Friday, February 27, 2009

GASKIYA DOKIN KARFE.

Dangane da bayanin dana yi a jaridar aminiya mai taken KAN BATUN RIBADU A TSAKA MAI WUYA, amman jaridar aminiya ta bashi taken dayafi dacewa dashi na HARYANZU INA GOYAN BAYAN RIBADU.kuma aka bugashi a jaridar ranar 20/2/09. a cikin kasidar dai na dada bayyana dalilan da sukasa nayi wancan rubutun mai taken RIBADU A TSAKA MAI WUYA wanda aka buga ranar 19/12/08, kuma shine silar yin wannan kasida na HARYANZU INAGOYAN BAYAN RIBADU sadoda irin korafe korafen da na rika samu daga wadanda sukakaranta waccar kasidar ta farko na ranar 19/12/09.
kamar yadda nasha fadi, gaskiya dai dayace, kuma daga kinta sai bata. gaskiya akace kuma dokin karfe ne. Nayi imani cewa ko bijima ko ba dade, gaskiya zatayi halinta domin Allah ba azzalumin kowa bane.
Nayi farin ciki matuga kan sakwannin waya dana samu wajen wadanda suka karanta wannar kasida na HARYANZU INA GOYON BAYAN RIBADU dakuma wadanda suka bugo waya don bayyana ra'ayinsu kan batun. Allal hakika sakwannin dana samu sun nuna cewa yan Nijeriya da dama sunyi tir da wannan halin tsangwama da akema mallam Nuhu Ribadu duk dacew ya bautawa kasar nan iya bakin kokarinsa. kodayake, ansami wasu kalilan da basu amince da yadda shi Ribadu yayi ayyukansa ba, dama ance ai daidan wani karkataccen wani. Komadai yane, ina matukar godiya ga dukkan wadanda suka dauki lokaci suka aiko da ra'ayinsu.
godiya ta musamman ga wadanda suka aiko da sakwannin waya kamar su Malam Ibrahim dan zariya mazaunin Lagos, Labaran Waziri Darazo, Abubakar Muh.A.K Zabi Auyakari giyade Bauchi mazaunin Jos, Auwal, Bashir Dikko Funtua, Sani Bandy B/Gwari, da sauransu.
har ila yau, ba zan manta da dukkan wadanda suka bugo waya ba kamar su Malam Abubakar Sani daga Kaduna, Wada Isa daga Kano, Idris Suleiman Plateau mazaunin Legos, Mahmud daga Kano, Kawu saleh daga Jos, Abubakar Moh'd daga Kebbi,
zanyi amfani da wanna dama in mika ban hakuri ga wadanda suka aiko da sako ko bugo waya amman basuga sunansu ba, suyi hakuri abin ne da yawa wai mutuwa ta shiga kasuwa. Wasu na manta sunansu da lambarsu, wasu kuma na kasa daukar sakon waya da suka aiko dashi har kuma sakon ya bace. Don Allah ayi hakuri saboda ayyukan sunada yawa.
Allah yayi mana jagora a dukkan ayyukanmu. wassalam.

No comments: