country ranging from lack of potable water, defective health system, educational degradation, lack of security and agricultural backwardness, to mention but a few.

Yar’adua needs to institutionalize drastic measures to counter the current global economic crises that is currently affecting the globe. If care is not taken Nigeria like any other under-developed countries is going to be affected negatively this can be seen from the sharp increase in US dollar against Naira and in the fall of price of oil in the world market, looking at the value of Naira in 1999 which is 120 Naira against US Dollar compared with its value today which is 163 Naira against US Dollar one can simply conclude that Yar’adua administration is nothing but a set back. Nigerian stock exchange is also not looking good and there is the problem of unemployment in the country. Yar’adua should as a matter of agency address these issues once and for all to avoid further escalation of the problem. It is very unfortunate that despite the vast natural resources that God in his infinite mercy endow Nigeria with, the resources are mismanaged by a very few and the masses are left in squalor and poverty. The national cake is being looted and squandered by few out of Whims and Fancies to the detriment of the majority.

In some instances the money is spend not in the right way as in the case where dogs were transported into the country at the price of 2 millions naira. What a madness! Now the question is what is the benefit derivable from the Nigerian democracy, is it a dividend or a loss? Infact there is nothing tangible to show which Nigerians can be said to have been benefited in the fast ten years of democratic rule. Indeed the poor remain poorer and the reach remain reacher by day. This is therefore a challenge to the Yar’adua’s government to do something concrete before the remaining two years elapse and it then become too late to cry.

SHEKARA GOMA NA MULKIN DIMOKRADIYYA: Riba ko Asara?

Kwanci tashi ba wuya, shekara kuma kwana ne inji masu iya magana. Yau shekara goma kenen da mulkin dimokradiyya ya sake dawowa a kasarnan, yayin da kuma shugaba Umaru Musa ’Yar’adua ke cika shekaru biyu a gadon mulki bayan ya gaji Obasanjo wanda ya kwashe shekaru takwas yana mulkin Nijeriya.

Shekaru goma da aka kwashe ana mulkin dimokradiyya lamari ne daya dace ‘yan Nijeriya musamman ma talakawa suyi waiwaye suga irin ribar da suka samu a wadannan shekaru. Koda yake, tuni ‘yan Nijeriya suka bayyana rashin jin dadinsu da irin bala’i da halin kaka-ni-kayi da suka shiga a karkashin mulkin Obasanjo na shekaru takwas wanda yakare ba tare da sun amfanu ba. Irin wannan hali da talakawa suka samu kansu a lokacin mulkin Obasanjo na rashin aikin yi, tsadar rayuwa, tabarbarewar masana’antu, da sauran matsananci hali yasa sukayi tururuwa don kawo sauyi a lokacin zaben 2007 amma hakarsu bata cimma ruwa ba, don kuwa wanda Obasanjo keso ne ya gaje shi.

Kasancewar ‘Yar’adua shugaban kasa yasa wasu kalilan daga cikin yan Nijeriya tunanin cewa za’a samu sauyi don ganin yadda shi ‘Yar’adua ya dauko salon shugabancin da farko inda ya fara neman halasta gwamnatinsa a idon yan kasa dama duniya baki daya, domin kuwa yasan cewa zabensa cike yake da magudi. An fara maraba da ‘Yar’adua ne bayan ya bayyana aniyarsa na yin aiki da kowa inda ya fara neman goyon bayan ‘yan adawa dasu shiga a dama dasu don ci gaban Nijeriya, yayi kuma alkawarin sakin mara ga fannin shari’a batare da yi masu katsalandan ba da dai sauransu. Hakan kuwa ya fito fili ne yayinda alkalai suka rika yiwa masu rike da mukaman siyasa karkashin jam’iyar PDP kamar gwamnoni, yan majalisu, da dai sauransu wadanda aka halasta masu zaben da basu sukayi nasara ba tsirara a kotunan zabe, kuma shugaba ‘Yar’adua baice uffan ba, sabanin yadda Obasanjo ya rika cin karensa ba babbaka a kotunan zabe lokacin mulkinsa. ‘Yar’adua yayi hakan ne don samun goyon bayan yan Nijeriya don su amince dashi.

Baiwa fannin shari’a cin gashin kanta da ‘Yar’adua yayi da sauran hukumomi ya sauya tunanin yan Nijeriya kan ‘Yar’adua inda kowa ya fara yabamasa da cewa za’a samu kyakkyawar sauyi a gwamnatinsa da kuma kawo karshen halin da yan Nijeriya suka tsinci kansu a zamanin mulkin uban gidansa Obasanjo. Har yau, manufofin gwamnatin ‘Yar’adua guda bakwai babu wanda aka cimma ko aka aiwatar, gashi shekara biyu sun wuce saura biyu kawai suka rage masa.

Idan aka dubi fannin wutar lantarki, wanda shine uwa uba, kuma sanadiyyar sa masana’antu da dama sun durkushe,lamarin ba’a cewa komai. Lokacin Obasanjo ba irin kwamiti da ba’a kafa ba don samun saukin abun amman duk abanza, domin kuwa ankashe biliyoyin naira lokacin Obasanjo amman kwalliya bata biya kudin sabulu ba. Shi kanshi ‘Yar’adu ya kafa kwamitoci har guda uku akan wutar lantarki amman har yanzu labarin bai canza ba. Har yau, anada matsalar rashin kyakkyawar ruwan sha, rashin kwakkwaran tsarin kula da lafiyar yan Nijeriya, tabarbarewar tsarin ilimi, rashin tsaro, fannin noma ma duk bata canja zani ba.

Tilasa ‘Yar’adua sai yayi da gaske kan tashin gwauron zabi da dalar amurka keyi akan naira. Bayan hawan Obasanjo mulki a shekara 1999, naira ta daga ta kai #120 a darajar dalar amurka daya, inda dukkan yan Nijriya suka yi tir da wannan lamari. Amma yanzu karkashin mulkin ‘Yar’adua, dalar amurka daya itace daidai da #180. Kasuwar hannun jarin Nijeriya shima ba’a barshi a baya ba, don kuwa sai kara durkushewa takeyi a kullum, rashin aikinyi ya gallabi yan kasa. Hakika wadanan lamari ne da suke bukatar gaggawar maida hankali akansu. Hakan kuwa na nuna cewa mulkin ‘Yar’adua na neman ya zarce na Obasanjo a sukurkucewa.

Kullum dai abin sai kara tabarbarewa sukeyi duk kuwa da irin arzikin da Allah yayi wa Nijeriya, koda yake arzikin kan komane aljihunan kalilan daga cikin yan kasa sauran kuma a kashesu ta hanyar da bazasu amfani al’umma ba. Kamar dai yadda akeso a sayo wai karnuka kan naira miliyan biyu akan ko waani kare guda daya! Wanna lamari da mai yayi kama?

To wai a tsawon wadannan shekaru suwa suka amfana ko sukaci ribar mulkin dimokradiyyar nan? Shin anci riba ne ko asara akayi? Alal hakika babu abinda ‘yan Nijeriya a yau zasuce sunci ribarsa a tsawon shekaru goma da suka wuce. Talaka bai amfana ba ta ko ina kuma baici ribar dimokradiyya ba don kuwa har yanzu yana nan yana ci gaba da dandana kudarsa da ta samo asalin tun mulkin Obasanjo, ba’a aiwatar da ayyukan ci gaban kasa ba, masana’antu sai kara durkushewa sukeyi, ga rashin aiki ga matasa, da dai sauransu. Don haka, wannan wani kalu bale ne ga shugaba ‘Yar’adua na ganin yayi kokarin aiwatar da manufofinsa a cikin shekaru biyu da suka rage masa.
Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukan mu na alhairi, amin.

kaji kadan..

Wednesday, April 1, 2009

YUNKURIN HALLAKA GWAMNAN YOBE

watanni biyu bayan rasuwar gwamnan jihar yobe, senata Mamman Bello Ali, sai gashi sabon gwaman jihar Alhaji Geidam na fuskantar barazanar kisa. hakan kuwa ya fito filine lokacin da akayi zargin an samasa guba a abinci, kuma da aka ba karnuka abincin, sunci sun mutu nan take. haka ya haifar da rudani a jihar ta yobe da hukumomin jihar baki daya. saidai kuma wata majiya daga fadar gwamnatin ta karyata wannan labari, inda sukace gwamnan na nan cikin koshin lafiya babu kuma wani yunkuri na hallakashi.

Sunday, March 22, 2009

FACTS ABOUT AFRICA!

The history of present day Africa states could be traced to colonial rule, courtesy of the Berlin conference of 1885, which divided African territories into areas of influence of European powers. The actual rule was brief or long, depending on the policy of the colonial powers. At the end of the colonial rule, independence was granted as a result of mutual settlement or prolonged war of independence.

At independence, African states establish their government based on liberal democratic principles with a flourishing multi-party system. Within four years, multi-party system collapsed, giving way to one party rule or military authoritarianism. This system of government continued to dominate the African political landscape until the end of the 1980’s.

From the Northern Horn to the southern cape: and from the Tropical Savannah of the west to Equatorial Region of the East, the entire continent was caught in a wave of democratization. Indeed, democracy became the only game in town. One of the essentials features of democratization process is election.

TARIHIN AFRIKA A TAKAICE

Tarihin kasahen Nahiyar Afrika ya samo usuli ne daga Taron Berlin da akayi a shekarar 1885 a wannan taron ne aka amince da yanyanke Afrika ga daulolin Nahiyar Turai. Irin mulkin mallaka ko mulaka'u da daulolin Nahiyar Turai din suka yi na wa'adi ne ya Allah mai tsawo ko takaitacce. A karshen mulkin mallakar, kasashen da aka mallaka sun sami 'yanci a sakamakon fahimta da yarjejeniya ko kuma bayan anyi gwagwarmayar yakin kwatan 'yanci.

kasashen Afrika da suka sami 'yanci kan tafiyar da harkokin mulkin dimokuradiyya mai tsarin mulki da jam'iyun siyasa kan yin aiki tare. A dan lokaci kadan (kamar shekaru hudu) tsarin siyasa mai jam'iyu da yawa kan ruguje ya haifar da jam'iya daya mai kama-karya ko kuma mulkin soja. Irin wannan yanayi ne ya yiwa harkokin siyasa kaka-gida a kasashen Afrika har zuwa karshen shekarun 1980.


Ilahirin Nahiyar Afrika ta tsunduma cikin hadahadar tsarin mulki irin na dimokuradiya wanda hakan ba ya samuwa sai ta hanyar zabe.

Wednesday, March 11, 2009

SAMMACIN AL-BASHIR: ADALCI KO ZALUMCI?

A ranar laraba ne 4/3/2009, kotun kasa da kasa da ke birnin Hague ta bayar da umurnin damko shugaban kasar Sudan, Omar Hassan Al-Bashir. Kotun na zargin shugaba Al-Bashir ne da laifukan kisan kare dangi a Dafur daga 2003. Tuni wannan sammacin ya haifar da cece-ku-ce a kasar Sudan da ma duniya baki daya inda mafiyawancin kasashe ke tir da wannan umurni na kotun duniya. To amma bai kamata ayi tuya a manta da albasa ba, domin kuwa ya kamata mu duba muga menene ummul aba isin haifar da wannan rikici na dafur? Kuma su waye keda hannu a rikicin? Tun bayan da arzikin mai ya samu a kasar Sudan, Amurka tayi kokarin ganin ta shiga kasar ta tafiyar da harkar mai amma hakanta bai cimma ruwa ba don kuwa basu samu yadda suke so, hakan kuwa shine silsilan rikicin Dafur kuma ita Amurka itace ta haifar da rikicin don ta kasa samun biyan bukatanta. Domin kuwa kafin bullar mai a kasar, Sudan na zaune cikin zaman lafiya ne ba tashin hankali a cikinta. Alal hakika kotun kasa da kasa dake Hague batayi adalci ba kan umurnin da ta bayar na damko shugaba Al-Bashir bisa zargin kisan kare dangi, kamar yadda mai gabatar da karar a kotun kasashen duniya Lius Moren-Ocampo yayi. Wannan hukunci kuma ka iya kawo cikas ga yunkurin tattaunawar sulhu da ake yi da nufin kawo karshen yakin da ake yi a yankin na Dafur mai arzikin mai.

Hakan ya nuna a fili cewa kotun bata aikinta yadda ya kamata, ko kuma ace akwai ‘yan lele da bata iya taba su. In harda gaskene kotun na gudanar da aiki tsakani da Allah ai ba Al-Bashir ya kamata su kwallafa idon su a kansa ba. Ga babban wanda ya aikata kisan biliyoyin al’umma a Afghanistan da Iraq, ko shakka babu tshohon shugaban kasar amurka Goerge W. Bush da tshohon prime minister Birtaniya Tony Blair sune kotun birnin Hague ya kamata taba da sammacin kama su. Har ila yau, kisan kare dangi da yahudun bani Israel sukayi wa palasdinawa shima abin dubawane, domin kuwa bani yahudun sunyi amfani da makamai masu kazamin guba, sunyi lugudan wuta iri-iri akan palasdinawa wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwar mutane bila a dadun, wasu kuma suka jikkata ga asarar dukiyoyi da akayi da dai sauransu. To wadanna ba laifine da yakamata kotun ta hukunta wadanda suka aiwatar dashi ba? Bush har ya yi yakinsa a kasar Iraq bai nuna wa duniya koda tsinke daga abinda yace yana zargin kasar dashi na makaman kare dangi ba. Sanadiyyar haka dumbin al’ummar kasar Iraq suka rasa rayukansu, dukiyoyi sun salwanta, ga lalata masu kasa da yayi Kuma kowa na kallonsa ba wanda yace masa uffan. Ashe wannan ba babban laifine da yakamata ace kotun ta dauki mataki mai karfi kan wanda ya aikatashi ba ganin cewa zargin da akeyi ma kasar kage ne kawai ba gaskiya a cikinta? ko kuwa shi yafi karfin doka ne? Tabbas baza mu taba ci gaba ba idan akace doka zata rika aiki kan wasu ‘yan tsirari ne kawai, sukuma ‘yan lele a barsu su rika cin karensu ba babbaka.

A fili yake kuma kowa ya sani saidai aki fadin gaskiya rikicin Sudan Amurka ne ta haddasa shi karkashin mulkin kama karya na Bush W.George, don haka Bush ya kamata ayi sammaci ba Al-Bashir ba. Lokaci yayi matuka da yakamata kasashen afrika su fahimci irin kallon da kasashen yamma keyi masu, don kuwa wannan umurni da kotun ta bayar kan Al-Bashir hannunka mai sanda ne ga sauran shugabannin, don haka su gagguta nuna rashin goyon bayansu kan wannan umurni na kotun mara tushe balle makama, domin ance idan gemun dan uwanka ya kama da wuta to shafa ma naka ruwa. Don haka, kotun kasa da kasa ta sake nazari kan wannan umurni da ta bayar na damko Al-Bashir, Bush da sauran ‘yan kan zaginsa ya kamata a damko kafin aje ga Al-Bashir (in har yayi laifin da za’a kamashi). Allah ya taimaki nahiyar afrika ya kuma kareta daga sharrin kasashen yammaci.
Allah ya yi mana jagoranci a dukkan ayyukan mu na alhairi, amin.

Sunday, March 8, 2009

Matasa Na da Mahimmanci ga ci gaban al'umma.

Matasa akace manyan gobe, kuma tushen cigaban kowace al’umma. Hakika wannan zancen haka yake, domin kuwa suna da babbar rawar dasuke takawa wajen tafiyar da harkokin yau da kullum. Saidai wani babbar matsala dake tare dasu shine rashin nuna halin ko inkula da gwamnati keyi masu. Rashin sanin muhimmancin matasan yasa haka ko kuwa rashin sanin su wanene matasa? To yadai kamata kowa yasan cewa matasa sune manyan gobe kamar yadda aka sani, kuma suna da babbar gudun muwa da zasu iya bayarwa wajen aikin raya kasa. Shin menene kalmar masata take nufi? Kan wanene hakkin matasa ya rataya? Menene kalmar manyan gobe take nufi, kamar dai yadda akance matasa manyan gobe? Wani irin kalu balene yake gaban su matasan? Menene zai iya faruwa kan irin rikon sakainar kashi da akeyiwa su matasan?
Ita dai kalmar matasa na nufin samari ne wadanda shekarunsu ya fara daga 18-25, kokuma daga 18-30 kamar yadda wadansu suke gani, yakuma ma danganta ne da yadda kowa yake ganin lokacin da yakamata a kira mutum a matashi, wato daga shekara 18 zuwa yadda yasamu. Idan kuma muka duba shin kowane ne hakkin matasa ya rataya akansa, zamu ga cewa hakkin nasu bawai ya rataya akan gwamnati bane kawai, harma da iyaye da sauran al’umma, koda yake ana iya cewa gwamnati ita keda babbar hakki. Abinda gwanmati ya kamata tayi wa matasa shine, samar da ilimi bai daya garesu, tsaro, kula da lafiyan su, sai uwa uba aikin yi domin kuwa wannan hakkine wanda ya rataya akanta. Sukuwa iyaye da sauran al’umma, hakkin sune suga cewa sunba matasa tarbiyya mai kyau, kuma sun basu horon daya dace dasu wajen tafiyar da ayyukansu na yau da kullum. Domin kuwa duk wata al’umma da take son cigaba, sai tabayar da cikakkiyar kulawa ga matasanta da basu kyakkyawar horon daya dace dasu don zama wakilansu na gari bana banza ba a duk inda suka shiga.
Allah sarki! Bahaushe yace wai matasa manyan gobe, kuma ko shakka babu wannan Magana haka take, kamar yadda nace a baya. Domin dai ita kalmar manyan gobe na nufin matasa ne zasu amshi tafiyar da ragamar mulki a duk lokacin da wadanda suke mulkin a yau suka tsufa ko wa adin barin aikin su yayi. Saidai labarin a kasar nan tamu Nijeriya tasha bamban. Domin kuwa, idan aka duba tun daga matakin kananan hukumomi har izuwa ta gwamnatin tarayya, za’a ga cewa duk wadan da shekarun su yafara daga 50-60 koma fiye da haka sune a madafun iko. Ba za’a ga matasa wadanda shekarunsu ya fara daga 35-40 ba, duk dacewa suna da babbar gudun muwar da zasu iya bayarwa wajen ci gaban kasar nan.
Matasa a yau sun zama kashin bayan ci gaban kowace al’umma, batare da la’akari da muhimmancin su a cikin al’umma ba, dakuma rawar da zasu taka ta fannin gina kasa. Hakika wannan yaka mata yazama kalu bale gasu matasan don ganin martabarsu ya karbu a ko ina, ta hanyar kaura cema duk wani aikin ash-sha, shaye-shaye da dai suransu, ganin cewa akwai bata gari acikinsu, kuma bahaushe yace wake daya shi ke bata gari. Saboda haka yaza ma wajibi ga matasa da su gyara kansu, sukuma san cewa dabi’ar banza bazata haifar masu da da mai ido ba. Har ila yau kada matasa su yadda su zama ‘yan bangan siyasa, abin nufi anan shine, kada wasu ‘yan tsirarun mutane su rika amfani dasu wajen tada zaune tsaye don kawai cimma burinsu, wanda bayan su wadannan mutane sun samu abin da sukeso basa yiwa su matasan komai illa su watsar dasu. Matasa susan cewa fa su wakilai ne na samar da zaman lafiya ba hargitsi ba a cikin al’umma. Komai na iya faruwa a duk lokacin da aka tauye ma matasa hakkinsu ko akaci gaba da nuna halin ko inkula dangane da rayuwarsu, musamman ma idan babu cikakken tsaro, ilimi, da uwa uba aikinyi da kuma sauran abubuwan more rayuwa wanda yazama hakkine na hukuma ta samara dasu. Rashin wadan nan abubuwa zai iya jefa matasa a tsaka mai wuya, kamar dai sace-sace, yawon banza da sauran aikin ashsha da baza’a rasaba, wanda kuma bama fatan hakan ya faru ga su manyan goben.
Daga karshe, ya kamata gwamnati da sauran hukumomin da abun yashafa da su san cewa fa matasa ba abin wasa bane a kowace irin al’umma. Musamman ma ganin cewa sune manyan gobe kamr yadda nayi bayani a baya, kuma suna da gudun muwa na cigaba da zasu iya bayarwa. Don haka yana da kyau a rika duba duk wata irin matsaloli dake damunsu, da kuma yin kokarin samar masu da maganinsa. Kana duk wata al’umama ko gwamnati data ga ayyukanta na samun cikas ko rashin ci gaba, to ta waiwaya ta dubi matasanta taga yadda al’amuransu yake tafiya.
Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukanmu na alhairi amin.

Tuesday, March 3, 2009

SHIN MATASALAR RUWA ZAI ZAMA TARIHI A ZARIA?

Budaddiyar Wasika Ga Gwamna Namadi Sambo.
Duk dan adam yana da bukatan abubuwan more rayuwa na yau da kullum kamar su wutan lantarki, hanyoyin sufuri masu nagarta,da dai sauransu.amman saidai a yau akasin hakan ake samu. Koda yake, wasu ma ana iya cewa sun zama dole yin amfani dasu. Misali, koda yake ruwa ba’a ce dashi abin more rayuwa ba, amman dukkan mai numfashi na bukatansa a kulli yaumin domin sha, girki da kuma sauran ayyukan yau da kullum

Kash! Saidai labarin a birnin zariya ba haka yake ba. Domin kuwa ruwa ya zama dan gwal. Saboda a yau duk wanda yazo garin zariya daga wata garin, to babu abinda da zasu fara yi masa maraba face ‘yan garuwa. Wadanda suke sayar da ruwan nasu da dan karan tsada, kuma gashi wasu daga cikinsu ruwan nasu bawai yana da kyau bane. Wanda idan hakan ta daure, to nan gaba ba’a san abinda zai haifarba.

Koda yake wannan matsala na rashin ruwa a birnin zariya bawai sabon lamari ne ba, saidai kawai yadda rashin nasa yake dada tabarbarewa. Na tabbata duk yaron da ke zariya a yau, wanda shekarunsa basu wuce sha takwas zuwa ashirin ba, wallahi bai taba ganin ankawo ruwan famfo a gidansu ba. Wannan matsala kuwa ta wuce duk iya tunanin mutane, domin kuwa kamar yadda nace ne tun farko, al’amarin yana neman wuce gona da iri. Abin ban takaici ne yadda a yau yara kanana cikin dare suke fita ko kuma da subahin fari da sunan suna zuwa neman ruwan da iyayensu zasu yi masu abinci. Wanda hakan kan iya sa yaran shiga wani halin da bai dace ba.

A kwai bukatan hukumomi ko gwamnati data shiga cikin wannan lamari don kawo saukinsa ga al’ummar da suke yiwa shugabanci. Koda yake, mai girma gwamnan kaduna Alhaji Namadi Sambo, ya samar da famfuna masu aiki da hasken rana wadanda zasu iya aiki daga safe har zuwa la’asar ko ace yamma. Saidai labarin ba haka yake ba, domin kuwa famfunan sun zama abin adone kawai a birnin na zariya. Saboda idan famfon yabada ruwa na kamar sa’a uku a rana, to sai yayi kamar mako daya koma fiye da haka bai sake bada ruwa ba duk da cewa da hasken rana yake aiki bada wutan lantarki ba. Wani abin ban haushi ma shine yadda manya da kanan yara ke dambe a wajen diban ruwan, wanda hakan kan haifair da jin raunuka da dama gasu yaran. Koda yake yin damben nasu nada dalili, domin wani bokitinsa takan kwana biyu ko uku a layi, amman lokaci daya wanda yafisu son zuciya sai yazo yace sai ya diba kafin su, wani lokaci kuma sukan tashi a tutan ma’aho. kai yanzuma kalilan daga cikin wadannan famfuna ke aiki. koda yake ana iya cewa nesa tazo kusa, domin kuwa mai girma Gwamna Namadi Sambo yabada kwangilar gyara ruwan Zariya don al'umma su samu saukin wannan hali na mawuyacin ruwa da suke ciki. to amman abin tambay shine: shin wadanda alhakin ya rataya akansu zasuyi aiki tsakani da Allah don kawo karshen wannan hali ganin cewa kusan shekaru goma kenen ake shelar cewa matsalar ruwa a Zariya zata zama tarihi amma har yau shiru akeji kamar Mallam yaci shirwa?

Don haka ya kamata gwamnatin jihar kaduna data karamar hukumar zariya suyi hubbasa wajen magance wannan fitina data addabi jama’ar nasu, ganin cewa ma yana daya daga cikin alkawuran da suka daukan masu yayin yakin neman zabe. Saboda wanna ruwa da ‘yan garuwa ke sayarwa, mafi yawancinsu bamasu kyau bane, kuma shan irin wadannan ruwan na iya haifar da barkewar wata cuta. (Amma bawai ina kashema yan garuwa kasuwa ne ba, a'a gaskiyar lamari ne, kuma nayi bayanin cewa bawai dukkansu ne keda ruwa mara kyau ba.)

Ya kamata mai girma gwamna alhaji namadi sambo, ya sake duba wadan nan famfuna da aka kafa masu aiki da hasken rana don su rika aiki yadda ya kamata, don kada yazamana anyisu amman babu amfani ganin cewa kudin al’umma aka dauka akayi aikin dashi, don haka yakamata suga amfanin yin aikin da dukiyarsu. Har ila yau, mai girma Gwamna yasa ido akan kwangilar aikin ruwan don kada marasa son ci gaban Zariya suyi kafan ungulu a aikin.
.Allah shiyi mana jagora a dukkan ayyukanmu na alhairi amin.

Friday, February 27, 2009

GASKIYA DOKIN KARFE.

Dangane da bayanin dana yi a jaridar aminiya mai taken KAN BATUN RIBADU A TSAKA MAI WUYA, amman jaridar aminiya ta bashi taken dayafi dacewa dashi na HARYANZU INA GOYAN BAYAN RIBADU.kuma aka bugashi a jaridar ranar 20/2/09. a cikin kasidar dai na dada bayyana dalilan da sukasa nayi wancan rubutun mai taken RIBADU A TSAKA MAI WUYA wanda aka buga ranar 19/12/08, kuma shine silar yin wannan kasida na HARYANZU INAGOYAN BAYAN RIBADU sadoda irin korafe korafen da na rika samu daga wadanda sukakaranta waccar kasidar ta farko na ranar 19/12/09.
kamar yadda nasha fadi, gaskiya dai dayace, kuma daga kinta sai bata. gaskiya akace kuma dokin karfe ne. Nayi imani cewa ko bijima ko ba dade, gaskiya zatayi halinta domin Allah ba azzalumin kowa bane.
Nayi farin ciki matuga kan sakwannin waya dana samu wajen wadanda suka karanta wannar kasida na HARYANZU INA GOYON BAYAN RIBADU dakuma wadanda suka bugo waya don bayyana ra'ayinsu kan batun. Allal hakika sakwannin dana samu sun nuna cewa yan Nijeriya da dama sunyi tir da wannan halin tsangwama da akema mallam Nuhu Ribadu duk dacew ya bautawa kasar nan iya bakin kokarinsa. kodayake, ansami wasu kalilan da basu amince da yadda shi Ribadu yayi ayyukansa ba, dama ance ai daidan wani karkataccen wani. Komadai yane, ina matukar godiya ga dukkan wadanda suka dauki lokaci suka aiko da ra'ayinsu.
godiya ta musamman ga wadanda suka aiko da sakwannin waya kamar su Malam Ibrahim dan zariya mazaunin Lagos, Labaran Waziri Darazo, Abubakar Muh.A.K Zabi Auyakari giyade Bauchi mazaunin Jos, Auwal, Bashir Dikko Funtua, Sani Bandy B/Gwari, da sauransu.
har ila yau, ba zan manta da dukkan wadanda suka bugo waya ba kamar su Malam Abubakar Sani daga Kaduna, Wada Isa daga Kano, Idris Suleiman Plateau mazaunin Legos, Mahmud daga Kano, Kawu saleh daga Jos, Abubakar Moh'd daga Kebbi,
zanyi amfani da wanna dama in mika ban hakuri ga wadanda suka aiko da sako ko bugo waya amman basuga sunansu ba, suyi hakuri abin ne da yawa wai mutuwa ta shiga kasuwa. Wasu na manta sunansu da lambarsu, wasu kuma na kasa daukar sakon waya da suka aiko dashi har kuma sakon ya bace. Don Allah ayi hakuri saboda ayyukan sunada yawa.
Allah yayi mana jagora a dukkan ayyukanmu. wassalam.

Monday, February 23, 2009

KARNUKAN 'YAN SANDA SUNFI TALAKA AMFANI!

Ci gaban ko wace kasa da kwanciyar hankali ya danganta ne kan irin tsaron da take dashi. Domin kuwa tsaro na daya daga cikin abubuwan dake kawo ci gaba a ko wace kasa. Duk kasar da babu cikakken tsaro a cikinta, la shakka wannan kasa na cikin fargaba da karuwar barayi da sauran masu aikata miyagun ayyuka.
Hakika hubbasar gwamnatin Nijeriya na sayo karnuka don baiwa rundunar yansanda domin kara inganta harkar tsaro abin a yabane matuka gaya. Domin kuwa hakan zai dada taimakawa jami’an tsaron durkushe ko wani irin gungu na barayi da kuma bata gari. Amma fa akwai alamar tambaya a cikin wannan lamarin. Domin kuwa kudin da gwamnatin tayi ikirarin cewa za’a sayo ko wani kare guda daya ya wuce daukar mai hankali, sannan ga kudin yin masa hidima a kowani ranar Allah ta’ala. Baya ga naira miliyan biyu a kan ko wani kare da za’a sayo, akwai kuma kudin ciyar dashi a kowani rana naira kusan dubu biyu koma fiye da haka. Kenan, kudin abincin ko wani kare a wata ya fi albashin wani dan sanda kenan. Lallai kam Allah ya kawomu wani zamani da a nijeriya dabba yafi dan adam daraja da kuma amfani a wajen gwamnatin kasa.
Alal hakika akwai bukatar gwamnatin nijeriya ta sake lale da kuma duba wannan kudi da aka ware don sayo karnukan nan wadanda akafi sani da POLICE DOG don kaucewa yin almubazzaranci da dukiyar jama’a. Domin kuwa hakan zaizama abin tir da kuma Allah wadai, ganin yadda talaka ke cikin kunci hali, tsadar rayuwa ga rashin ci sau uku a rana amma ace wai an dauki kudin talakawa wuri na gugar wuri har naira miliyan biyu don sayo ko wani kare guda daya.
Bawai wannan na nufin hubbasan da gwamnati keyi na sayo karnuka don inganta harkan tsaro bashi da kyau ba ne, a’a makudan kudin da akeson kashewa ne don sayo karnukan sukayi yawa, musamman ma ganin cewa akwai hanyoyi da yawa da za’a iya inganta harkan tsaro a kasarnana. Alal misali, akwai bukatar sayowa jami’an tsaro kayan aiki na zamani don samun yin gogayya da takwarorinsu na kasashen ketare dakuma samun damar yin ayyukansu ba tare da wani fargaba ba. Domin kuwa sama da kashi tamanin cikin dari na kayan aikinsu tsoffini kuma basu da inganci. Har ila yau, a kawi bukatar turasu yin kwasa-kwasai don kara gogewa da sanin makaman aiki (koda yake gwamnati ta soke zuwa kasahen waje don yin kwas-kwasai sakamakon faduwar darajar man fetur a kasuwar duniya) da dai sauransu. Don haka sayo karnuka ba tare daba jami’ai horon daya kamata ba tamkar yin aikin banzane domin kuwa kwalliya bazata biya kudin sabulu ba.
Waima abin tambaya shine, shin ya dace a kashe wadannan makudan kudin don sayo karnuka kawai? Zai yi kyau sosai idan aka sake duba kasafin da akayi don sayo wadannan karnuka,kuma gwamnati ta rika sara tana duban bakin gatari ba wai a fake da guzma a harbi karsanaba. A gayawa talakawa gaskiyar abinda za’ayi da kudinsu bawai sayo karnuka ba.

Tuesday, February 17, 2009

MUGABE AND HIS NEW CABINET

After a long battle

DOLE TASA MUGABE YA BA TSVANGARAI PM

Bayan kai ruwa rana da aka dade anayi a rikicin siyasar Zimbabwe tsakanin jam’iyar adawa ta MDC da kuma shugaba Mugabe na zanu PF, a makon jiya ne aka cimma daidaito inda aka rantsar da Morgan Tsvangarai a matsayin prime minister ranar Alhamis 12/2/09 ,bayan ankwashe shekara guda ana neman hanyar sulhu da kokarin kafa gwamnatin hadin kasa. Rantsar da Tsvangarai a wannan matsayi yayi ma kasashen duniya da jama’ar Zimbabwe dadi matuka gaya, domin kuwa suna ganin haka wani mataki ne da zai kawo karshen mulkin kama karya na Mugabe (kamar yadda yan kasar suke ikirari) musamman ma ganin yadda kasashen yamma suka sakawa kasar takunkumi daban daban sakamakon rashin hulda mai nagarta da mugabe keyi da kasashen. Koda yake, a fili yake cewa dole tasa Mugabe ya amince da raba madafan ikon don ganin yadda yake dada samun matsin lamba daga kasashen duniya, ba wai don yanason yin hakan ba.
Zimbabwe dai ta shiga ko ace tana halin kaka na kayi kamar dai matsalar tattalin arziki, faduwar darajar kudin kasan, barkewar cututtuka da dai sauransu. Alal hakika wadannan matsaloli sune zasu zamo kalu balen sabon prime minister don ganin yaba da tasa irin gudun muwar wajen magancesu in har za’a sake masa mara yayi fitsari. Saidai kuma a wani bangaren, masana siyasa na ganin shigar Tsvangariai cikin gwamnatin hadin kasar bazata yi tasiri ba, musamman ma ganin yadda Mugabe ya dauke manyar mukamai kamar su ministan cikin gida, kasahen ketare, da dai sauransu yaba wa yan jam’iyarsa. Har ila yau, jam’iyar dai ta Mugabe ita keda yawan ministoci a cikin gwamnatin.
Koda yake jam’iyar Tsvangarai nada yawan kujerun majalisa, don haka wannnan wata damace ga shi don ganin ba’a tilasta masu bin dokoki ko ka’idojin da ba bisa hanya suke ba. Alal hakika, akwai bukatar Tsvangari ya rika sara yana duban bakin gatari akan aikinsa ganin cewa yana da kima a idon jama’ar kasar sa dama duniya baki daya ta fanin diflomaciyya. Kada ya zama dan amshin shatar Mugabe, domin kuwa kasashe da dama anyi irin wannan gwamnatin hadin kasa amman daga baya sai yan adawa su rikide su manta da akidarsu don neman kawai abin duniya.
Yin aiki tukuru da tsare gaskiya da amanar kasa sune kadai zasu dada kare mutunci da kimar sabon prime minister. Ya kamata ya nesanta kansa da dukkan wasu nau’i na almubazzaranci da dukiyar kasa. Wani babbban abin ban haushi da Allah wadai shine yadda Mugabe ya ware kudi wuri na gugar wuri har sama da dala miliyan dari uku wai don bukin tunawa da ranar haihuwarsa kawai! Wanna aiki da mai yayi kama? Koda yake wanna ba abin mamaki bane, domin kuwa duk shugabannin da suka hau mulki ta hanyar satan kuri’u da murdiya saboda karfin iko, basa tsinanawa talakawansu komai illa nakasa su. Lokaci yayi da shugabanni zasu yi karatun natsuwa ga maganar da shugaban amuruka Barack Obama yayi bayan an rantsar dashi inda yace “ al umma zasu rika tunawa da shugabanninsu kan abubuwan da suka gina masu ne bawai abinda suka lalata masu ba”. Ko shakka babu wannan zancen gaskiya ne, domin kuwa duk wanda yayi al mubazzaranci ko ya sace dukiyar talakawansa, la shakka bazasu taba mantawa dashiba, amman bawai don aikin alheri da yayi ba, a’a don lalata masu da salwantar da arzikinsu da yayi.
Yin kaka gida akan mulki yazama ruwan dare a nahiyar afrika, inda shugabanni keson dawwama a mulki har sai illa masha Allahu, kamar dai yadda ya faru a kasar Kenya-inda nan ma anyi dauki ba dadi tsakanin Kibaki da Odinga, kafin acimma daidai tuwa daga karshe. To yanzu ma hakanne ke faruwa a Zimbabwe don kuwa Mugabe ya rantse mutu ka rabasa da mulkin kasar domin kuwa yace Zimbabwe kasarce, don haka ba gudu ba ja da baya. Yanzudai zabi ya rage ga Tsvangarai na ko ya tsaya yayi aikin da zai ceto kasar daga cikin halin kuncin Da take ciki da kuma kawo sauyi ga salon mulkin kasar, ko kuma akasin hakan. Amman fa karya manta cewa, yanzu talakawan sa da sauran kasashen duniya sunsa masa ido suga irin kamun luddayin da zaiyi, don haka sai yayi duk mai yiwuwa yaba marada kunya.

ZIYARAR SHUGAN KASAR SIN

ZIYARAR SHUGABA HU JIN TAO
La shakka ziyarar da shugaban kasar Sin Mista Hu Jin Tao yakai a wasu kasashe na nahiyar afrika don habbaka dangantakar kasuwanci tsakaninsu abin ayi maraba da shine matuka gaya. Alal hakika wanna ziyara tasa za taba kasashen dama bude sabon babi tsakani su da kasar ta Sin, musamman ma ganin cewa kasashen na Mali, Senegal, Tanzania da kuma Tsibirin Moroshiyos kasashene masu tasowa kuma wadanda basu da karfin tattalin arziki.
Wannan Mataki da shugaba Hu ya dauka duk da cigaba da tabarbarewar tattalin arzikin kasashen duniya, don dada habbaka huldar dangantaka tsakanisu wanda dama tuni suke huldar kasuwanci tare, ya samu karbuwa ga dukkan yan kasashen dama nahiyar afrika baki daya. Tabbas Mista Hu yayi kwakkwarar tunani na zaban wadannan kasashen don ganin sunyi huldar kasuwanci tare, duk kuwa da cewa kasar Sin kasa ce da taci gaba nesa ba kusa ba da wadannan kasahen.
Hakan kuwa zai kawo ci gaba ba karami ba ga akasashen in har duldar tasu tayi karko, dafatan sauran kasashe masu cigaban masana’antu da tattalin arziki zasu dada karfafa huldar cinikayyarsu da sauran kasashen afika don suma su samu su daga.

Thursday, February 5, 2009

TRIBUTE TO GOV. MAMMAN BELLO ALI

To Allah we are and to him our return is! Gov Mamman Ali has been call to glory. That’s ordinary of human lives. He died when his contribution is highly needed in his state and indeed the country at large. We all believed that what God has destined to happen no human being on this earth can change it. While he lived, Mamman Ali was a cool headed unassuming person who gave everybody his due respect. A philanthropist, a man who stood for justice, fair play and equity. A hardworking and trustworthy. Yobe state and Nigeria has lost a great man.
It’s our earnest prayer that the almighty Allah will have mercy on him, together with all the muslims who died before him right from the time of prophet Adam (A.S). May he afford us the will and patience to pray for them and bless us with those who will pray for us when we die. We pray to almighty Allah to continue to give the family, relatives and friends the fortitude to bear the irreplaceable lost. We also pray that his gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.

TRIBUTE TO GOV. MAMMAN BELLO ALI

To Allah we are and to him our return is! Gov Mamman Ali has been call to glory. That’s ordinary of human lives. He died when his contribution is highly needed in his state and indeed the country at large. We all believed that what God has destined to happen no human being on this earth can change it. While he lived, Mamman Ali was a cool headed unassuming person who gave everybody his due respect. A philanthropist, a man who stood for justice, fair play and equity. A hardworking and trustworthy. Yobe state and Nigeria has lost a great man.
It’s our earnest prayer that the almighty Allah will have mercy on him, together with all the muslims who died before him right from the time of prophet Adam (A.S). May he afford us the will and patience to pray for them and bless us with those who will pray for us when we die. We pray to almighty Allah to continue to give the family, relatives and friends the fortitude to bear the irreplaceable lost. We also pray that his gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.

KAN BATUN RIBADU A TSAKA MAI WUYA!

A cikin watan disamban shekarar data gabata ne na rubuta wata kasida mai taken RIBADU A TSAKA MAI WUYA, kuma jarida Aminiya ta buga a ranar 19/12/2008. kasidar taja hankalin wadanda suka karanta ta da dama, domin kuwa wasu sun kira wasu kuma sun aiko da sakon waya suna masu bayyana ra'ayinsu dangane da kasidar. Alal hakika kowa nada yancin bayyana ra'ayinsa ko tofa albarkacin bakinsa kan lamuranyau da kullum, kamar yadda nima nayi ta hanyar rubuta wannan kasidar.

kusan dukkan sakonnin dana samu da kuma wadanda suka bugo waya, in banda kalilan daga cikinsu,sunyi tir ne da kuma Allah wadai da wannan kasida nawa suna masu cewa bani da tunani. wani bawan Allah cewa yayi "wallahi inajin dadin kasidunka dana ke karantawa , amman ban taba tunanin bakasan abinda kakeyi ba sai a wannan daka rubuta kan Ribadu da kake kiran talakawa wai suyi masa addu'a", wasu sunce dani dan koran Ribadu ne da dai sauransu.
kamar dai yadda nace ne daga farko, kowa nada yancin furta albarkacin bakinsa a kowani irin lamari domin a mulkin dimokaradiyya muke-Nidai bansan wannan bawan Allah (Ribadu) ba, haka shima bai sannin ba. Ban taba ganin sa ido da ido ba, kuma babu wata alaka tsakani na dashi, haka kuma banyi tunanin nan gaba wani abu zai hadani dashiba balle mu hada idanu da shi, don haka maganar cewa ni dan koransa ne duk bata taso ba. kuma bawai na rubuta wannan kasida bane don in faranta ma Ribadu rai ko magoya bayansa ba, a'a ni gaskiyan lamari ne kawai na fadi gwargwadon sanina.

ya kamata mu fahimci cewa gaskiya fa dayace kuma daga kinta sai bata-Ribadu yayi iya bakin kokarinsa, domin kuwa ya sadaukar da kansa da rayuwarsa ya bautawa Nijeriya, don haka inhar baza'a gode masaba, to bai kamata a tsine masaba. Hukumar EFCC karkashin jagorancin Ribadu a wancan lokaci bata ragama kowa ba komai girman mutum a kasar nan in har ankamasa da yin almubazzarancin da dukiyar al'umma, yayi aikinsa batare da nuna sanayyaba, wanda hakan ga dukmaison gaskiya yasan cewa shine adalci, bawai a kyale yan lele surika cin karensu babu babbakaba, wadanda basu da gata kuma a musguna masu. koda yake banyi mamakin masu irin wannan suka marasa ma'ana akan Ribadu ba, domin kuwa kashi casa'in cikin dari na wadanda suka aikomun da ra'ayinsu kan kasidar tawa manya mutane ne a kasarnar, wata kila aikin malam Ribadu ya shafi wasu nasu ne ko su kansu. Amman hakan bai kamata yasa murika take gaskiya mu maidata karya ba, kada son zuciya ta rika dibanmu murika kinyinma kanmu adalci akan lamuran yau da kullum.

Zaiyi kyau idan zamu rika yinma kanmu adalci idan mutum yayi aikin alhei a fadi, haka kuma idan yayi akasin hakan shima a fadi kuma a nuna masa yadda zai gyara. Tayin hakane kawai zamuci gaba bawai ta fadin son rai da suka marasa ma'ana ba. Koda yake, sanin kowane a yau babu wanda za’a nunasa ace dari bisa dari shi tsarkakakkene, ma’ana bai dadan kuskure tare dashi, don haka Ribadu kamar sauran mutane na iya yin kuskure yayin gudanar da aikinsa domin shi dan adamne kuma baifi karfin yin kura kurai ba, amma duk da haka bazaiyi kyau a garemu ba idan muka ce zamu boye ayyukan alheri dayayi a kasar nanba.
Alal hakika wannan hali da Malam Nuhu Ribadu ya shiga ciki abin kunya ne ga Nijeriya, ace mutane kamar su Ribadu wadanda suka sadaukar da rayuwarsu sukayi aiki tukuru an kasa saka masu da alheri sai aibantasu akeyi. Tababs wannna koma bayane ko shakka babu, gwamnatin nijeriya ta gaza wajen kare mutuncin Ribadu da kimarsa. Hakan kuwa manuniyace ga yan baya wadanda keda kudirin bautawa kasarnan da kada ko kusa suyi tunanin yin haka, domin suma nasu zata samesu kamar yadda ake cin zarafin Ribadu duk da irin gudunmuwar daya bayar wajen ci gaban kasrnan.

Hakika suma sarakuna da shugabannin arewa sun gaza matuka gaya kan rashin tsoma bakinsu kan wannan tsangwama da cin zarafi da akema Ribadu. Ya kamata shugabannin arewa suyi kokarin nemarmasa yancinsa na dan kasa kuma suyi kiran a gaggauta dakatar da wannan tsangwama da ake masa, don kare kimarsa a idon duniya. Abin bakin cikine yadda akasamu daya daga cikin shugabannin arewa ya fito fili yana nuna jin dadinsa kan halin da wannan bawan Allah yake ciki.

Daga karshe, zanjawo hankalin masu irn wadannan suka susan cewa bantaba yin kwai naba saida zakara, don haka ya kamata mu ajiye son zuciya a gefe, don samun cigaba. Har ila yau, bazan gaji da kira ga talakawa da masu murajin tabbatar da gaskiya da adalci a kasarnan ba da suci gaba dayin addu’a don Allah ya kubutar da wannan dan mutaliki, adali kuma haziki kan azzaluman mutanen da sukasa shi a gaba. Allah yayi mana jagora, amin.

Wednesday, January 21, 2009

BUSH'S AND OBAMA'S ADMINISTRATION: WILL THERE BE ANY CHANGE?

Nobody could believe that it would happen. Likewise, had it been that we have read it, it is now a reality. It’s no longer a dream, a myth, or a fallacy. It was yestarday, the 20th day of January, 2009, when and where impossibilities turned into possiblities. For it was a historical day, date, and year, where the first black African, in person of Barrack Hussain Obama, was sworn-in as the 44th American president. It was really a massive turn-out pf people from every nooks and crannies of the world to the city of Washington for witnessing the historical event.

With the exception of the former American president, John F. Kennedy, Obama has enjoyed and indeed is enjoying an unprecedented support of Americans. With a black man and African by origin occupying the white house as an American president, certainly and without any iota of doubt a new chapter has now been opened in the political history of America, in particular, and the world in general. And to this end, we are saying kudos to the late Martins Luther King (jnr) who fought against racism and the liberation of the blacks in America. This is because the dream he had for many years has now turned into reality. Wherein he dreamt that there would be a day in which a black and a white man will eat in the same plate, marry each other and react with each other.

Today, all the blacks, not only in America but also across the world, are jubilating for seeing their black counterpart steering the executive powers of America and Americans. To them (blacks), this is a clear indication of putting into finality the long-aged racism in America. To cut the long story short, the African countries, including his (Obama) country of origin, that is Kenya, are left with their arm in akimbo, awaiting him (Obama) with alacrity to see what positive changes could he brought to them.

However, the African countries seems to have forgotten or wittingly ignored the fact that Obama was not elected by the Africans but rather by the Americans. As such and with greatest respect to such unreasonable expectations by the Africans, what Obama can only do Africa and Africans is nothing more than what his predecessors has done of financial assistance whenever the need arises.

Surely, obama will be facing numerous challenges, such as; the current economic crises, international politics, security and peace of the world, putting things in order in the middle-east, and above all, regaining the lost prestige of America during the time of Bush (Jnr).

Although, in his speeches, after taken the oath of office, Obama has promised to repatriate all the Americans soldiers that are currently on mission in Iraq as well as shutting down the guantanamo-bay. These tallies with what he had promised in the course of his campaigning. He went further and communicated to the world by saying that America is and will remain to be a friend to all nations and he gave his word of assurance to the world that there will be a good and cordial relationship in this kind of friendship with the whole world in general and the muslims countries in particular. One interesting thing with his speech was the way and manner he successfully distinguished himself from people like Bush (Jnr) by saying that they will be definitely remembered by people upon what they have built not upon what they have destroyed. This is whole heartedly welcomed by Americans and the whole world, for they hate to be taken back to where they were in the era of their former president Bush (Jnr). But, the main question is how could he achieve those ambitions and promises? Certainly, there is a high need for president Obama to know who is who to go with in his administration. The right thinking people and the people with a foresight and high caliber are, without any doubt, the right persons Obama should go with.

However, the most devastating thing is how the American secretary of state, Mrs. Hillary Clinton, came openly few days before their inauguration and commended the barbarity and brutality of Israel over the inhabitant of Gaza. That commendation of her was really really unbecoming. She ought to have sympathized with the innocent people of Gaza, condemned the inhuman acts of Israel and shown her readiness to contribute immensely on how to tackle the absence of peace in Gaza without any fear or favour whatsoever. I may be right if I say that people like Hillary Clinton are likely to bring obstacles in this current administration of Obama. To crown it all, all eyes are now on Obama to see how can he face and tackle what is currently happening in Gaza. Contrariwise, many people are of the view that the world will experience no changes during the reign of Obama, because wherever he is, an American is an American and carries along with him an American policy(ies). Now, the one million dollars question is “will Obama be a man in a million and deliver the goods?” expecially taking into consideration the absence of cordial relationship between America and the majority of the rest of the world during the draconian tenure of Bush (Jnr) in office.

Whatever the case may be, only time can prove (within his first year in office) whether Obama can take Americans and the world to the promise land.

SHIN ZATA CANJA ZANI A AMURUKA KUWA?

kamar a mafarki, a ranar talatan data gabatane ashirin ga watan janairun wannan shekarar aka rantsar da Barack Obama a matsayin shugaban kasar Amuruka na arba'in da hudu. Miliyoyin jama’a ne daga wurare daban daban sukayi cincirundo a birnin Washington don halarta da kuma cire kwantsar ido a wanna rana mai cike da dimbin tarihi. Obama dai yasamu goyon bayan amurukawa da yawa da kuma farin jini inda yakasance shugaban amuruka na biyu da amurukawan suka nuna masa kauna sosai bayan John F. Kennedy. Alal hakika kasancewar sa amatasayin shugaban amuruka ya bude sabon babi a siyasar amuruka dama duniya baki daya musamman ma ganin cewa shi bakin fatar amuruka ne. Yau dai gashi shekaru da dama sunwuce, amman mafarkin da dan fafutukar yaki da wariyar launi a amuruka Martins luther king junior yayi ya zamu gaskiya, inda yayi mafarkin cewa watan wata rana za'a samu farare da bakake suna cin abinci tare kuma suna hulda. Yau bakaken fata a amuruka dama sauran kasashen duniya sai farin ciki suke wanda baya musaltuwa ganin cewa gashi ansami bakin fata dan afirika na farko dake jan ragamar mulkin amuruka, kasar da ake ganin bazata taba bari baki ya mulketa ba.Hakan kuwa ana ganin ya kawo karshen nuna wariyar launi a kasar. Hatta akasar shi ta haihuwa wato kenya da sauran kasashen afrika da dama sun nuna farincikinsu kan wannan rana inda suke fatan shi shugaban na amuruka kuma dan afrika zai kawo sauyi mai amfani a afrika. Wani abinda yan afrika suka manta shine, Obama dai amurukawa suka zabesa don haka duk wanna tunanin da sukeyi na cewa wai zaifi bada fifiko ga kasashen afrika ba zai taba yiwuba. Abin kawai da zai iya yi shine, kamar yadda wadanda ya gada suke bada tallafi ga nahiyar afrika, shima ya kokarta yayi hakan inkuma da hali ya kara fiye da yadda sukayi.
Hakika Obama zai fuskanci kalu bale da dama kamar dai tabarbarewar tatalin arziki, siyasar duniya, tsaro, rikicin gabas ta tsakiya, sai uwa uba dawo da kimar amuruka a idon duniya da dai sauransu. koda yake, ajawabinsa bayan yayi rantsuwar kama aiki obama ya dada jaddada kudirinsa na janye sojojin amuruka dake iraqi, da kuma rufe sansanin guantanamo wanda dama tun lokacin yakin neman zabensa yayi wadannan alkawurran. Bai tsaya nan ba, domin kuwa yace Amuruka kawar dukkan kasashen duniya ne, inda ya dada bada tabbacin yin hulda ta kakkyawar hanya da kasashen musulmai da ma sauran kasahen duniya. Wani abin sha’awa da wannan rana shine yadda Obama ya banbance gari da tsakuwa, inda yace al’umma zasu rika tunawa da shugabanninsu kan abinda suka gina na alheri ba abinda suka ruguza ba. Wanna furucin ya yiwa amurukawa da kasashen duniya dadi matuka gaya, domin kuwa basa fatan fitunonin da tsohon shugaban kasar Bush ya sakasu a ciki ya kara faruwa. Amman wai ta yaya zai cimma wadannan kudirorin nasa? Tabbas akwai bukatan shugaba Obama yasan wadanda zai nada a matsayin mukarrabansa da zasu taimaka masa wajen cimma wannan burin nasa. Mutane masu hangen nesa da sanin yakamata sune kadai zasu dace da tafiyar nasa. Wani abin shakku da kuma ban tsoro shine yadda sakatariyar harkokin wajen amurukan Madam Hillary Clinton, kwanaki kadan kafin a rantsar da gwamnatin nasu ta fito fili ta nuna goyon bayan Israela kan kisan kiyashin da tayi a zirin Gaza. Wannan furucin nata ko kadan bai daceba, kamata yayi taba da nata gudunmuwar yadda za a shawo kan rikicin na Gaza ta hanyar diflomaciyya, ba tare da nuna goyon bayan ko wani bangareba. Alal hakika, irin su Hillary Clinton zasu iya kawo cikas da koma baya kan wannan tafiya wanda yana cike da buruka da dama.
Yanzu dai duniya tasa ma Obama ido taga irin rawar da zai taka da kuma yadda zai tunkari rikicin gabas ta tsakiya da dai sauransu. Saidai kuma a bangare daya, mutane da dama na ganin ai bazata sake zani ba, domin wai ba Amuruke har abada shi ba Amuruke ne akidarsu tanan tare dasu. Babbar ayar tambaya a nan itace, shin Obama zai ba marada kunya ya cikama amurukawa alkawurran da ya dauka da kuma yin hulda ta hanyar diflomaciyya da sauran kasashen duniya? Musamman ma ganin yadda dankon zumunci tsakanin amuruka da kasashen duniya yayi tsami sakamkon mulkin kama karyar da mista Bush yayi a lokacin mulkinsa. koma yazata kasance za'a gani a cikin shekarar farko na mulkinsa da zaiyi.

Tuesday, January 13, 2009

GAZA GENOCIDE: FAILURE OF ARAB LEADERS.

The war on Gaza has become shameful to the Arab leaders since they can not call for urgent and immediate ceasefire and an end to the blockade. They (Arab leaders) lost their voices and become dumb since the war on Gaza started where more than nine hundred palastinies have been killed, leaving Tens of thousands wounded and homeless. Its indeed a failure to arab leaders, since they did not show their concern about it and did not also call for immediate ceasefire and an end to this blockade.Its high time therefore for all muslim ummah to boycott goods from Israel and America as a way of protesting. May Allah protect the palastinies from attack by the Israeli troops.

Friday, January 9, 2009

A DAKATAR DA RUWAN BAMA BAMAI A GAZA.

Harin bama bamai da israela ta kaddamar a karshen watan disamban shekarar data gabata a yankin zirin Gaza abin ayi tir, da kuma Allah wadai dashi ne. Domin kuwa yakin ya jefa palasdinawa cikin halin kaka nakayi na rashin abinci, ruwan sha, wutar lantarki da dai sauransu baya ga hasaran rayuka da dukiyoyi. Hatta harkar sadarwa ta yanke saboda rashin wutan lantarki, wadanda suka jikkata basa samun cikakken kula a asibiti, wanda hakan kansa su mutu daga karshe.
Wannan danyen aiki da Israela take aikatawa a Zirin Gaza ya kai intaha, domin kuwa ya maida yara da dama marayu, wasu matan sun rasa mazajensu, a wani bangaren kuma maza sun rasa matayensu da ‘ya ‘yansu, gidajen jama’a sun salwanta da kuma dukiyoyi inda jama’a da dama yanzu suke gararanba a gari suna neman wajen tsugunawa duk a sanadiyyar wannan kazamin fada dayaki ci yaki cinyewa.
Wani abin ban haushi da takaici shine yadda majalisar dinkin duniya ta nuna halin ko inkula ga mummunar ta’adin da Israela keyi wa palasdinawa, tayi gum taki cewa komai. Hakan kuwa bai dace ba domin kuwa majalisar dinkin duniya nada cikakken ikon tsawatarwa Israela don dakatar da harin bama bamai da take yiwa palasdinawa. Yanzu ya fito fili karara, musamman ma ganin yadda yar sandan duniya wato kasar amuruka taki cewa uffan kan lamarin, da kuma halin ko oho da majalisar dinkin duniya ta nuna cewa suna da ra’ayi akan lamarin. Domin kuwa, hakkin majalisar dinkin duniya ne ta sasanta kasashen cikin lumana da diflomaciyya, amman taki yin hakan ta zurawa Israela ido tana cin karenta ba babbaka a Zirin Gaza. Akwai bukatan majalisar dinkin duniya ta sake salon yadda take tafiyar da lammuranta, ma’ana ta rikayin adalci da kuma cin gashin kanta basai tajira wata kasa ta bata umurni ba. Koda yake, kin daukan mataki da majalisar tayi a kan Israela wani umurni ne daga amuruka. Domin kuwa amuraka ce ke tafiyar da harkokin majalisar dinkin duniya, har ila yau hedkwatar majalisar na kasar amuruka, don haka shiyasa amuruka ke taka rawar da taga dama ta sanadiyar sake da nuna rashin iya aiki da majalisar tayi.
Yin biris kuwa da kasashen larabawa sukayi kan wannan lamari, suka ki taimakawa palasdinawa don tsoron kada amuruka tasa masu takunkumi ko ta kirasu yan ta’adda wallahi yazamo babban abin kunya da kuma hasara garesu. Domin kuwa Israela ba ita kadai ke aikata wannan kisan kiyashin da takeyi a zirin Gaza ba, tana samun taimako amma su larabawa sunkasa taimakawa yan uwansu. Tabbasa dole a jinjinawa kasashen masar da faransa kan namijin kokarin da sukeyi wajen ganin an kawo karshen wannan zibda jini da akeyi. Hakika kiran dakatar da ruwan bama bamai a zirin Gaza da kashen biyu sukayi, dakuma kiran a zauna a teburin shawara abin ayi maraba da shine kuma a yaba masu matuka gaya . Domin kuwa ta hakane kawai za’a iya warware rashin jituwa dake tsakanin israela da kungiyar Hamas na palasdinu. Abin fata a nan shine, Allah yasa wannan matakin da masar da faransa ke son cimma ya haifar da da mai ido, a kuma samu nasara . Lokaci yayi da kasashen musulmi zasu yi kiran a dakatar da ruwan baba bamai a gaza, da kuma nuna rashin jin dadinsu da kisan bayin Allah da Israela keyi a zirin Gaza, don su san cewa fa abinda suke aikatawa bai daceba, kuma baza a kyalesu su cigaba da wannan ta’addi ba.
Hakika al’ummar palasdinawa na wani hali na kunci, rashi da kuma tausayi duk sakamakon wannan bala’in ba Israela ta jefasu ciki, don haka muna tayaku addu’ar allah ya kareku da karewarsa, ya tsareku da tsarewarsa, ya kuma fidda ku daga cikin wannan halin kunci da kuka samu kanku a ciki.