Thursday, September 29, 2011

Jawabin Shugaban Kungiyar Gizago A Taronta Karo Na Uku Da Akayi A Katsina


JAWABIN SHUGABAN KUNGIYAR GIZAGO NA KASA A TARONTA KARO NA UKU DA AKA SHIRYA A JAHAR KATSINA RANAR 25/9/2011, A DAKIN TARO NA KATSINA MOTEL.

Da sunan Allah mai rahma mai jin kai. Ya ‘yan uwana gizagawa, tare da sauran manyan baki, ina cike da farin ciki tare da yimaku barka da zuwa wajen taron kungiyarmu mai albarka ta GIZAGO a Jihar Katsina ‘dakin kara’.
• Kamar yadda mafi yawancin mu suka sani, an kafa kungiyar Gizago a Jaridar Aminiya cikin watan Aprilu, 2008 don sada zumumnci, amma daga baya ‘ya’yan kungiyar suka fadada ayyukanta zuwa habaka harshen hausa da inganta al’adun gargajiya da kuma bada taimako ga ‘ya’yan kungiyar da sauran al’umma. Kuma hedkwatar wannan kungiya na kasa yana Jihar Katsina ne. A takaice manufofin wannan kungiya sune:
1. Habaka harshen hausa. 2. Inganta al’adun gargajiya. 3. Sada zumunci 4. Bada tallafi ga ‘ya’yan kungiya da sauran al’umma.
• Anyi taron farko na wannan kungiya a Jihar Kano a shekarar 2009 inda uban kungiya kuma babban bako a wannan rana Dr. Bala Muhammad ya gabatar da lacca akan muhimmancin raya al’adun Hausa, kuma wannan ne karo na farko da ‘ya’yan kungiyar suka san junansu ido-da-ido domin kuwa da a Jaridane kawai ake sada zumunci da yin wasu al’amurra da suka shafi kungiyar.
• Taro na biyu anyishi ne a Kaduna Birnin Gwamna a shekarar 2010, kuma taron ya maida hankali ne kan bunkasar harshen hausa a duniya inda Farfesa Dalhatu Muhammad na Jami’ar Ahmadu Bello dake Zariya ya gabatar da laccar. A wannan karon kuma, wato taron kungiyar na uku wanda akeyi yau a Birnin Katsina Fadar Gwamnatin Jihar Katsina, za’a tattaunane a kan irin gudunmuwar da matasa zasu bada wajen habaka harshen hausa da inganta al’adun Hausawa, kuma Farfesa Ibrahim Malumfashi Shugaban Sashen harshen Hausa na Jami’ar Jihar Kaduna zai gabatar da laccar.
• A bangaren habaka harshen hausa da kungiyar keyi, as samu ci gaba sosai domin kuwa an samu daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar mai suna Malam M.S. Suleiman zaria ya wallafa littafi mai suna BAZAZZAGIYA wanda aka kaddamar a taron kungiyar karo na biyu da akayi a Kaduna. Kuma littafin yayi bayani kan wasu Sarakunan Arewa, da kuma dangantakar barkwanci tsakanin zagezagi da kanawa. Haka kuma, dan kungiyar mai suna Ado Ahmad Gidan Dabino, wanda sananne ne a duniyar marubuta, shima ya wallafa littafai da dama cikin harshen Hausa.
• Wajen bada tallafi kuwa, kungiyar nan ta bada tallafin kudi da kayayyaki na dubban nairori ga wadanda rikicin Jos ya afka masu a farkon shekaran 2010. Har ila yau, kungiyar nan a karkashin rassanta na wasu Jihohi ta bada tallafi ga gidajen marayu, nakasassu, gidan yari, makarantu da dai sauransu. Amma munaso a fahimcemu cewa, bawai muna fadin wadannan ayyuka bane don mutane su yaba mana, a’a muna fadine don jama’a su san cewa wannan kungiya ta Gizago ba Kaman sauran kungiyoyi bane, domin kuwa a kullum tana aiwatar da manufofinta, kuma tana fadin ayyukanta ne don sauran ‘ya’yan kungiyar su zage dantse wajen bada gudunmuwa don ganin ankai ga tudun muntsira.
• Kungiyar Gizago ta fara ne da mambobin da basu kai guda 20 ba, amma a yau, kungiyar na da mambobi 2022, kuma kungiyar na da rassa a sama da Jahohin Nijeriya ashirin da kuma wasu daga cikin kasashen ketare, domin kuwa a yanzu haka dinnan muna da mambobinmu na rassan Jamhoriyar Nijar acikin dakin taron nan tare da mu wadanda sukayi takakkiya tunda ga kasarsu don halartan wannan taro mai dimbin mahimmanci.
NASARORI.
• Dan gane da nasarorin da kungiyar Gizago ta samu kuwa sune, an samu damar rubutawa da kamala kundin tsarin mulkinta kuma an kaddamar da wannan kundi ga ‘ya’yan kungiyar A Kano a shekarar 2010. Har ila yau, bayan kwashe shekaru ana ta fadi ta shin yin rijista da hukumar dakema kungiyoyi da kamfanoni rijista, a yanzu an samu damar kammala wannan rijistar da hukumar C.A.C. hakika wannan ba karamin nasara bane domin kungiya yanzu bata da wani fargaban gudanar da taro ko ayyuka a ko ina cikin kasar nan harma da ketare domin ta cika dukkan sharuddan da gwamnati ta gindaya kafin ayi mata rijista. Har ila yau, kungiya ta bude shafi a duniyar gizo inda ake musayan ra’ayoyi tsakanin mambobinta da sauran al’umma a ko ina cikin duniya.
• Wannan kungiya a kullum sai kara karbuwa takeyi a ko ina tare da samun yabo kan irin ayyukan da take gudanarwa. Domin kuwa, hatta kungiyar muryar talaka mai fafutukan ganin anyi mulkin adalci ta yaba da aikinmu inda ta bamu takardan shaidan yabo a taronta na farko da tayi a shekarar da ta gabata.


• Amma fa inason kusan cewa dukkan irin nasarorin da wannan kungiya take samu ya biyo bayan irin gagarumin gudunmuwar da Madugu uban tafiya, limamin sada Zumunci, Direban Jirgin Gizagawa Malam Bashir Yahuza Malumfashi keyi wajen aiki tukuru don ganin kungiya ta samu nasarar gudanar da ayyukanta- tare kuma da irin damar da kamfanin Jaridar Aminiya ke bamu wajen ci gaba da yada manufofinmu. Hakika sun cancanci a yaba masu, don haka muna rokon Allah madaukakin sarki ya albarkaci kamfanin MEDIA TRUST.
• Haka suma iyayen wannan kungiya, Dr Bala Muhammad, Mahmoon Baba-Ahmad, Ado Saleh Kankia, Dr Yusuf Adamu da Alhaji Bello lawal, da sauran iyayen kungiya a matakan Jihohi ya zama dole a yaba musu kan irin gudunmuwa da kuma lokacin da suke bawa wannan kungiya a ko wane lokaci. Wannan kungiya na alfahari daku a kowane lokaci, dafatan zaku ci gaba da bada goyon bayanku kan ayyukanta da kuma shawarwari don ganin ankai ga tudun muntsira. Suma shugabaninnin wannan kungiya wadanda lokaci ba zai bada daman a bayyana sunayensu ba, sun cancanci a yaba masu matuka kan irin namijin kokari da sukeyi wajen hada kan mambobin kungiyar tare da yin ayyukan dake kawo ma kungiya ci gaba. Haka suma ‘ya’yan kungiyar ya zama dole a yaba masu kan irin hadin kan da suke bayarwa don ci gaban kungiya, da fatan zasuci gaba da bada hadin kai a ko wane lokaci.
• Kafin in kammala wannan jawabi, zanso in sanar da dukkan wanda ke dakin taron nan cewa a shekaru 3 nan da muka kwashe, dukkan ayyukan da kungiyar nan keyi da kuma gudanar da taronta na shekara shekara, da kuma bada tallafi da takeyi da dai sauran ayyuka, dukkan kudaden yana fitowane daga aljihunta. Ma’ana, daga ‘ya’yan kuniyar. Sune sukan sanyama kansu haraji su tara kudaden da ake bukata. Don haka, a yau, kungiya zata gabatar da neman gudunmuwa don samar da Ofishinta na dundundun a Jihar Katsina, tare kuma dayin sauran ayyukan da ta saba.


HARSHEN HAUSA.
• Har ila yau, zanso in sanar daku cewa, don ganin harshen hausa ya bunkasa a ko ina, kungiyar Gizago a shekara mai zuwa zata maida hankali ne wajen fadakar da daliban makarantun sakandire da jami’o’i musamman hausawa dasu rungumi wannan harshe nasu na iyaye da kakanni, tare kuma da taimaka masu da litattafan karatun hausa gami da shirya taron bita gasu daliban kan yadda ya dace su rika karatu da rubutun hausa, musamman ganin cewa matasa hausawa yanzu basason karanta littatafan hausa da kuma yin rubutun hausa. Don haka zamuyi maraba da duk wata irin gudumuwa da zamu samu daga gareku don cimma wannan manufa da muka sanya a gaba. Wannan kungkiya tana adduar Allah ya jikan marubutan Hausa irin su Marigayi Abubakar Imam, da dai sauransu domin kuwa sun bada gagarumin gudunmuwa wajen bunkasar harshen Hausa. Haka kuma, Kungiyar Gizago na sake jinjina da yabawa ga Alhaji Bashir Usman Tofa, Dr Bukar Usman, Mallam Bashir Yahuza Malumfashi, Ado Ahmad Gidan Dabino, Mallam M.S Sulaiman Zaria, da suran Marubuta kan irin gudunmuwar da suke bayarwa a halin yanzu wajen bunkasa Adabin Hausa. Muna rokon Allah madaukakin Sarki da ya kara masu basira da hikima kan wannan aiki da sukeyi.
• Daga karshe, muna addu’ar Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, haka kuma muna addu’ar Allah yasa ayi taro lafiya a gama lafiya, kuma bakinmu na nesa da kusa kowa ya koma gida lafiya.

Wassalam
Naku har kullum
Mallam Muntaka Abdul-Hadi Dabo
(Sardaunan A Bari Ya Huce)
National chairman,
Gizago

Tuesday, May 3, 2011

EPITAPH TO YAR'ADUA AND THE PRESENT STATE OF THE NATION


Day in, day out, every soul will surely taste the bitterness of death. Whosoever has come to the end of his life, a second will not be added to him. May 5th, will remain unforgettable to many Nigerians because of the shocked news they received. It was on that day that the then president and commander in chief of the armed forces Mallam Umaru Musa Yar’adua answered the call of Almighty Allah, after a protracted illness. As we all know, Yar’adua was (s)elected as president in 2007 through an election that was full of malpractices. Though, Yar’adua himself admitted that the (s)election that brought him to power was characterized by an unprecedented election malpractices in the history of Nigeria, and that necessitated him to constitute a committee under the chairmanship of the former chief Jutice of the federation justice Muhammad Lawal Uwais to look into the matter and come up with a lasting panacea to the problem. And he (Yar’adua) also promised to conduct a free and fair election in 2011(i.e. the just concluded election last month) that will be accepted by all Nigerians and the world in general, but he did not live long to actualize his dreams.

When he came to power in 2007, late Yar’adua showed a good sense of respect to all the arms of government by allowing them to discharge their responsibilities without disrupting them. The judicial arm, which is the last hope for the poor man enjoyed full autonomy in his tenure. This was corroborated by the fact that he (Yar’adua) remained dumb when the election tribunals nullified the (s)election of his party candidates (PDP) at various level of government on the ground of electoral malpractices. The former C-in-C, without any iota of doubt showed a sense of maturity in that respect which was never obtained in Obasanjo’s era and this present administration.

While he lived, Yar’adua was cool headed unassuming person who gave everybody his due respect. A man who stood for justice, fair play and equity. Surely, he will be remembered for his quiet dignity, sincere believe in rule of law, commitment to Deeping democracy and landmark resolution of Niger Delta crisis, etc. no doubt, Katsina state and Nigeria has lost an honest leader who meant well for his people. He is no longer with us, but Nigerians would surely be guided by his spirit of exemplified humility, and they will never relent in praying for the repose of his soul.

During his tenure, there was peace in the country and we never had a bomb blast in the three years he spent steering the mantle of leadership in Nigeria as its number one citizen. Unlike what is happening now, bomb blast in all angles of the country, killing of innocent people by police on high roads, etc. it’s very shameful that even the first bomb blast took place at eagle square on October 1st, last year when Nigeria was celebrating her 50th anniversary as a sovereign nation- followed by the one on Xmas Eve, another one on election Eve and during election in some part of the country, to mention but few, where several people lost their lives and many were injured. Imagine what we used to hear before in Afghanistan , Baghadaza, and Somalia , we are now hearing and witnessing it in our own dear country. This is certainly a big problem and if care is not taken, Nigeria will in no distant time (though we are not praying for it) become another Baghadaza, especially Borno State where the case is more rampant.

I can boldly now say, without fear of contradiction that insecurity has become a daily business in Nigeria and Nigerians are used to it. But it’s very annoying that the present administration has been doing nothing to find a lasting solution to the problem. Is this how we are going to continue? If things should continue the way they are now, what will Nigeria become in the next few years? Only time can tell, and it’s quite unfortunate that we did not make a right choice in the last month elections, where we allowed the same bunch of liars and looters to rule us again. We have forgotten the situation we found ourselves in the last years, and still we are going to face it again for another good four years- what a pity! It’s my candid opinion that the Northern part will suffer a lot, because the so-called northern leaders in the north have sold the right of their people to the politicians.

We all witnessed what happened in some of the northern states when the presidential election result was announced, and the upheavals led to the loss of lives, properties of millions naira were vandalized, thousands of people fled their houses, etc and these so-called leaders in the north are the caused because they don’t protect the interest of their people. They only protect their interest and pocket. Even Chief Obasanjo, the former President of this country confirmed this when he said to Jonathan “the northern leaders are ravenous and egocentric. Use what their brother (Yar’adua) left behind and bribe them, they will vote for you” imagine! Surely, the northern part will continue to remain where they are if their so-called leaders did not change, and their children will definitely continue to be slaves forever and remain backward in terms of education.

Conclusively, the upheavals in the northern part should serve as a deterrent to our leaders, and know that Nigerians are pushed to the wall and they can stand up and fight for their right whenever the need arises! A word, they say, is enough to the wise.

Friday, December 31, 2010

HISTORY AND THEORY OF LIFE ENCOUNTER.


Man is a product of his thought life. No one can ever rise above the level of his thinking, and life should always mean something to a person- this has been something I have always believed in. people should realize how lucky they are to be alive in this world, and should make the most of what time they have on earth to strive to achieve what they love. Through this effort, they should also try their best to make the world around them a better place. I was born two and half decades ago, at Anguwar Fatika village, Zaria-Nigeria. I’m a student of Agricultural Engineering (though the programme is on hold now), I am fond of writing and reading, but unfortunately found myself in Engineering field-though I strongly believed that through Agriculture, I can help my country in terms of simplifying ‘food production’, and making it available across the nation, and it will serve as a source of income to the country.
As a hobby to me, I read anything I can get my hands on- newspapers, books, brochures, magazines, online materials, etc. I wonder why some people are very opposed to reading. Reading is a good habit, and there is so much to benefit by reading, as well as serving as a way to rest. I love to read, write and make new friends always.
This world is full of mysteries. So far, I’ve learnt a lot of lessons in life. People kiss you and betray you; they smile at you and at the same time hate you. It’s true that problems are the spice of life, and life without it (problem) is an Illusion. And for every problem, there is an expiry date- problems are not meant to make us down, but to tell us that we have a lot of challenges ahead of us in life. Everybody in this world has some worries, but worries are only natural and human- Also everyone is at least sad at some point, but life is not all time sadness. People go through pains and agonies in life, obstacles here and there while trying to achieve something. But no matter what we may come across along the way, we should always remember that there is still space at the top, and the ladder of success is never crowded at the top- also challenges and set backs are not new in the game of life.
No doubt, year 2009 and 2010 will never go away from my memory. I’ve suffered throughout the years and the memory still brings to my eyes tears. Indeed, life is full of challenges. But as a true believer, I believed that what God has destined for us, no human being on this earth can change it, and He has a reason for everything. Failure was never part of my dream because I live in the world of dream and I dream big. I thought I’ll succeed always in whatever I want, but life proved me wrong. In this life, it’s good to understand that one don’t have to be the most intelligent person to make it in life, but always aim to be the one that makes it to the top even when you think you can’t, continue and don’t stop, work hard with dogged determination-and that’s the best reward you can give people who fight and limit you, by saying you can never amount to anything.
Despite the challenges I encountered, today I can say am the luckiest among my colleagues. I am grateful to the Almighty Allah for His grace and Mercies. ‘Never give up in life’ will always be my advice to people, because nothing is impossible with God. And we should always put it at the back of our mind that there is time for everything, and our destiny cannot be denied, it can be delayed only. One has to sometimes fight a battle more than once in order to win, today I am indeed grateful to God; the sky is not just my limit now, but the starting point. I wanted to be a soldier first, then considered becoming an Engineer, finally now an Aviator in the making. Truly, every disappointment is a blessing-ALHAMDULILLAHI.
I like politics in my life, but hate to be a politician because of the way and manner we take politics in Nigeria, and am not one to be dabbled too much in matters which do not concern me. I believe as a person am not very outspoken, but can write a lot- some people frequently describe me as being shy or reclusive- but that is not true, because when one gets to know me, one realizes that I can be quite friendly and nice. I endorsed the idea that the only way to help our dear country move forward is actually by trying to do something about the problems we face, and for me, this means engaging in reading and writing-though some people said it’s through politics we can help our country, yes agreed. But I believe if we cultivate the reading and writing habit, we can make this country a better place to be by offering our suggestions and contributions through the available means (such as media) on how things should be done in our dear country-Nigeria.
In life, I want to be happy and see other people happy, because life is all about helping and lifting others; it’s about making worthy and laudable contributions, and impact. It’s also about being useful to our mankind. My aim always is to be the voice of the voiceless in Nigeria if not in the world. Because our future doesn’t look bright, and the only thing we can do now is to stand up and fight for our right- I always wonder when Nigeria will ever be right as it keeps on diminishing right before our very sight, and the worst part of it is the inefficiency of our leaders-as most of them are but a bunch of liars. There is no better time to make meaningful contribution to Nigeria than now, a time when our country is at a crossroad, a time when people think wrong, when values are distorted, when smartness is considered a higher virtue than honesty; when rigging is celebrated and people defend wrong actions because it pays them in the short term. What legacies are we leaving to our unborn child? We have to wake up, think deep and also speak out the truth always even if the leaders will not listen- lets use our pen and communicate to them. It will be a rough journey I know, but believe me our efforts will surely not be in vain. Our pen should always be our weapon!
Last but not the least; life is beautiful, indeed beautiful but short. If we can truly sit down and remember the last day, we can see this life has nothing to pay. Therefore, the earlier we REPENT the better, because we don’t know when the angel of death will come. It could be today, tomorrow or next-only God knows. We all are sinners in one way or the other, so the best thing is to bow to the creator, the Supreme Being and ask Him for his forgiveness and our well being, and say no to bad things again. The end is getting nearer, and time waits for no one. This last paragraph is my resolution at the age of 25. Lastly, remember not to give up in life. In brief, this is my history and theory of life encounter.

Saturday, October 2, 2010

SHEKARU HAMSIN NA SAMUN MULKIN KAI: RIBA KO ASARA?



Kwanci tashi ba wuya, shekara kuma kwana ne inji masu iya magana. Yau shekaru hamsin kenan da kasar nan ta samu ‘yancin kanta daga turawan mulkin mallaka na Ingila a ranar 1 october, 1960. Inda a wancan lokacin ‘yan kishin kasa irin su Alhaji Abubakar Tafawa Balewa, Sa Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto, Nnamdi Azikwe, Cif Obafemi Awolowo sukayi fafutukar ganin kasar nan ta samu ‘yancin kanta, tare kuma da aikin ginata da kuma inganta ta ba wai gina kawunansu ba kamar yadda muke ganin shugaban nin yanzu sunayi.

Shekaru hamsin da akayi na samun ‘yancin kai lamari ne da ya dace ‘yan Nijeriya musamman ma talakawa suyi waiwaye suga irin ribar da suka samu a wadannan shekaru. Koda yake, tuni ‘yan Nijeriya suka bayyana rashin jin dadinsu da irin bala’i da halin kaka-ni-kayi da suka shiga a tsawon wadannan shekaru a karkashin mulkin shugabannin da suka samu a halin yanzu wadanda ke sanya bukatunsu a farko kafin bukatun al’ummar da suke ma mulki. Sabanin irin salon mulkin da mazajen jiya suka rika yi, inda a kullum buri da bukatun talakawansu ne a gaba kafin nasu bukatun. Alal misali, Sa Ahmadu Bello “primier” jihar Arewa ya fito daga jihar Sokoto, amman ya ga babu inda yafi da cewa da a gina jami’a a yankin arewa a wancan lokacin sai Zaria, domin nan ne ya zamo tsakiyar Jihohin arewa, wanda inda yanzu ne saidai shugaban dake mulki yace a ginata a garinsa!

A wancan lokaci ba’a san wani abu wai cin hanci da rashawa ba, kuma idan mutum yayi laifi komin girmansa da mukaminsa a kasa, doka zatayi aiki akansa ko da kuwa Sa Ahmadu Bello ne ya haifeshi, sabanin abinda yake faruwa a yanzu inda akema dokoki karan tsare, tare da hana hukunta masu laifi indai suna da uwa a gindin murhu. Wannan mummunan dabi’a na rashin bin doka da oda da kuma barin fannin shari’a tayi aikinta yadda ya kamata ya kara kazancewa ne a zamanin mulkin Cif Olusegun Obasanjo na baya bayan nan, inda ya rika cin karensa ba babbaka a kotunan kasar nan tare da yin hawan kawaraye ga dokoki.

Akwai al’amurra da dama da ya kamata a duba, don a fahimci irin ci gaba ko akasin haka a wadannan shekaru hamsin da kasar nan tayi da samun ‘yancin kai. Idan aka dubi fannin wutar lantarki, wanda shine uwa uba, kuma sanadiyyar sa masana’antu da dama sun durkushe,lamarin ba’a cewa komai. Lokacin mulkin Obasanjo na farar hula ba irin kwamiti da ba’a kafa ba don samun saukin abun amman duk abanza, domin kuwa ankashe biliyoyin naira lokacin Obasanjo amman kwalliya bata biya kudin sabulu ba. Har yau, anada matsalar rashin kyakkyawar ruwan sha, wanda hakan yasa ake ta samun karuwar cututtuka a kasa. Rashin kwakkwaran tsarin kula da lafiyar yan Nijeriya, asibitoci babu kwararrun likitoci da magunguna. Tabarbarewar tsarin ilimi duk kuwa da cewa muna da makarantu da jami’o’i masu yawa amman babu ilimi mai nagarta da kayan koyarwa na zamani. Ga rashin tsaro,inda ta kai ga cewa a ranar da ake farin cikin cika shekaru hamsin da samun ‘yancin kai saiga bama bamai sun tashi a cikin dandalin da shugaban kasa ke jawabi! Yin garkuwa da mutane kuwa ya zama ruwan dare a Nijeriya, inda ba babba ba yaro, ga yawan kashe bayin Allah da basuji basu gani ba. Fannin noma ma duk bata canja zani ba, wanda ada noma itace babban hanyar da Nijeriya ke samun kudaden shiganta kafin zuwan man fetur amman yanzu anyi watsi da ita. Rashin aikin yi ga ‘yan kasa sai karuwa yakeyi, wanda hakan shi ke yawaita samun ‘yan zauna gari banza da kuma jefa wasu shiga cikin miyagun ayyuka. kasuwannin hannu jari kullum sai kara durkushew sukeyi. Hanyoyin sufuri sun zama wani kadarko na mutuwa saboda rashin kyawunsu, kuma haryanzu ba’ayi wani abu da zai nuna cewa gwamnati ta damu da lamarin ba.

Kullum dai abin sai kara tabarbarewa sukeyi duk kuwa da irin arzikin da Allah yayi wa Nijeriya. Alkalumma sunyi nuni da cewa tun bayan da kasarnan ta samu ‘yancin kanta, ba’a taba samun kudaden shiga ba kamar shekaru goma na baya da suka wuce, amman talaka bai gani a kasa ba! Shin ina kudaden suke zuwa ne? koda yake arzikin kan komane aljihunan kalilan daga cikin ‘yan kasa sauran kuma a kashesu ta hanyar da bazasu amfani al’umma ba. Kamar dai yadda a shekarun baya aka sayo wai karnukan ‘yan sanda kan naira miliyan biyu akan ko wani kare guda daya! Alhalin ‘yan Nijeriya na fama da yunwa da talauci, cin abinci sau uku yana wuya a rana. Wanna lamari da mai yayi kama?
Na tabbata yau dasu Sardaunan Sokoto zasu fito daga kabari suga irin halin da kasarnan take ciki, wallahi sai sunyi allah ya isa da Tir da salun mulkin shugannin yanzu. Domin kuwa sunci amanasu na kin gudanar da mulkin adalci tare da gina al’umma kamar yadda su Sardaunan sukayi. Saboda mafi yawancin shugannnin yanzu dake madafun iko sunci gajiyar mulkin adalci da su Sardauna sukayi, domin mafi yawancinsu karatun da sukayi kyauta ne ba tare da sun biya koda sisin kwabo ba. Amman a yau su mene sukayi wa fannin ilimi? ‘ya’yansu ma basa karatu a kasar sai dai kasashen waje, wanda hakan yasa sukeyiwa fannin ilimi rikon sakainar kashi. Wanda yayi makarantar elementare a da yafi dan jami’ar yanzu iya turanci da sanin boko. A da muna da jiragen sama, da na kasa, da na ruwa, wutar lantarki, ruwan famfo, kamfanin sadarwa duk suna aiki yadda ya kamata, amman yanzu fa? A yau Nijeriya bata da kima a idon duniya sakamakon babakere da handama tare da halasta kudin haram da shugabannin kasar nan keyi, kuma kullum gashi darajar kudin mu sai kara durkushe wa yakeyi.
To wai a tsawon wadannan shekaru anci riba ne ko asara akayi? Kuma ina aka dosa? A gaskiya za’a iya cewa babu wani amfani da aka samu da mulkin kai, kila ma gara mulkin turawan da abinda yake faruwa a kasa. Domin kuwa su turawan mulkin Ingila a wancan lokaci sun gudanar da mulkin adalci ba tare da nuna bam-banci tsakanin talaka da sarki ba ko mai kudi a duk lokacin da sukazo yin hukunci, abinda yayi wuya a halin yanzu karkashin mulkin ‘yanci. A gaskiya ya zama dole shugabannin Nijeriya su sauya salon yadda suke gudanar da mulki, dole su maida bukatun al’ummarsu a farko kafin komai, su samar da aikin yi ga ‘yan kasa tare da yin ayyukan da zasu kawo ma kasar ci gaba ba kawunansu ba. Kuma a fardado da masana’antu da suka durkushe don samar da aikin yi ga matasa,tare da samar da ingantaccen hasken wutar lantarki wanda shine jigo kan daurewar masana’antu.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.

Thursday, August 26, 2010

TSARIN KARBA KARBA: Yarjejeniyar PDP?

A kwanakin bayane, jaridun kasar nan da kuma kafafen yada labarai suka cika al’ummar kasar nan da labarai kan dambarwar siyasar da ta mamaye jam’iyyar PDP mai mulki kan tsarin karba karba na jam’iyyar, inda wasu ke nuna goyon bayan aci gaba da bin wannan tsarin yayinda wadansu ke ganin lokaci yayi da za’a sakinma kowa mara a jam’iyyar ya nemi takara ba tare da anyi la’akari daga ko wani shiyya ya fito ba.

Ga dukkan mai bibiyar al’amurran siayar kasar nan, musamman ma akan jam’iyyar PDP yasan tsarin karba karba na jam’iyyar ya samo asaline a shekarar 2002 lokacin da ake dab da zaben shekarar 2003 inda jama’a da dama kamar mataimakin shugaban kasa na wancan lokaci Atiku Abubakar dama suaran mutane suka nuna sha’awarsu na tsayawa takarar shugabancin kasar nan, amman haka bata yiwuba sakamakon yar jejeniyar da dattawan jam’iyyar sukayi kan yadda jam’iyyar zata rika fidda dan takara. Yar jejeniyar wacce ta amine dan kudu yayi skearu takwas yana mulki, kana dan arewa shima yayi mulki na shekaru takwas, wanda hakan ne ya baiwa cif olusegun obasanjo damar ci gaba da rike madafun iko a shekarar 2003 har zuwa shekarar 2007.

Kasancewar jarjejeniyar da jam’iyyar PDP tayi ne yasa a shekarar 2007 marigayi umaru musa Yar’adua ya zamo shugaban kasa bayan hukumar zabe ta bayya nashi a matsayin wanda ya samu rinjaye a kuri’un da aka kada. Kasancewar Yar’adua shugaban Nijeriya a shekarar 2007 ya nuna cewa mulki ya dawo arewa, kuma za’ayi tsawon shekaru takwas kenan dan arewa zaija ragarmar mulkin kasar. Sai dai a halin yanzu, hakan na nema ya zama tarihi. Musamman ma ganin yadda wasu ke kaiwa da komawa don ganin an tabbatar ma shugaba Goodluck wanda ya dare madafun iko sakamakon rasuwar shugaba Yar’adua , wannan kujera a shekarar 2011 maimakon dan arewa. Yanzu takai matsayin wadansu a jam’iyar na PDP na cewa basu san batun karba karba a jam’iyyar ba, ahalin kuwa sune sukayi wannan yar jejeniyar.

Wani abin ban haushi da kona rai shine yadda tsohon shugaban kasar nan Olusegun Obasanjo wanda shine mutum na farko da ya ci ribar karba karban, amman yau yayi kememe ba kunya ya fito fili ya shaida ma duniya cewa baisan batun karba karba a jam’iyyar ba. Shima sabon shugaban jam’iyyar na PDP wanda aka daurasa don yaja akalar jam’iyyar bayan murabus din tilas da akasa halastaccen shugaban jam’iyyar Vicent yayi don yaki yarda a rushe yarjejeniyar da akayi kan karba karaba ya fito fili yace babu batun karba karba a PDP. Koda yake, kalaman na sabon shugaban PDP ba abin mamaki bane, domin abinda aka kawosa yayi kenan, wanda sabanin yin hakan za’ayi waje rod da shine.

Amman ayar tambayar anan itace, me yasa za’a rushe tsarin karba karba na jam’iyyar PDP a halin yanzu yayin da arewa ke yin nasu wa’adin na shekaru takwas? Ko kuwa rasuwar Yar’adua ta zama wani dama ne na da’a ruguje wannan yarjejeniyar. Me yasa shugabannin arewa suka zama yan abi yarima asha kida ne, musamman ma gwamnoni. A zahirin gaskiya, indai har za’ayi adalci to kamata yayi a bari arewa ta kamala nata wa’adin mulkin kafin a rushe tsarin karba kraban, wanda kin yin hakan na iya haifar da komai a kasar na. lokaci yayi da ‘yan arewa zasu maida hankali wajen ci gaban yankinsu, koda yake shugabanninmu sune ke kawo mana koma baya a kowane fanni, musamman ma idan mukayi la’akari da taron da gwamnonin arewa sukayi a baya kan batun karba karba inda sukaje suka yi gaban kansu ba tare da jin ra’ayoyin talakawansu ba.

Sanin kowa ne kamar yadda su gwamnonin ke ikirari, cewa ko wane dan kasa yana da ‘yancin yin takara idan zabe yazo. Tabbas wannan haka yake, kuma shima shugaba Goodluck kamar ko wane dan Nijeriya yana da ‘yancin tsayawa takara a shekarar 2011, amma fa ba’a jam’iyyar PDP domin akwai yarjejeniyar da ta amince cewa yanzu dan arewa ne zai yi mulki. Idan kuma har Goodluck yaga yana da sha’awar dole yayi takara a 2011, to sai ya bar jam’iyyar PDP ya koma wata jam’iyya yayi takara. Yin haka shi zai nuna cewa an girmama wannan yar jejeniya da akayi a baya, kuma kimar shugaba Goodluck zata karu don mutumta wanna doka da yayi.

Alla yasa ayi zabe lafiya kuma a samu shugabanni masu kishin talakawansu da zasuyi aiki don ci gaban al’umma, ba masu kishin aljuhunsu bad a cigana iyalansu kawai. Allah yai mana jaogarnci a dukkan al’amuranmu nayau da kullum.

Monday, July 19, 2010

ZONING: Agreement by PDP Elders..


Zoning in PDP is an agreement by well respected elders of the party, and any attempt to change it at this critical period will not bode well for this country. Therefore, President Jonathan should please turn deaf ears to people who are calling on him to contest the 2011 election. I’m surprised by the PDP national chairman’s claim that zoning is no longer in the agenda of PDP. Was the chairman not aware when the agreement was made?

We all know that President Jonathan like any other Nigerian has the right to contest for any political office, but it shouldn’t be in this case under the platform of PDP because of that agreement. The southern part of the country were allowed to rule for eight years and its now turn for the northern part, and Yar’adua’s demise should not alter it until after 2015. I hold no brief for PDP to win, I’m only saying that the agreement of the party should be respected. But if President Jonathan must contest the presidential seat come 2011, he should decamp to another party and contest but not under the platform of PDP. Therefore, the hungry national chairman should know that there is no need to revisit zoning now.

Sunday, June 6, 2010

12th ANNIVERSARY OF GEN. ABACHA'S DEMISE!



June 8,2010, will be exactly 12years that Almighty Allah deemed it fit to take back the life of Gen. Sani Abacha.

The death of General Abacha is a great lost not only to his family, but to the entire nation-because he was a great patriot and a brave general who dedicated himself to the service of his country. Abacha had a vision, he meant well for Nigeria, and we never had a peaceful president like him. History will always remember general Abacha as a hero who did his best for his country. We pray to Almighty Allah to continue to give the family, friends and well wishers the fortitude to bear the irreplaceable lost.

We also pray that your gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.

Abacha we are still with you in spirit and we love you, but God loves you more.

Kwanci tashi babu wuya inji malam bahaushe, A ranar 8 ga watan yuni na wannan shekaran ne tsohon shugaban mulkin sojan kasarnan marigayi janar sani abacha ke cika shekara goma sha biyu da rasuwa

Alal hakika rasuwar janar abacha ya girgiza dukkan alahirin yan nijeriya, musamman ma ganin yadda a wancan lokacin yayi yun kurin farfado da tattalin arzikin kasan nan, da kuma biyan basukan da kasashen ketare ke bin mu, amman hakan batayiwu ba sai mai kowa mai komai ya dauki abinsa.

Duk dan nijeriya mai bibiyar yadda al’amurra suka rika kaiwa da komowa a wannan kasa
lokacin mulkin marigayi janar abacha, yasan cewa shine shugaban da al’ummar nijeriya baza su taba mantawa da shiba. Domin kuwa a lokacin mulkin sane yayi shelar cewa duk kasashen ketare da ke bin kasarnan bashi za’a biyasu kuda densu ba tare da bata wani lokaci ba, amman saboda butulci, yaudara,mugunta da keta irin na nasara sai sukayi kememe suka ki amsar kudaden nasu wai saboda wa’adin da aka ba nijeriya na data biya wadannan basukan basu cika ba. Gashi a yau kuwa basukan sai kara karuwa sukeyi kuma da dukkan alamun babu ranar biyansu..

Har ila yau, janar abacha ya kasance shugaban nijeriya na farko da yaki bada kai bori ya hau ga kasashen yammacin turai da sauransu, musamman ma ganin yadda yafi mai da hankali ga kasashen afrika wajen gudanar da harkokin mulkinsa. Hakan kuwa yasa kasashe da dama suka rika sanya ma nijeria takunkumi, wai suna masu cewa tarayyar nijeriya nada shugaba mai mulkin kama karya. Wannan furuci nasu kuwa ba komai ya kawo shiba illa kin yarda da janar abacha yayi nadasu shigo kasar nan su rika cin karensu babu babbaka-kamar dai yadda labarin yake a yanzu, domin kuwa yanzu kowa yasan cewa kasashen yamma na taka rawa sosai kan yadda ake gudanar da mulki ko harkokin kasar nan. Wanda a wancan lokaci janar abacha yaki yarda da hakan.
Saboda rashin fahimtar salon mulkin janar abacha, wasu yan nijeriya da dama suka bi sahun kasashen ketare wajen yin tir da gwamnatin nasa suna masu cewa wai kasarnan tana fama da talauci,yunwa ,rashin aikin yi, rashin tsaro da dai sauran korafe korafe da dama.

Da madai ance dan adan ba’a iya masa face ubangijin daya halicceshi, duk kokarin da marigayi janar abacha yayi a lokacin mulkinsa na ganin yan nijeriya sunji dadin wannan gwamnatin, duk jama’a basu ganiba sai tsinema mulkinsa aka rika yi ana Allah wadai da ita. Kodayake gaskiya tananan a gaskiyarta, domin kuwa a yanzu al’ummar kasannan sun fahimci irin hangen nesan da janar abacha ya rika yi da kuma irin gyara kasannan dayaso yayi. Domin kuwa yanzu sun dawo suna kewarsa.

Ba komai yasa suka gane hakan ba illa irin halin da suka tsinci kansu daga farkon shekarar 1999, wanda hakan yasa yan nijeriya yanzu sun gane cewa tabbas janar abacha gwarzon shugabane kuma mai kishin kasar san e da nahiyar afrika. Duk da irin tonon sililin da tsohuwar gwamnatin kasarnan karkashin mulkin Obasanjo ta rika yiwa iyalan janar abacha baisa yan nijeriya yin nadama da kewar da sukeyi na shi abachan ba, illa karamasu karfin gwuiwa. Domin kuwa kowa yasan kahon zukar da gwamnatin tasa ga iyalan janar abacha siyasa ne kawai, domin so suke su bata masa suna a idon duniya…dayake Allah ba azzalumin kowa bane sai gashi yau itama waccan gwamnatin data rika kwance wa iyalan janar abacha zani a kasuwa goguwar ya koma kanta, kuma dukkan abinda da akace ana zargin gwamnatin data shude haka yake babu ko tantama. Koda yake nasan yan nijeriya sunsan abinda nake nufi, kuma sune suka fi dacewa dasu fadi hakan don sunsan irin halin da suka tsinci kansu cikin shekaru takwas da suka gabata ko shekaru goma.

Daga karshe, babu abinda zamuce illa allah ya gafartama janar abacha, ya kyautata kwanciya, yaba iyalansa da abokan arziki kara jure wanna babbar rashi, yasa aljanna firdaus makoma, mu kuma idan tamu tazo yasa mu cika da imani. Sukuma shugaban ninmu Allah yasa suyi kishi irin na marigayi janar abacha, kuma yabasu ikon sauke nauyin dake kansu.

Friday, May 28, 2010

ELEVEN YEARS OF DEMOCRACY: Success or Failure?


Day in, day out, a wise man says that a year is just akin to a day. It is now eleven years since the return of civilian and democratic rule or government in Nigeria and simultaneously the incumbent president, Goodluck Jonatan, is now in his third week in office after stepping into the shoes of the former president Late Umaru Musa ‘Yar’adua who died some weeks back, after spending about three years steering the mantle of leadership in Nigeria as its number one citizen from 2007 to 5th May 2010.



It is now desirable for Nigerians, especially those at the grass roots level, to look back and cogitate over this period of decade of democratic rule in Nigeria on what dividend or developments do they achieve or experience. Though they have since expressed their dismay over the catastrophic conditions they had found themselves during the eight years of draconian rule of Mr. Obasanjo.Those conditions/situations of unemployment, high cost of living, melting down industries and factories, e.t.c during those eight years of Obasanjo were some of the reasons that necessitated Nigerians to come out during the 2007 General elections (in order) to bring changes and thereby find a lasting panacea to their worries.



Few Nigerians expect that there could be a meaningful change on the ground of the mannerism of leadership of late Yar’adua at the inception or assumption of office by trying to legitimatize his government to the Nigerians in particular and the whole world in general. This is clearly because he is fully aware that the election that brought him into office was characterized by an unprecedented election malpractices in the history of Nigeria . Respect for the rule of law, independence of the judiciary, unity government, zero-tolerance to corruption, and the like, are some of the reasons why some Nigerians welcomed the late Yar’adua’s government. He (Yar’adua) actually delivered the goods with respect to the independence of the judiciary. This is corroborated from the fact that he remained mute when the election Tribunals and Courts were busy nullifying the elections of P.D.P candidates at the various level of government on the ground of electoral malpractices. Late Yar’adua has, without any iota of doubt, shown a sense of maturity in that respect which was not obtained in the Obasanjo’s era.



The recognition of the autonomy of the judiciary and that of the other branches of government by the Yar’adua’s administration had crucially changed the minds of many Nigerians from expecting to the hoping that a new messiah has come to save Nigeria and Nigerians from the shackles of squalor and poverty which they found themselves in during the Obasanjo’s era.

If we look at the power sector during Obasanjo’s regime, many committees were constituted to address the issue but with little to show. Billions of Naira have been spent fruitlessly. The present administration has also constituted the committees some years back for the same purpose but with little or no success at all. Many problems are still deeply rooted in the country ranging from lack of potable water, defective health system, educational degradation, lack of security and agricultural backwardness, to mention but a few.



It is very unfortunate that despite the vast natural resources that God in his infinite mercy endow Nigeria with, the resources are mismanaged by a very few and the masses are left in squalor and poverty. The national cake is being looted and squandered by few out of Whims and Fancies to the detriment of the majority. In some instances the money is spend not in the right way as in the case where dogs were transported into the country at the price of 2 millions naira. What a madness!



Jonathan should as a matter of urgent, address these issues once and for all to avoid further escalation of the problem, Especially the internal problem surrounding his party (PDP) so as to ensure a credible election come 2011 becouse we need to have a credible, free and fair election not selection. the election that will be accepted by all Nigerians and international observers, so that at the end, he (jonathan) will be trusted more, and also earn reputation both at home and abroad.



Now the question is what is the benefit derivable from the Nigerian democracy, is it a dividend or a loss? Infact there is nothing tangible to show which Nigerians can be said to have been benefited in the fast eleven years of democratic rule. Indeed the poor remain poorer and the reach remain reacher by day. This is therefore a challenge to the Jonathan’s government to do something concrete before the remaining year elapse and it then become too late to cry.