Tuesday, May 29, 2007

kan batun yan nijeriya mu rungumi kaddara


Dangane da sharhohin da na rika yi a harkan siyasar dake gudana a kasannan, na rika samun sakonnin text ta waya na dangane da sharhohin, wanda kuma wannan jaridar ta aminiya mai farin jini ta rika buga sharhohin nawa. Jama’a da dama sun bayya na ra’ayoyin su dangane da rubutun nawa daban daban wadanda aka rigaya aka buga.
Saidai kuma ra’ayoyin nasu yasha banban, inda mafi yawancin su suke adawa da sharhohin nawa musamman ma mai taken ‘YAN NIJERIYA MU RUNGUMI KADDARA’. Ala hakika mutane da dama sunyi suka akan wannan ra’ayi nawa inda wadansu ke danganani dad an amshin shata, wasu ma sunce wai hala an bani kudine bayan an buga wata sharhi da nayi mai taken ‘RASHIN HADIN KAN YAN ADAWA YA JAWO ARINGIZON KURI’U’ shi yasa nazo nayi na ‘yan nijeriya mu rungumi kaddara, da dai sauran korafe korafe da dama. Hakika kowa yana da yancin fadin ra’ayinsa, amma ina son jama’a suyi mun kyakkyawar fahimta, kuma inason mutane da sauran masu karatu musamman masu karanta wannan jarida ta aminiya, dasu sani fa, ni dai sharhi kawai nayi dangane da al’amurran siyasar kasan nan. Kuma bana yi hakanne don in tozarta wani ko wata ba, amma idan hakan tasa na bata ma wani ko wata rai, to don allah ayi hakuri domin kuwa ba manufuta bakenan in kuntatawa jama’a.
Dangane da cewa ni dan amshin shatane, ko kuma an bani kudine yasa nake haka duk bata tasoba. domin kuwa ina tsammanin ban ambaci sunan kowace jam’iyya ba don agoyi bayan ta. Cewa kawai nayi da a rungumi kaddara, a hada karfi da karfe kana a goya wa sabbin shugabannin baya don samun sukunin sauke nayin da yahau kansu. Tabbas kowa yasan cewa zabubbukan dasu ka gabata sun sami kura kurai da dama, amma abin da yafi dacewa garemu shine amanta duk koma mene yafaru don a tabbatar da jaririyar dimokradiyya dake niman zama da gindin ta. Na kuam fadi hakane don ganin cewa, komai dai mukaddari ne daga allah, bamu da wani zabi wanda yawu ce nashi. Kana kuma duk cikakkem mai imani kamata yayi da yasan cewa alkur’ani mai girma yana manu nuni da cewa allah ke bada mukin ga wanda yaso a duk lokacin da yaso yin hakan, kuma ya amsheta a kowani lokaci idan yaso yin hakan.
Daga karshe, ina yi ma masu karatu da sauran jama’a fatan alheri a dukkan ayyukan sun a alheri, musamman ma wadan da suka aikomun da sakon text na bayyana ra’ayoyin su. Allah ya albarkace mu baki daya, yasa muga 29 ga want mayu lami lafiya. Dafatan an fahimce ni da kyau. Wassalam

No comments: