Thursday, September 29, 2011

Jawabin Shugaban Kungiyar Gizago A Taronta Karo Na Uku Da Akayi A Katsina


JAWABIN SHUGABAN KUNGIYAR GIZAGO NA KASA A TARONTA KARO NA UKU DA AKA SHIRYA A JAHAR KATSINA RANAR 25/9/2011, A DAKIN TARO NA KATSINA MOTEL.

Da sunan Allah mai rahma mai jin kai. Ya ‘yan uwana gizagawa, tare da sauran manyan baki, ina cike da farin ciki tare da yimaku barka da zuwa wajen taron kungiyarmu mai albarka ta GIZAGO a Jihar Katsina ‘dakin kara’.
• Kamar yadda mafi yawancin mu suka sani, an kafa kungiyar Gizago a Jaridar Aminiya cikin watan Aprilu, 2008 don sada zumumnci, amma daga baya ‘ya’yan kungiyar suka fadada ayyukanta zuwa habaka harshen hausa da inganta al’adun gargajiya da kuma bada taimako ga ‘ya’yan kungiyar da sauran al’umma. Kuma hedkwatar wannan kungiya na kasa yana Jihar Katsina ne. A takaice manufofin wannan kungiya sune:
1. Habaka harshen hausa. 2. Inganta al’adun gargajiya. 3. Sada zumunci 4. Bada tallafi ga ‘ya’yan kungiya da sauran al’umma.
• Anyi taron farko na wannan kungiya a Jihar Kano a shekarar 2009 inda uban kungiya kuma babban bako a wannan rana Dr. Bala Muhammad ya gabatar da lacca akan muhimmancin raya al’adun Hausa, kuma wannan ne karo na farko da ‘ya’yan kungiyar suka san junansu ido-da-ido domin kuwa da a Jaridane kawai ake sada zumunci da yin wasu al’amurra da suka shafi kungiyar.
• Taro na biyu anyishi ne a Kaduna Birnin Gwamna a shekarar 2010, kuma taron ya maida hankali ne kan bunkasar harshen hausa a duniya inda Farfesa Dalhatu Muhammad na Jami’ar Ahmadu Bello dake Zariya ya gabatar da laccar. A wannan karon kuma, wato taron kungiyar na uku wanda akeyi yau a Birnin Katsina Fadar Gwamnatin Jihar Katsina, za’a tattaunane a kan irin gudunmuwar da matasa zasu bada wajen habaka harshen hausa da inganta al’adun Hausawa, kuma Farfesa Ibrahim Malumfashi Shugaban Sashen harshen Hausa na Jami’ar Jihar Kaduna zai gabatar da laccar.
• A bangaren habaka harshen hausa da kungiyar keyi, as samu ci gaba sosai domin kuwa an samu daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar mai suna Malam M.S. Suleiman zaria ya wallafa littafi mai suna BAZAZZAGIYA wanda aka kaddamar a taron kungiyar karo na biyu da akayi a Kaduna. Kuma littafin yayi bayani kan wasu Sarakunan Arewa, da kuma dangantakar barkwanci tsakanin zagezagi da kanawa. Haka kuma, dan kungiyar mai suna Ado Ahmad Gidan Dabino, wanda sananne ne a duniyar marubuta, shima ya wallafa littafai da dama cikin harshen Hausa.
• Wajen bada tallafi kuwa, kungiyar nan ta bada tallafin kudi da kayayyaki na dubban nairori ga wadanda rikicin Jos ya afka masu a farkon shekaran 2010. Har ila yau, kungiyar nan a karkashin rassanta na wasu Jihohi ta bada tallafi ga gidajen marayu, nakasassu, gidan yari, makarantu da dai sauransu. Amma munaso a fahimcemu cewa, bawai muna fadin wadannan ayyuka bane don mutane su yaba mana, a’a muna fadine don jama’a su san cewa wannan kungiya ta Gizago ba Kaman sauran kungiyoyi bane, domin kuwa a kullum tana aiwatar da manufofinta, kuma tana fadin ayyukanta ne don sauran ‘ya’yan kungiyar su zage dantse wajen bada gudunmuwa don ganin ankai ga tudun muntsira.
• Kungiyar Gizago ta fara ne da mambobin da basu kai guda 20 ba, amma a yau, kungiyar na da mambobi 2022, kuma kungiyar na da rassa a sama da Jahohin Nijeriya ashirin da kuma wasu daga cikin kasashen ketare, domin kuwa a yanzu haka dinnan muna da mambobinmu na rassan Jamhoriyar Nijar acikin dakin taron nan tare da mu wadanda sukayi takakkiya tunda ga kasarsu don halartan wannan taro mai dimbin mahimmanci.
NASARORI.
• Dan gane da nasarorin da kungiyar Gizago ta samu kuwa sune, an samu damar rubutawa da kamala kundin tsarin mulkinta kuma an kaddamar da wannan kundi ga ‘ya’yan kungiyar A Kano a shekarar 2010. Har ila yau, bayan kwashe shekaru ana ta fadi ta shin yin rijista da hukumar dakema kungiyoyi da kamfanoni rijista, a yanzu an samu damar kammala wannan rijistar da hukumar C.A.C. hakika wannan ba karamin nasara bane domin kungiya yanzu bata da wani fargaban gudanar da taro ko ayyuka a ko ina cikin kasar nan harma da ketare domin ta cika dukkan sharuddan da gwamnati ta gindaya kafin ayi mata rijista. Har ila yau, kungiya ta bude shafi a duniyar gizo inda ake musayan ra’ayoyi tsakanin mambobinta da sauran al’umma a ko ina cikin duniya.
• Wannan kungiya a kullum sai kara karbuwa takeyi a ko ina tare da samun yabo kan irin ayyukan da take gudanarwa. Domin kuwa, hatta kungiyar muryar talaka mai fafutukan ganin anyi mulkin adalci ta yaba da aikinmu inda ta bamu takardan shaidan yabo a taronta na farko da tayi a shekarar da ta gabata.


• Amma fa inason kusan cewa dukkan irin nasarorin da wannan kungiya take samu ya biyo bayan irin gagarumin gudunmuwar da Madugu uban tafiya, limamin sada Zumunci, Direban Jirgin Gizagawa Malam Bashir Yahuza Malumfashi keyi wajen aiki tukuru don ganin kungiya ta samu nasarar gudanar da ayyukanta- tare kuma da irin damar da kamfanin Jaridar Aminiya ke bamu wajen ci gaba da yada manufofinmu. Hakika sun cancanci a yaba masu, don haka muna rokon Allah madaukakin sarki ya albarkaci kamfanin MEDIA TRUST.
• Haka suma iyayen wannan kungiya, Dr Bala Muhammad, Mahmoon Baba-Ahmad, Ado Saleh Kankia, Dr Yusuf Adamu da Alhaji Bello lawal, da sauran iyayen kungiya a matakan Jihohi ya zama dole a yaba musu kan irin gudunmuwa da kuma lokacin da suke bawa wannan kungiya a ko wane lokaci. Wannan kungiya na alfahari daku a kowane lokaci, dafatan zaku ci gaba da bada goyon bayanku kan ayyukanta da kuma shawarwari don ganin ankai ga tudun muntsira. Suma shugabaninnin wannan kungiya wadanda lokaci ba zai bada daman a bayyana sunayensu ba, sun cancanci a yaba masu matuka kan irin namijin kokari da sukeyi wajen hada kan mambobin kungiyar tare da yin ayyukan dake kawo ma kungiya ci gaba. Haka suma ‘ya’yan kungiyar ya zama dole a yaba masu kan irin hadin kan da suke bayarwa don ci gaban kungiya, da fatan zasuci gaba da bada hadin kai a ko wane lokaci.
• Kafin in kammala wannan jawabi, zanso in sanar da dukkan wanda ke dakin taron nan cewa a shekaru 3 nan da muka kwashe, dukkan ayyukan da kungiyar nan keyi da kuma gudanar da taronta na shekara shekara, da kuma bada tallafi da takeyi da dai sauran ayyuka, dukkan kudaden yana fitowane daga aljihunta. Ma’ana, daga ‘ya’yan kuniyar. Sune sukan sanyama kansu haraji su tara kudaden da ake bukata. Don haka, a yau, kungiya zata gabatar da neman gudunmuwa don samar da Ofishinta na dundundun a Jihar Katsina, tare kuma dayin sauran ayyukan da ta saba.


HARSHEN HAUSA.
• Har ila yau, zanso in sanar daku cewa, don ganin harshen hausa ya bunkasa a ko ina, kungiyar Gizago a shekara mai zuwa zata maida hankali ne wajen fadakar da daliban makarantun sakandire da jami’o’i musamman hausawa dasu rungumi wannan harshe nasu na iyaye da kakanni, tare kuma da taimaka masu da litattafan karatun hausa gami da shirya taron bita gasu daliban kan yadda ya dace su rika karatu da rubutun hausa, musamman ganin cewa matasa hausawa yanzu basason karanta littatafan hausa da kuma yin rubutun hausa. Don haka zamuyi maraba da duk wata irin gudumuwa da zamu samu daga gareku don cimma wannan manufa da muka sanya a gaba. Wannan kungkiya tana adduar Allah ya jikan marubutan Hausa irin su Marigayi Abubakar Imam, da dai sauransu domin kuwa sun bada gagarumin gudunmuwa wajen bunkasar harshen Hausa. Haka kuma, Kungiyar Gizago na sake jinjina da yabawa ga Alhaji Bashir Usman Tofa, Dr Bukar Usman, Mallam Bashir Yahuza Malumfashi, Ado Ahmad Gidan Dabino, Mallam M.S Sulaiman Zaria, da suran Marubuta kan irin gudunmuwar da suke bayarwa a halin yanzu wajen bunkasa Adabin Hausa. Muna rokon Allah madaukakin Sarki da ya kara masu basira da hikima kan wannan aiki da sukeyi.
• Daga karshe, muna addu’ar Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, haka kuma muna addu’ar Allah yasa ayi taro lafiya a gama lafiya, kuma bakinmu na nesa da kusa kowa ya koma gida lafiya.

Wassalam
Naku har kullum
Mallam Muntaka Abdul-Hadi Dabo
(Sardaunan A Bari Ya Huce)
National chairman,
Gizago

Tuesday, May 3, 2011

EPITAPH TO YAR'ADUA AND THE PRESENT STATE OF THE NATION


Day in, day out, every soul will surely taste the bitterness of death. Whosoever has come to the end of his life, a second will not be added to him. May 5th, will remain unforgettable to many Nigerians because of the shocked news they received. It was on that day that the then president and commander in chief of the armed forces Mallam Umaru Musa Yar’adua answered the call of Almighty Allah, after a protracted illness. As we all know, Yar’adua was (s)elected as president in 2007 through an election that was full of malpractices. Though, Yar’adua himself admitted that the (s)election that brought him to power was characterized by an unprecedented election malpractices in the history of Nigeria, and that necessitated him to constitute a committee under the chairmanship of the former chief Jutice of the federation justice Muhammad Lawal Uwais to look into the matter and come up with a lasting panacea to the problem. And he (Yar’adua) also promised to conduct a free and fair election in 2011(i.e. the just concluded election last month) that will be accepted by all Nigerians and the world in general, but he did not live long to actualize his dreams.

When he came to power in 2007, late Yar’adua showed a good sense of respect to all the arms of government by allowing them to discharge their responsibilities without disrupting them. The judicial arm, which is the last hope for the poor man enjoyed full autonomy in his tenure. This was corroborated by the fact that he (Yar’adua) remained dumb when the election tribunals nullified the (s)election of his party candidates (PDP) at various level of government on the ground of electoral malpractices. The former C-in-C, without any iota of doubt showed a sense of maturity in that respect which was never obtained in Obasanjo’s era and this present administration.

While he lived, Yar’adua was cool headed unassuming person who gave everybody his due respect. A man who stood for justice, fair play and equity. Surely, he will be remembered for his quiet dignity, sincere believe in rule of law, commitment to Deeping democracy and landmark resolution of Niger Delta crisis, etc. no doubt, Katsina state and Nigeria has lost an honest leader who meant well for his people. He is no longer with us, but Nigerians would surely be guided by his spirit of exemplified humility, and they will never relent in praying for the repose of his soul.

During his tenure, there was peace in the country and we never had a bomb blast in the three years he spent steering the mantle of leadership in Nigeria as its number one citizen. Unlike what is happening now, bomb blast in all angles of the country, killing of innocent people by police on high roads, etc. it’s very shameful that even the first bomb blast took place at eagle square on October 1st, last year when Nigeria was celebrating her 50th anniversary as a sovereign nation- followed by the one on Xmas Eve, another one on election Eve and during election in some part of the country, to mention but few, where several people lost their lives and many were injured. Imagine what we used to hear before in Afghanistan , Baghadaza, and Somalia , we are now hearing and witnessing it in our own dear country. This is certainly a big problem and if care is not taken, Nigeria will in no distant time (though we are not praying for it) become another Baghadaza, especially Borno State where the case is more rampant.

I can boldly now say, without fear of contradiction that insecurity has become a daily business in Nigeria and Nigerians are used to it. But it’s very annoying that the present administration has been doing nothing to find a lasting solution to the problem. Is this how we are going to continue? If things should continue the way they are now, what will Nigeria become in the next few years? Only time can tell, and it’s quite unfortunate that we did not make a right choice in the last month elections, where we allowed the same bunch of liars and looters to rule us again. We have forgotten the situation we found ourselves in the last years, and still we are going to face it again for another good four years- what a pity! It’s my candid opinion that the Northern part will suffer a lot, because the so-called northern leaders in the north have sold the right of their people to the politicians.

We all witnessed what happened in some of the northern states when the presidential election result was announced, and the upheavals led to the loss of lives, properties of millions naira were vandalized, thousands of people fled their houses, etc and these so-called leaders in the north are the caused because they don’t protect the interest of their people. They only protect their interest and pocket. Even Chief Obasanjo, the former President of this country confirmed this when he said to Jonathan “the northern leaders are ravenous and egocentric. Use what their brother (Yar’adua) left behind and bribe them, they will vote for you” imagine! Surely, the northern part will continue to remain where they are if their so-called leaders did not change, and their children will definitely continue to be slaves forever and remain backward in terms of education.

Conclusively, the upheavals in the northern part should serve as a deterrent to our leaders, and know that Nigerians are pushed to the wall and they can stand up and fight for their right whenever the need arises! A word, they say, is enough to the wise.