Sunday, June 6, 2010

12th ANNIVERSARY OF GEN. ABACHA'S DEMISE!



June 8,2010, will be exactly 12years that Almighty Allah deemed it fit to take back the life of Gen. Sani Abacha.

The death of General Abacha is a great lost not only to his family, but to the entire nation-because he was a great patriot and a brave general who dedicated himself to the service of his country. Abacha had a vision, he meant well for Nigeria, and we never had a peaceful president like him. History will always remember general Abacha as a hero who did his best for his country. We pray to Almighty Allah to continue to give the family, friends and well wishers the fortitude to bear the irreplaceable lost.

We also pray that your gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.

Abacha we are still with you in spirit and we love you, but God loves you more.

Kwanci tashi babu wuya inji malam bahaushe, A ranar 8 ga watan yuni na wannan shekaran ne tsohon shugaban mulkin sojan kasarnan marigayi janar sani abacha ke cika shekara goma sha biyu da rasuwa

Alal hakika rasuwar janar abacha ya girgiza dukkan alahirin yan nijeriya, musamman ma ganin yadda a wancan lokacin yayi yun kurin farfado da tattalin arzikin kasan nan, da kuma biyan basukan da kasashen ketare ke bin mu, amman hakan batayiwu ba sai mai kowa mai komai ya dauki abinsa.

Duk dan nijeriya mai bibiyar yadda al’amurra suka rika kaiwa da komowa a wannan kasa
lokacin mulkin marigayi janar abacha, yasan cewa shine shugaban da al’ummar nijeriya baza su taba mantawa da shiba. Domin kuwa a lokacin mulkin sane yayi shelar cewa duk kasashen ketare da ke bin kasarnan bashi za’a biyasu kuda densu ba tare da bata wani lokaci ba, amman saboda butulci, yaudara,mugunta da keta irin na nasara sai sukayi kememe suka ki amsar kudaden nasu wai saboda wa’adin da aka ba nijeriya na data biya wadannan basukan basu cika ba. Gashi a yau kuwa basukan sai kara karuwa sukeyi kuma da dukkan alamun babu ranar biyansu..

Har ila yau, janar abacha ya kasance shugaban nijeriya na farko da yaki bada kai bori ya hau ga kasashen yammacin turai da sauransu, musamman ma ganin yadda yafi mai da hankali ga kasashen afrika wajen gudanar da harkokin mulkinsa. Hakan kuwa yasa kasashe da dama suka rika sanya ma nijeria takunkumi, wai suna masu cewa tarayyar nijeriya nada shugaba mai mulkin kama karya. Wannan furuci nasu kuwa ba komai ya kawo shiba illa kin yarda da janar abacha yayi nadasu shigo kasar nan su rika cin karensu babu babbaka-kamar dai yadda labarin yake a yanzu, domin kuwa yanzu kowa yasan cewa kasashen yamma na taka rawa sosai kan yadda ake gudanar da mulki ko harkokin kasar nan. Wanda a wancan lokaci janar abacha yaki yarda da hakan.
Saboda rashin fahimtar salon mulkin janar abacha, wasu yan nijeriya da dama suka bi sahun kasashen ketare wajen yin tir da gwamnatin nasa suna masu cewa wai kasarnan tana fama da talauci,yunwa ,rashin aikin yi, rashin tsaro da dai sauran korafe korafe da dama.

Da madai ance dan adan ba’a iya masa face ubangijin daya halicceshi, duk kokarin da marigayi janar abacha yayi a lokacin mulkinsa na ganin yan nijeriya sunji dadin wannan gwamnatin, duk jama’a basu ganiba sai tsinema mulkinsa aka rika yi ana Allah wadai da ita. Kodayake gaskiya tananan a gaskiyarta, domin kuwa a yanzu al’ummar kasannan sun fahimci irin hangen nesan da janar abacha ya rika yi da kuma irin gyara kasannan dayaso yayi. Domin kuwa yanzu sun dawo suna kewarsa.

Ba komai yasa suka gane hakan ba illa irin halin da suka tsinci kansu daga farkon shekarar 1999, wanda hakan yasa yan nijeriya yanzu sun gane cewa tabbas janar abacha gwarzon shugabane kuma mai kishin kasar san e da nahiyar afrika. Duk da irin tonon sililin da tsohuwar gwamnatin kasarnan karkashin mulkin Obasanjo ta rika yiwa iyalan janar abacha baisa yan nijeriya yin nadama da kewar da sukeyi na shi abachan ba, illa karamasu karfin gwuiwa. Domin kuwa kowa yasan kahon zukar da gwamnatin tasa ga iyalan janar abacha siyasa ne kawai, domin so suke su bata masa suna a idon duniya…dayake Allah ba azzalumin kowa bane sai gashi yau itama waccan gwamnatin data rika kwance wa iyalan janar abacha zani a kasuwa goguwar ya koma kanta, kuma dukkan abinda da akace ana zargin gwamnatin data shude haka yake babu ko tantama. Koda yake nasan yan nijeriya sunsan abinda nake nufi, kuma sune suka fi dacewa dasu fadi hakan don sunsan irin halin da suka tsinci kansu cikin shekaru takwas da suka gabata ko shekaru goma.

Daga karshe, babu abinda zamuce illa allah ya gafartama janar abacha, ya kyautata kwanciya, yaba iyalansa da abokan arziki kara jure wanna babbar rashi, yasa aljanna firdaus makoma, mu kuma idan tamu tazo yasa mu cika da imani. Sukuma shugaban ninmu Allah yasa suyi kishi irin na marigayi janar abacha, kuma yabasu ikon sauke nauyin dake kansu.