Tuesday, July 28, 2009

TABARBAREWAR ILIMI A NIJERIYA.



TABARBAREWAR ILIMI A NIJERIYA.:ummul aba isin yajin aikin jami'o'i



Yau a Nijeriya, harkan Ilimi ya shiga halin ko in kula da kaka ni kanyi saboda irin rikon sakainar kashi da rashin bashi muhimmanci da wadanda alhakin abun ya rataya a kansu.Akwai abin takaici kwarai da gaske idan mutum yayi la'akari da irin halin kuncin da wasu mutane suke ciki wadanda rayuwarsu ke da matukar tasiri ga kasarmu, amma aka kyalesu cikin bakar wahala sakamakon wani tsari na mulkin mallaka da ba kowa ke cin gajiyarsa ba. Wadannan mutane sun kasance tsani da mutum kan taka har ya kai ga wani matsayi a rayuwarsa. har ila yau wadannan mutane suke dasa harsashin ganin fadi-tashin da mutum keyi a rayuwarsa har ya cimma wani matsayi ko nasara a rayuwa.



wadannan mutane ba wasu bane illa malaman makaranta wadanda dan abin da suke samu bai taka kara ya karya ba in aka kwatantashi da irin aikinsu na sadaukarwa. Matsayin malaman makaranta ga ginin kasa da al'umma al'amari ne da ba ya misaltuwa. Komai matsayin mutum, duk yadda ya kai da daukaka a rayuwa sai da yabi ta hanyar malamai kafin ya cimma wannan matsayi.



yajin gama gari da malaman jami'o'in kasar nan keyi abin kunya ne ga wannan gwamnatin karkashin jagorancin Alhaji Umaru Musa Yar'adua, wanda shima tsohon malamin makaranta ne amman yayi biris da bukatunsu, yaki yaji kukansu balle ayi tunanin share masu hawayensu.

yau a kasarnan, dalibai kan shafe shekara takwas suna karatun da ya kamata ace anyisa a shekara hudu saboda yajin aiki da malam kanshiga lokaci zuwa lokaci, yayinda takwarorin karatunsu da kanje kasar malaysia ko Amurka kan share shekara uku kacal don samun digiri daidai da na nijeriya da akan kwashe shekara takwas ana yinsa sakamakon yajin aikin. malamin makaranta ba'a dauke shi a bakin komai ba a Nijeriya, bashi da daraja a idon shugabanni da su kansu daliban, duk kuwa da cewa duk wani shugaba dake tun kaho a kasar nan dama duniya baki daya malamin makaranta shine tsanin farko da yabi har ya kai ga wannan matsayi da yake.





Wannan karara ya nuna hujjar da malaman jami'o'i ke da ita ta shiga yajin aiki saboda irin halin ko-in-kula da gwamnatocin da aka yi a kasar nan suka rika nunawa game da batun kyautata rayuwar malaman. Don gwamnatin 'Yar'aduwa ma tafi kowacce nuna halin ko-oho game da mummunan matsayin da malaman jami'o'i ke ciki, sai tafi mayar da hankali ga biyawa 'yan majalisu burinsu na wasoso akan dukiyar jama'a. Yayin da aka yarjewa dan majalisa ya rika kwasar Naira miliyan goma (N10,000,000) a kowane wata, wani malamin jami'an idan kaji albashinsa sai ka rike baki kana salati, don kuwa abin ba'a cewa komai. koda yake ba komai ya haifar da rikon saikanar kashi da shugannin keyiwa harkar ilimin kasar nan ba face cewa 'ya 'yan su basa karatu a kasar nan, sun turasu kasashen waje suna biyamasu kudin karatun nasu da dukiyar al'umma.



Ilimi dai shine kashin bayan ci gaban al'umma, amma wadansu na kokarin gurguntashi saboda tsabar keta. Ya kamata Gwanmatin Yar'adua ta gaggauta daukan mataki don kawo karshen wannan yajin aikin gama gari da jami'o'in kasar nan keyi don baiwa dalibai samun zarafin kammala karatunsu a kan lokaci.

Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukanmu na alhairi, amin.

YAWAN MUTUWAR AURE: WAKE DA LAIFI?

HAKIKA

Monday, July 13, 2009

CE-CE KU CE KAN ZIYARAR OBAMA ZUWA GHANA

Tun bayan da shugaba Barack Obama na Amurka ya bayya aniyarsa ta kai ziyara zuwa kasar Ghana, al'ummar Nijeriya keta ce-ku-ce kan wannan ziyarar ganin Obama bai zabi Nijeriya ba duk kuwa da dimbin tattalin arzikin da kasar keda shi fiye da Ghana, sai kuma uwa uba kallon da akeyima kasar (Nijeriya) a matsayin uwa maba da mama a nahiyar afrika.



Sanin kowane bawai wani abu yasa obama ya zabi zuwa Ghana ba face yadda suke mutuntawa da kuma girmama dimokuradiyya. Hakan ya fito filine bayan halastacce kuma tsarkakakken zaben gama gari na kasar, inda jam’iyar hamayya ta sami rinjaye kan jam’iyar dake mulki kuma aka tabbatar mata da nasarar da ta samu (lamarinda yasha banban da Nijeriya). Rashin yin magudin zabe da satar kuri’u da Ghana batayi ba shi ya kara tabbatar mata da mutunci a idon duniya da kuma nuna yadda kasar ta rungumi akidar dimokuradiyya ta ingantacciyar hanya. Wadan nan sune manyan dalilan da yasa shugaba Obama ya zabi zuwa kasar Ghana bai dauki Nijeriya ba (kasar da magudin zabe, satar kuri’u, zaben kaci-baka-ciba ,baka-ciba-kaci,,cin hanci da rashawa da rashin baiwa yan kasa hakkokinsu ya zama abin ado). Don haka, banga dalilin da zaisa al’ummar Nijeriya musammanma mukarraban gwamnati su rika tada muryoyinsu kan wannan ziyarar da Obama ya kai Ghana ba, domin kuwa kamar yadda Obama yace “amurka zata dada karfafa zumunci da kuma taimakon ta ga kasashen da suka rungumi dimokuradiyya ta halastaccen hanya”. Abin tambaya a nan shine,musamman ma ga wadanda suke korafin cewa Obama yaki zuwa Nijeriya- wai mulkin dimokuradiyya akeyi a Nijeria?



Hakika wannan ziyarar da obama ya kai Ghana ya zama kalu bale ga Nijeriya, kuma hannunka mai sanda ne ga sauran kasashe irin Nijeriya wadanda suka maida mulki kamar gadon gidansu da kuma hawa madafun iko ta ko wani irin hanya. In har Nijeriya na son Obama ya kawo irin wannan ziyarar daya kai Ghana to saifa ta inganta hanyoyin zabe ba tare da yin magudiba, rungumar dimokuradiyya ta halastacciyar hanya, baiwa yan kasa hakkokinsu, sakinmara ga jam’iyyun adawa da kafofin yada labarai masu zaman kansu da dai sauransu. Tabbas yaU Ghana ta zama farin wata sha kallo kuma zakaran gwajin dafi a nahiyar afrika. Ghana ta ciri tuta wajen cigaban al’ummarta duk kuwa da cewa kasar tana daya daga cikin kasashen dage baya wajen tattalin arziki a nahiyar afrika, amma saboda da shugabanni masu kishin ci gaban kasar da take dashi yasa a yau sunfi Nijeriya ci gaba ta ko wani hanya amman banda hanyar magudin zabe da satar dukiyan talakawa. Kalu balenku shugabannin Nijeriya.

Allah yai mana jagoranci a dukkan ayyukan mu na alhairi, amin.