Wednesday, January 21, 2009

BUSH'S AND OBAMA'S ADMINISTRATION: WILL THERE BE ANY CHANGE?

Nobody could believe that it would happen. Likewise, had it been that we have read it, it is now a reality. It’s no longer a dream, a myth, or a fallacy. It was yestarday, the 20th day of January, 2009, when and where impossibilities turned into possiblities. For it was a historical day, date, and year, where the first black African, in person of Barrack Hussain Obama, was sworn-in as the 44th American president. It was really a massive turn-out pf people from every nooks and crannies of the world to the city of Washington for witnessing the historical event.

With the exception of the former American president, John F. Kennedy, Obama has enjoyed and indeed is enjoying an unprecedented support of Americans. With a black man and African by origin occupying the white house as an American president, certainly and without any iota of doubt a new chapter has now been opened in the political history of America, in particular, and the world in general. And to this end, we are saying kudos to the late Martins Luther King (jnr) who fought against racism and the liberation of the blacks in America. This is because the dream he had for many years has now turned into reality. Wherein he dreamt that there would be a day in which a black and a white man will eat in the same plate, marry each other and react with each other.

Today, all the blacks, not only in America but also across the world, are jubilating for seeing their black counterpart steering the executive powers of America and Americans. To them (blacks), this is a clear indication of putting into finality the long-aged racism in America. To cut the long story short, the African countries, including his (Obama) country of origin, that is Kenya, are left with their arm in akimbo, awaiting him (Obama) with alacrity to see what positive changes could he brought to them.

However, the African countries seems to have forgotten or wittingly ignored the fact that Obama was not elected by the Africans but rather by the Americans. As such and with greatest respect to such unreasonable expectations by the Africans, what Obama can only do Africa and Africans is nothing more than what his predecessors has done of financial assistance whenever the need arises.

Surely, obama will be facing numerous challenges, such as; the current economic crises, international politics, security and peace of the world, putting things in order in the middle-east, and above all, regaining the lost prestige of America during the time of Bush (Jnr).

Although, in his speeches, after taken the oath of office, Obama has promised to repatriate all the Americans soldiers that are currently on mission in Iraq as well as shutting down the guantanamo-bay. These tallies with what he had promised in the course of his campaigning. He went further and communicated to the world by saying that America is and will remain to be a friend to all nations and he gave his word of assurance to the world that there will be a good and cordial relationship in this kind of friendship with the whole world in general and the muslims countries in particular. One interesting thing with his speech was the way and manner he successfully distinguished himself from people like Bush (Jnr) by saying that they will be definitely remembered by people upon what they have built not upon what they have destroyed. This is whole heartedly welcomed by Americans and the whole world, for they hate to be taken back to where they were in the era of their former president Bush (Jnr). But, the main question is how could he achieve those ambitions and promises? Certainly, there is a high need for president Obama to know who is who to go with in his administration. The right thinking people and the people with a foresight and high caliber are, without any doubt, the right persons Obama should go with.

However, the most devastating thing is how the American secretary of state, Mrs. Hillary Clinton, came openly few days before their inauguration and commended the barbarity and brutality of Israel over the inhabitant of Gaza. That commendation of her was really really unbecoming. She ought to have sympathized with the innocent people of Gaza, condemned the inhuman acts of Israel and shown her readiness to contribute immensely on how to tackle the absence of peace in Gaza without any fear or favour whatsoever. I may be right if I say that people like Hillary Clinton are likely to bring obstacles in this current administration of Obama. To crown it all, all eyes are now on Obama to see how can he face and tackle what is currently happening in Gaza. Contrariwise, many people are of the view that the world will experience no changes during the reign of Obama, because wherever he is, an American is an American and carries along with him an American policy(ies). Now, the one million dollars question is “will Obama be a man in a million and deliver the goods?” expecially taking into consideration the absence of cordial relationship between America and the majority of the rest of the world during the draconian tenure of Bush (Jnr) in office.

Whatever the case may be, only time can prove (within his first year in office) whether Obama can take Americans and the world to the promise land.

SHIN ZATA CANJA ZANI A AMURUKA KUWA?

kamar a mafarki, a ranar talatan data gabatane ashirin ga watan janairun wannan shekarar aka rantsar da Barack Obama a matsayin shugaban kasar Amuruka na arba'in da hudu. Miliyoyin jama’a ne daga wurare daban daban sukayi cincirundo a birnin Washington don halarta da kuma cire kwantsar ido a wanna rana mai cike da dimbin tarihi. Obama dai yasamu goyon bayan amurukawa da yawa da kuma farin jini inda yakasance shugaban amuruka na biyu da amurukawan suka nuna masa kauna sosai bayan John F. Kennedy. Alal hakika kasancewar sa amatasayin shugaban amuruka ya bude sabon babi a siyasar amuruka dama duniya baki daya musamman ma ganin cewa shi bakin fatar amuruka ne. Yau dai gashi shekaru da dama sunwuce, amman mafarkin da dan fafutukar yaki da wariyar launi a amuruka Martins luther king junior yayi ya zamu gaskiya, inda yayi mafarkin cewa watan wata rana za'a samu farare da bakake suna cin abinci tare kuma suna hulda. Yau bakaken fata a amuruka dama sauran kasashen duniya sai farin ciki suke wanda baya musaltuwa ganin cewa gashi ansami bakin fata dan afirika na farko dake jan ragamar mulkin amuruka, kasar da ake ganin bazata taba bari baki ya mulketa ba.Hakan kuwa ana ganin ya kawo karshen nuna wariyar launi a kasar. Hatta akasar shi ta haihuwa wato kenya da sauran kasashen afrika da dama sun nuna farincikinsu kan wannan rana inda suke fatan shi shugaban na amuruka kuma dan afrika zai kawo sauyi mai amfani a afrika. Wani abinda yan afrika suka manta shine, Obama dai amurukawa suka zabesa don haka duk wanna tunanin da sukeyi na cewa wai zaifi bada fifiko ga kasashen afrika ba zai taba yiwuba. Abin kawai da zai iya yi shine, kamar yadda wadanda ya gada suke bada tallafi ga nahiyar afrika, shima ya kokarta yayi hakan inkuma da hali ya kara fiye da yadda sukayi.
Hakika Obama zai fuskanci kalu bale da dama kamar dai tabarbarewar tatalin arziki, siyasar duniya, tsaro, rikicin gabas ta tsakiya, sai uwa uba dawo da kimar amuruka a idon duniya da dai sauransu. koda yake, ajawabinsa bayan yayi rantsuwar kama aiki obama ya dada jaddada kudirinsa na janye sojojin amuruka dake iraqi, da kuma rufe sansanin guantanamo wanda dama tun lokacin yakin neman zabensa yayi wadannan alkawurran. Bai tsaya nan ba, domin kuwa yace Amuruka kawar dukkan kasashen duniya ne, inda ya dada bada tabbacin yin hulda ta kakkyawar hanya da kasashen musulmai da ma sauran kasahen duniya. Wani abin sha’awa da wannan rana shine yadda Obama ya banbance gari da tsakuwa, inda yace al’umma zasu rika tunawa da shugabanninsu kan abinda suka gina na alheri ba abinda suka ruguza ba. Wanna furucin ya yiwa amurukawa da kasashen duniya dadi matuka gaya, domin kuwa basa fatan fitunonin da tsohon shugaban kasar Bush ya sakasu a ciki ya kara faruwa. Amman wai ta yaya zai cimma wadannan kudirorin nasa? Tabbas akwai bukatan shugaba Obama yasan wadanda zai nada a matsayin mukarrabansa da zasu taimaka masa wajen cimma wannan burin nasa. Mutane masu hangen nesa da sanin yakamata sune kadai zasu dace da tafiyar nasa. Wani abin shakku da kuma ban tsoro shine yadda sakatariyar harkokin wajen amurukan Madam Hillary Clinton, kwanaki kadan kafin a rantsar da gwamnatin nasu ta fito fili ta nuna goyon bayan Israela kan kisan kiyashin da tayi a zirin Gaza. Wannan furucin nata ko kadan bai daceba, kamata yayi taba da nata gudunmuwar yadda za a shawo kan rikicin na Gaza ta hanyar diflomaciyya, ba tare da nuna goyon bayan ko wani bangareba. Alal hakika, irin su Hillary Clinton zasu iya kawo cikas da koma baya kan wannan tafiya wanda yana cike da buruka da dama.
Yanzu dai duniya tasa ma Obama ido taga irin rawar da zai taka da kuma yadda zai tunkari rikicin gabas ta tsakiya da dai sauransu. Saidai kuma a bangare daya, mutane da dama na ganin ai bazata sake zani ba, domin wai ba Amuruke har abada shi ba Amuruke ne akidarsu tanan tare dasu. Babbar ayar tambaya a nan itace, shin Obama zai ba marada kunya ya cikama amurukawa alkawurran da ya dauka da kuma yin hulda ta hanyar diflomaciyya da sauran kasashen duniya? Musamman ma ganin yadda dankon zumunci tsakanin amuruka da kasashen duniya yayi tsami sakamkon mulkin kama karyar da mista Bush yayi a lokacin mulkinsa. koma yazata kasance za'a gani a cikin shekarar farko na mulkinsa da zaiyi.

Tuesday, January 13, 2009

GAZA GENOCIDE: FAILURE OF ARAB LEADERS.

The war on Gaza has become shameful to the Arab leaders since they can not call for urgent and immediate ceasefire and an end to the blockade. They (Arab leaders) lost their voices and become dumb since the war on Gaza started where more than nine hundred palastinies have been killed, leaving Tens of thousands wounded and homeless. Its indeed a failure to arab leaders, since they did not show their concern about it and did not also call for immediate ceasefire and an end to this blockade.Its high time therefore for all muslim ummah to boycott goods from Israel and America as a way of protesting. May Allah protect the palastinies from attack by the Israeli troops.

Friday, January 9, 2009

A DAKATAR DA RUWAN BAMA BAMAI A GAZA.

Harin bama bamai da israela ta kaddamar a karshen watan disamban shekarar data gabata a yankin zirin Gaza abin ayi tir, da kuma Allah wadai dashi ne. Domin kuwa yakin ya jefa palasdinawa cikin halin kaka nakayi na rashin abinci, ruwan sha, wutar lantarki da dai sauransu baya ga hasaran rayuka da dukiyoyi. Hatta harkar sadarwa ta yanke saboda rashin wutan lantarki, wadanda suka jikkata basa samun cikakken kula a asibiti, wanda hakan kansa su mutu daga karshe.
Wannan danyen aiki da Israela take aikatawa a Zirin Gaza ya kai intaha, domin kuwa ya maida yara da dama marayu, wasu matan sun rasa mazajensu, a wani bangaren kuma maza sun rasa matayensu da ‘ya ‘yansu, gidajen jama’a sun salwanta da kuma dukiyoyi inda jama’a da dama yanzu suke gararanba a gari suna neman wajen tsugunawa duk a sanadiyyar wannan kazamin fada dayaki ci yaki cinyewa.
Wani abin ban haushi da takaici shine yadda majalisar dinkin duniya ta nuna halin ko inkula ga mummunar ta’adin da Israela keyi wa palasdinawa, tayi gum taki cewa komai. Hakan kuwa bai dace ba domin kuwa majalisar dinkin duniya nada cikakken ikon tsawatarwa Israela don dakatar da harin bama bamai da take yiwa palasdinawa. Yanzu ya fito fili karara, musamman ma ganin yadda yar sandan duniya wato kasar amuruka taki cewa uffan kan lamarin, da kuma halin ko oho da majalisar dinkin duniya ta nuna cewa suna da ra’ayi akan lamarin. Domin kuwa, hakkin majalisar dinkin duniya ne ta sasanta kasashen cikin lumana da diflomaciyya, amman taki yin hakan ta zurawa Israela ido tana cin karenta ba babbaka a Zirin Gaza. Akwai bukatan majalisar dinkin duniya ta sake salon yadda take tafiyar da lammuranta, ma’ana ta rikayin adalci da kuma cin gashin kanta basai tajira wata kasa ta bata umurni ba. Koda yake, kin daukan mataki da majalisar tayi a kan Israela wani umurni ne daga amuruka. Domin kuwa amuraka ce ke tafiyar da harkokin majalisar dinkin duniya, har ila yau hedkwatar majalisar na kasar amuruka, don haka shiyasa amuruka ke taka rawar da taga dama ta sanadiyar sake da nuna rashin iya aiki da majalisar tayi.
Yin biris kuwa da kasashen larabawa sukayi kan wannan lamari, suka ki taimakawa palasdinawa don tsoron kada amuruka tasa masu takunkumi ko ta kirasu yan ta’adda wallahi yazamo babban abin kunya da kuma hasara garesu. Domin kuwa Israela ba ita kadai ke aikata wannan kisan kiyashin da takeyi a zirin Gaza ba, tana samun taimako amma su larabawa sunkasa taimakawa yan uwansu. Tabbasa dole a jinjinawa kasashen masar da faransa kan namijin kokarin da sukeyi wajen ganin an kawo karshen wannan zibda jini da akeyi. Hakika kiran dakatar da ruwan bama bamai a zirin Gaza da kashen biyu sukayi, dakuma kiran a zauna a teburin shawara abin ayi maraba da shine kuma a yaba masu matuka gaya . Domin kuwa ta hakane kawai za’a iya warware rashin jituwa dake tsakanin israela da kungiyar Hamas na palasdinu. Abin fata a nan shine, Allah yasa wannan matakin da masar da faransa ke son cimma ya haifar da da mai ido, a kuma samu nasara . Lokaci yayi da kasashen musulmi zasu yi kiran a dakatar da ruwan baba bamai a gaza, da kuma nuna rashin jin dadinsu da kisan bayin Allah da Israela keyi a zirin Gaza, don su san cewa fa abinda suke aikatawa bai daceba, kuma baza a kyalesu su cigaba da wannan ta’addi ba.
Hakika al’ummar palasdinawa na wani hali na kunci, rashi da kuma tausayi duk sakamakon wannan bala’in ba Israela ta jefasu ciki, don haka muna tayaku addu’ar allah ya kareku da karewarsa, ya tsareku da tsarewarsa, ya kuma fidda ku daga cikin wannan halin kunci da kuka samu kanku a ciki.

Tuesday, January 6, 2009

ZABEN GHANA: DARASI GA NIJERIYA

Kasashe da dama a Nahiyar afrika da turai kan gudanar da zabe ta halatacciyar hanya, kuma zaben yakan amsu ga yan kasar, dama duniya baki daya. Akasindai yadda ya faru a Nijeriya. Zabe na baya bayan nan shine wacce kasar Ghana ta gudanar. Duk da cewa a zagayen farko na zaben anso a sami rudani, amman hakan baisa al’ummar kasar yin sake wajen kada kuri’unsu ba. Domin kuwa sun kada, kuma suka tsare, daga karshe suka raka kuri’un nasu harsai da aka tabbatarma wanda suka kada masa kuri’un nasu samun nasara da kuri’u sama da miliyan hudu.
Hakika samun nasaran da John Atta.na jam’iyar adawa yayi abin farin cikine, domin kuwa an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da lumana. Hatta masu sa ido na cikin gida dana kasashen ketare sunba da halaccin zaben. Abin sha’awa da zaben na kasar Ghana shine yadda aka tabbatarma da dan jam’iyar adawa samun nasaran zaben ba tare da anyi murdiya anba dan takarar jam’iyar dake mulkin kasarba, kamar dai yadda yanzu yake faruwa a wasu kasashen inda murdiyar zabe yazama ruwan dare.
Hakan ya nuna cewa dimokaradiya na aiki a kasar, kuma hukumar zaben itama naci gashin kanta batare da wani yayi mata katsalandan acikin ayyukanta ba.kuma babu azzaluman shugabanni masu cusawa al’umma mutanen da basa so. Tabbas wannan zabe na kasar Ghana ya zama kalu bale ga sauran kasashen nahiyar afrika, musamman ma nijeriya, inda magudin zabe ya zama abin ado, kuma ya mamaye kasar. Domin kuwa har yau an kasa gudanar da halatacce kuma karbabben zabe a kasar. Kullum sai jahiltan kanmu mukeyi muna kiran dimokaradiyar nijeriya wai jaririya. Mun kasa koya mata yadda ake tashi, zama, bale uwa uba tsayuwa da kafafun ta bibbiyu ba tare da wani ko wasu sun tsayar da itaba.
Yan nijeriya sun masu matuka gaya don ganin an fara gudanar da zaben gaskiya kuma tsarkakakke, kamar dai yadda ya gudana a kasar Amuruka , Ghana , da dai sauransu inda duk yan jam’iyar adawane suka lashe zaben. Koda yake, gwamnatin nijeriya tayi alkawarin yin gyaran fuska ga kundin tsarin zabe don samun damar gudanar da halatacen zabe nan gaba wanda dukkan yan kasa zasuyi maraba tare da na’am dashi. Amma ayar tambaya itace; wasu hanyoyi ne da matakai gwamnatin zata bi da kuma dauka don ganin cimma wannan buri nata? Kuma shin wadanda suka gudanar da zabubbukan baya sune zasu sake gudanar da masu zuwa? Hakika wadannan tambayoyi na bukatar amsoshi don wayar wa al’ummar kasar nan da kai don sanin ko da gaske gwamnatin keyi kan kawo sauyi ga yadda zabe ke gudana a kasar.