Tuesday, February 17, 2009

ZIYARAR SHUGAN KASAR SIN

ZIYARAR SHUGABA HU JIN TAO
La shakka ziyarar da shugaban kasar Sin Mista Hu Jin Tao yakai a wasu kasashe na nahiyar afrika don habbaka dangantakar kasuwanci tsakaninsu abin ayi maraba da shine matuka gaya. Alal hakika wanna ziyara tasa za taba kasashen dama bude sabon babi tsakani su da kasar ta Sin, musamman ma ganin cewa kasashen na Mali, Senegal, Tanzania da kuma Tsibirin Moroshiyos kasashene masu tasowa kuma wadanda basu da karfin tattalin arziki.
Wannan Mataki da shugaba Hu ya dauka duk da cigaba da tabarbarewar tattalin arzikin kasashen duniya, don dada habbaka huldar dangantaka tsakanisu wanda dama tuni suke huldar kasuwanci tare, ya samu karbuwa ga dukkan yan kasashen dama nahiyar afrika baki daya. Tabbas Mista Hu yayi kwakkwarar tunani na zaban wadannan kasashen don ganin sunyi huldar kasuwanci tare, duk kuwa da cewa kasar Sin kasa ce da taci gaba nesa ba kusa ba da wadannan kasahen.
Hakan kuwa zai kawo ci gaba ba karami ba ga akasashen in har duldar tasu tayi karko, dafatan sauran kasashe masu cigaban masana’antu da tattalin arziki zasu dada karfafa huldar cinikayyarsu da sauran kasashen afika don suma su samu su daga.

No comments: