Sunday, August 24, 2008

YINWA SOJOJI GARANBAWUL YA JAWO JUYIN MULKI A MAURITANIYA

Mauritaniya kasa ce wadda za’a iya cewa ta koma ta firkin dimokradiiya ne a shekaru biyu da suka wuce bayan halataccen zaben da aka yima Abdullahi Sidi ould cheikh. Kuma yaci gaba da jan ragamar mulkin kasan har farkon watan agusta na wannan shekara sa’ad da sojoji suka kifar da gwamnatin nasa.
Koda yake, sojojin sunbada dalilansu na kifar da gwamnatin na Abdullahi inda suka ce hambararren shugaban yana neman jefa kasar cikin wata mummunar rikicin siyasa da kuma rashin mutunta hafsoshin sojan kasar, ga kuma rashin iya gudanar da aiki yadda ya kamata. Dama dai, tuni su manyan dakarun kasar suka rika yi masa hannunka mai sanda kan yadda yake tafiyar da harkokin kasar da kuma yadda rikicin siyasa ya fara maimaye kasar, amman yayi kunnin uwar shegu dasu.
Takai a karshe ma inda shi hambararren shugaban yace yayi ma dukkan manyan hafsoshin tsaron kasar ritaya daga aiki batare da yaba da kwakkwaran dalilin yin hakan ba. Turkashi! Duk wanda yasan irin hubbasa da hafsoshi keyi dakuma irin gudunmuwar da suke bayar wa wajen kare al’umma da samar da tsaro a kasa ba zaiyi irin wannan makauniyar aiki da shugaba Abdullahi yayi ba.
Wannan mataki da shi Abdullahi ya dauka wanda kowa yasan cewa yayi babban kuskure, shine babban abinda ya tunzura sojoji yin juyin mulki a mauritaniya, inda sukace shugaba Abdullahi yanason kawo rudani a cikin harkan tsaron kasar. Wannan dai hali da hambararren shugaban ya sami kansa a ciki ana iya cewa shi ya tura kansa, domin kuwa gurguwar matakin daya dauka bata haifar masa da da mai ido ba.
Saidai kuma, sojojin dake jan ragamar mulkin kasar sunyi alwashin gudanar da zabe nan bada daewa ba ganin yadda majalisar dinkin duniya, kungiyar tarayyar afrika, da amurka (yar sandan duniya) da sauran kasashen duniya keta tir da wannan juyin mulkin daya gudana a mauritaniya.
Abinda za’ayi fata kawai shine, su sojojin dake jan ragamar kasar a halin yanzu su gudanar da zabe na adalci batare dayin magudi ba. Duk wanda ya sami nasara a bashi, kada suyi son zuciya su daura wanda suke ra’ayi akan mulki. Dafatan zasu gaggauta sako hambararren shugaban kamar yadda suka saki firamistan kasar.

1 comment:

Anonymous said...

The information here is great. I will invite my friends here.

Thanks