Sunday, March 22, 2009

FACTS ABOUT AFRICA!

The history of present day Africa states could be traced to colonial rule, courtesy of the Berlin conference of 1885, which divided African territories into areas of influence of European powers. The actual rule was brief or long, depending on the policy of the colonial powers. At the end of the colonial rule, independence was granted as a result of mutual settlement or prolonged war of independence.

At independence, African states establish their government based on liberal democratic principles with a flourishing multi-party system. Within four years, multi-party system collapsed, giving way to one party rule or military authoritarianism. This system of government continued to dominate the African political landscape until the end of the 1980’s.

From the Northern Horn to the southern cape: and from the Tropical Savannah of the west to Equatorial Region of the East, the entire continent was caught in a wave of democratization. Indeed, democracy became the only game in town. One of the essentials features of democratization process is election.

TARIHIN AFRIKA A TAKAICE

Tarihin kasahen Nahiyar Afrika ya samo usuli ne daga Taron Berlin da akayi a shekarar 1885 a wannan taron ne aka amince da yanyanke Afrika ga daulolin Nahiyar Turai. Irin mulkin mallaka ko mulaka'u da daulolin Nahiyar Turai din suka yi na wa'adi ne ya Allah mai tsawo ko takaitacce. A karshen mulkin mallakar, kasashen da aka mallaka sun sami 'yanci a sakamakon fahimta da yarjejeniya ko kuma bayan anyi gwagwarmayar yakin kwatan 'yanci.

kasashen Afrika da suka sami 'yanci kan tafiyar da harkokin mulkin dimokuradiyya mai tsarin mulki da jam'iyun siyasa kan yin aiki tare. A dan lokaci kadan (kamar shekaru hudu) tsarin siyasa mai jam'iyu da yawa kan ruguje ya haifar da jam'iya daya mai kama-karya ko kuma mulkin soja. Irin wannan yanayi ne ya yiwa harkokin siyasa kaka-gida a kasashen Afrika har zuwa karshen shekarun 1980.


Ilahirin Nahiyar Afrika ta tsunduma cikin hadahadar tsarin mulki irin na dimokuradiya wanda hakan ba ya samuwa sai ta hanyar zabe.

Wednesday, March 11, 2009

SAMMACIN AL-BASHIR: ADALCI KO ZALUMCI?

A ranar laraba ne 4/3/2009, kotun kasa da kasa da ke birnin Hague ta bayar da umurnin damko shugaban kasar Sudan, Omar Hassan Al-Bashir. Kotun na zargin shugaba Al-Bashir ne da laifukan kisan kare dangi a Dafur daga 2003. Tuni wannan sammacin ya haifar da cece-ku-ce a kasar Sudan da ma duniya baki daya inda mafiyawancin kasashe ke tir da wannan umurni na kotun duniya. To amma bai kamata ayi tuya a manta da albasa ba, domin kuwa ya kamata mu duba muga menene ummul aba isin haifar da wannan rikici na dafur? Kuma su waye keda hannu a rikicin? Tun bayan da arzikin mai ya samu a kasar Sudan, Amurka tayi kokarin ganin ta shiga kasar ta tafiyar da harkar mai amma hakanta bai cimma ruwa ba don kuwa basu samu yadda suke so, hakan kuwa shine silsilan rikicin Dafur kuma ita Amurka itace ta haifar da rikicin don ta kasa samun biyan bukatanta. Domin kuwa kafin bullar mai a kasar, Sudan na zaune cikin zaman lafiya ne ba tashin hankali a cikinta. Alal hakika kotun kasa da kasa dake Hague batayi adalci ba kan umurnin da ta bayar na damko shugaba Al-Bashir bisa zargin kisan kare dangi, kamar yadda mai gabatar da karar a kotun kasashen duniya Lius Moren-Ocampo yayi. Wannan hukunci kuma ka iya kawo cikas ga yunkurin tattaunawar sulhu da ake yi da nufin kawo karshen yakin da ake yi a yankin na Dafur mai arzikin mai.

Hakan ya nuna a fili cewa kotun bata aikinta yadda ya kamata, ko kuma ace akwai ‘yan lele da bata iya taba su. In harda gaskene kotun na gudanar da aiki tsakani da Allah ai ba Al-Bashir ya kamata su kwallafa idon su a kansa ba. Ga babban wanda ya aikata kisan biliyoyin al’umma a Afghanistan da Iraq, ko shakka babu tshohon shugaban kasar amurka Goerge W. Bush da tshohon prime minister Birtaniya Tony Blair sune kotun birnin Hague ya kamata taba da sammacin kama su. Har ila yau, kisan kare dangi da yahudun bani Israel sukayi wa palasdinawa shima abin dubawane, domin kuwa bani yahudun sunyi amfani da makamai masu kazamin guba, sunyi lugudan wuta iri-iri akan palasdinawa wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwar mutane bila a dadun, wasu kuma suka jikkata ga asarar dukiyoyi da akayi da dai sauransu. To wadanna ba laifine da yakamata kotun ta hukunta wadanda suka aiwatar dashi ba? Bush har ya yi yakinsa a kasar Iraq bai nuna wa duniya koda tsinke daga abinda yace yana zargin kasar dashi na makaman kare dangi ba. Sanadiyyar haka dumbin al’ummar kasar Iraq suka rasa rayukansu, dukiyoyi sun salwanta, ga lalata masu kasa da yayi Kuma kowa na kallonsa ba wanda yace masa uffan. Ashe wannan ba babban laifine da yakamata ace kotun ta dauki mataki mai karfi kan wanda ya aikatashi ba ganin cewa zargin da akeyi ma kasar kage ne kawai ba gaskiya a cikinta? ko kuwa shi yafi karfin doka ne? Tabbas baza mu taba ci gaba ba idan akace doka zata rika aiki kan wasu ‘yan tsirari ne kawai, sukuma ‘yan lele a barsu su rika cin karensu ba babbaka.

A fili yake kuma kowa ya sani saidai aki fadin gaskiya rikicin Sudan Amurka ne ta haddasa shi karkashin mulkin kama karya na Bush W.George, don haka Bush ya kamata ayi sammaci ba Al-Bashir ba. Lokaci yayi matuka da yakamata kasashen afrika su fahimci irin kallon da kasashen yamma keyi masu, don kuwa wannan umurni da kotun ta bayar kan Al-Bashir hannunka mai sanda ne ga sauran shugabannin, don haka su gagguta nuna rashin goyon bayansu kan wannan umurni na kotun mara tushe balle makama, domin ance idan gemun dan uwanka ya kama da wuta to shafa ma naka ruwa. Don haka, kotun kasa da kasa ta sake nazari kan wannan umurni da ta bayar na damko Al-Bashir, Bush da sauran ‘yan kan zaginsa ya kamata a damko kafin aje ga Al-Bashir (in har yayi laifin da za’a kamashi). Allah ya taimaki nahiyar afrika ya kuma kareta daga sharrin kasashen yammaci.
Allah ya yi mana jagoranci a dukkan ayyukan mu na alhairi, amin.

Sunday, March 8, 2009

Matasa Na da Mahimmanci ga ci gaban al'umma.

Matasa akace manyan gobe, kuma tushen cigaban kowace al’umma. Hakika wannan zancen haka yake, domin kuwa suna da babbar rawar dasuke takawa wajen tafiyar da harkokin yau da kullum. Saidai wani babbar matsala dake tare dasu shine rashin nuna halin ko inkula da gwamnati keyi masu. Rashin sanin muhimmancin matasan yasa haka ko kuwa rashin sanin su wanene matasa? To yadai kamata kowa yasan cewa matasa sune manyan gobe kamar yadda aka sani, kuma suna da babbar gudun muwa da zasu iya bayarwa wajen aikin raya kasa. Shin menene kalmar masata take nufi? Kan wanene hakkin matasa ya rataya? Menene kalmar manyan gobe take nufi, kamar dai yadda akance matasa manyan gobe? Wani irin kalu balene yake gaban su matasan? Menene zai iya faruwa kan irin rikon sakainar kashi da akeyiwa su matasan?
Ita dai kalmar matasa na nufin samari ne wadanda shekarunsu ya fara daga 18-25, kokuma daga 18-30 kamar yadda wadansu suke gani, yakuma ma danganta ne da yadda kowa yake ganin lokacin da yakamata a kira mutum a matashi, wato daga shekara 18 zuwa yadda yasamu. Idan kuma muka duba shin kowane ne hakkin matasa ya rataya akansa, zamu ga cewa hakkin nasu bawai ya rataya akan gwamnati bane kawai, harma da iyaye da sauran al’umma, koda yake ana iya cewa gwamnati ita keda babbar hakki. Abinda gwanmati ya kamata tayi wa matasa shine, samar da ilimi bai daya garesu, tsaro, kula da lafiyan su, sai uwa uba aikin yi domin kuwa wannan hakkine wanda ya rataya akanta. Sukuwa iyaye da sauran al’umma, hakkin sune suga cewa sunba matasa tarbiyya mai kyau, kuma sun basu horon daya dace dasu wajen tafiyar da ayyukansu na yau da kullum. Domin kuwa duk wata al’umma da take son cigaba, sai tabayar da cikakkiyar kulawa ga matasanta da basu kyakkyawar horon daya dace dasu don zama wakilansu na gari bana banza ba a duk inda suka shiga.
Allah sarki! Bahaushe yace wai matasa manyan gobe, kuma ko shakka babu wannan Magana haka take, kamar yadda nace a baya. Domin dai ita kalmar manyan gobe na nufin matasa ne zasu amshi tafiyar da ragamar mulki a duk lokacin da wadanda suke mulkin a yau suka tsufa ko wa adin barin aikin su yayi. Saidai labarin a kasar nan tamu Nijeriya tasha bamban. Domin kuwa, idan aka duba tun daga matakin kananan hukumomi har izuwa ta gwamnatin tarayya, za’a ga cewa duk wadan da shekarun su yafara daga 50-60 koma fiye da haka sune a madafun iko. Ba za’a ga matasa wadanda shekarunsu ya fara daga 35-40 ba, duk dacewa suna da babbar gudun muwar da zasu iya bayarwa wajen ci gaban kasar nan.
Matasa a yau sun zama kashin bayan ci gaban kowace al’umma, batare da la’akari da muhimmancin su a cikin al’umma ba, dakuma rawar da zasu taka ta fannin gina kasa. Hakika wannan yaka mata yazama kalu bale gasu matasan don ganin martabarsu ya karbu a ko ina, ta hanyar kaura cema duk wani aikin ash-sha, shaye-shaye da dai suransu, ganin cewa akwai bata gari acikinsu, kuma bahaushe yace wake daya shi ke bata gari. Saboda haka yaza ma wajibi ga matasa da su gyara kansu, sukuma san cewa dabi’ar banza bazata haifar masu da da mai ido ba. Har ila yau kada matasa su yadda su zama ‘yan bangan siyasa, abin nufi anan shine, kada wasu ‘yan tsirarun mutane su rika amfani dasu wajen tada zaune tsaye don kawai cimma burinsu, wanda bayan su wadannan mutane sun samu abin da sukeso basa yiwa su matasan komai illa su watsar dasu. Matasa susan cewa fa su wakilai ne na samar da zaman lafiya ba hargitsi ba a cikin al’umma. Komai na iya faruwa a duk lokacin da aka tauye ma matasa hakkinsu ko akaci gaba da nuna halin ko inkula dangane da rayuwarsu, musamman ma idan babu cikakken tsaro, ilimi, da uwa uba aikinyi da kuma sauran abubuwan more rayuwa wanda yazama hakkine na hukuma ta samara dasu. Rashin wadan nan abubuwa zai iya jefa matasa a tsaka mai wuya, kamar dai sace-sace, yawon banza da sauran aikin ashsha da baza’a rasaba, wanda kuma bama fatan hakan ya faru ga su manyan goben.
Daga karshe, ya kamata gwamnati da sauran hukumomin da abun yashafa da su san cewa fa matasa ba abin wasa bane a kowace irin al’umma. Musamman ma ganin cewa sune manyan gobe kamr yadda nayi bayani a baya, kuma suna da gudun muwa na cigaba da zasu iya bayarwa. Don haka yana da kyau a rika duba duk wata irin matsaloli dake damunsu, da kuma yin kokarin samar masu da maganinsa. Kana duk wata al’umama ko gwamnati data ga ayyukanta na samun cikas ko rashin ci gaba, to ta waiwaya ta dubi matasanta taga yadda al’amuransu yake tafiya.
Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukanmu na alhairi amin.

Tuesday, March 3, 2009

SHIN MATASALAR RUWA ZAI ZAMA TARIHI A ZARIA?

Budaddiyar Wasika Ga Gwamna Namadi Sambo.
Duk dan adam yana da bukatan abubuwan more rayuwa na yau da kullum kamar su wutan lantarki, hanyoyin sufuri masu nagarta,da dai sauransu.amman saidai a yau akasin hakan ake samu. Koda yake, wasu ma ana iya cewa sun zama dole yin amfani dasu. Misali, koda yake ruwa ba’a ce dashi abin more rayuwa ba, amman dukkan mai numfashi na bukatansa a kulli yaumin domin sha, girki da kuma sauran ayyukan yau da kullum

Kash! Saidai labarin a birnin zariya ba haka yake ba. Domin kuwa ruwa ya zama dan gwal. Saboda a yau duk wanda yazo garin zariya daga wata garin, to babu abinda da zasu fara yi masa maraba face ‘yan garuwa. Wadanda suke sayar da ruwan nasu da dan karan tsada, kuma gashi wasu daga cikinsu ruwan nasu bawai yana da kyau bane. Wanda idan hakan ta daure, to nan gaba ba’a san abinda zai haifarba.

Koda yake wannan matsala na rashin ruwa a birnin zariya bawai sabon lamari ne ba, saidai kawai yadda rashin nasa yake dada tabarbarewa. Na tabbata duk yaron da ke zariya a yau, wanda shekarunsa basu wuce sha takwas zuwa ashirin ba, wallahi bai taba ganin ankawo ruwan famfo a gidansu ba. Wannan matsala kuwa ta wuce duk iya tunanin mutane, domin kuwa kamar yadda nace ne tun farko, al’amarin yana neman wuce gona da iri. Abin ban takaici ne yadda a yau yara kanana cikin dare suke fita ko kuma da subahin fari da sunan suna zuwa neman ruwan da iyayensu zasu yi masu abinci. Wanda hakan kan iya sa yaran shiga wani halin da bai dace ba.

A kwai bukatan hukumomi ko gwamnati data shiga cikin wannan lamari don kawo saukinsa ga al’ummar da suke yiwa shugabanci. Koda yake, mai girma gwamnan kaduna Alhaji Namadi Sambo, ya samar da famfuna masu aiki da hasken rana wadanda zasu iya aiki daga safe har zuwa la’asar ko ace yamma. Saidai labarin ba haka yake ba, domin kuwa famfunan sun zama abin adone kawai a birnin na zariya. Saboda idan famfon yabada ruwa na kamar sa’a uku a rana, to sai yayi kamar mako daya koma fiye da haka bai sake bada ruwa ba duk da cewa da hasken rana yake aiki bada wutan lantarki ba. Wani abin ban haushi ma shine yadda manya da kanan yara ke dambe a wajen diban ruwan, wanda hakan kan haifair da jin raunuka da dama gasu yaran. Koda yake yin damben nasu nada dalili, domin wani bokitinsa takan kwana biyu ko uku a layi, amman lokaci daya wanda yafisu son zuciya sai yazo yace sai ya diba kafin su, wani lokaci kuma sukan tashi a tutan ma’aho. kai yanzuma kalilan daga cikin wadannan famfuna ke aiki. koda yake ana iya cewa nesa tazo kusa, domin kuwa mai girma Gwamna Namadi Sambo yabada kwangilar gyara ruwan Zariya don al'umma su samu saukin wannan hali na mawuyacin ruwa da suke ciki. to amman abin tambay shine: shin wadanda alhakin ya rataya akansu zasuyi aiki tsakani da Allah don kawo karshen wannan hali ganin cewa kusan shekaru goma kenen ake shelar cewa matsalar ruwa a Zariya zata zama tarihi amma har yau shiru akeji kamar Mallam yaci shirwa?

Don haka ya kamata gwamnatin jihar kaduna data karamar hukumar zariya suyi hubbasa wajen magance wannan fitina data addabi jama’ar nasu, ganin cewa ma yana daya daga cikin alkawuran da suka daukan masu yayin yakin neman zabe. Saboda wanna ruwa da ‘yan garuwa ke sayarwa, mafi yawancinsu bamasu kyau bane, kuma shan irin wadannan ruwan na iya haifar da barkewar wata cuta. (Amma bawai ina kashema yan garuwa kasuwa ne ba, a'a gaskiyar lamari ne, kuma nayi bayanin cewa bawai dukkansu ne keda ruwa mara kyau ba.)

Ya kamata mai girma gwamna alhaji namadi sambo, ya sake duba wadan nan famfuna da aka kafa masu aiki da hasken rana don su rika aiki yadda ya kamata, don kada yazamana anyisu amman babu amfani ganin cewa kudin al’umma aka dauka akayi aikin dashi, don haka yakamata suga amfanin yin aikin da dukiyarsu. Har ila yau, mai girma Gwamna yasa ido akan kwangilar aikin ruwan don kada marasa son ci gaban Zariya suyi kafan ungulu a aikin.
.Allah shiyi mana jagora a dukkan ayyukanmu na alhairi amin.