Sunday, September 27, 2009

BIRNIN KANO YA DAUKI BAKUNCIN TARON GIZAGO KARO NA FARRKO


A jiya asabar ne 26/9/09 akayi taron gizago karon farko na kasa baki daya a birin kano. Assalamu alaikum yan uwa maza da mata na wanna dandali, ina mai mika godiya ta da farinciki gareku baki daya da kuka sami damar halartar babban taron wannan kulob namu na GIZAGO SOCIAL AND CULTURAL. hakika yadda maza da mata mambobin wannan kungiya suka amsa kira tareda masu mata fatan alahiri sukayi cincirondo zuwa wannan taro kwansu da kwarkwatansu daga sassa daban daban na kasar nan, wata kila ma harda makwabta abin farin cikine kwarai da gaske, kuma wata alamace ta cimma burinmu.
godiya ta musamman ga Dr. Bala Muahammed, sheik aminu daurawa, malam bashir yahuza malumfashi, aburrahaman haruna(dodo) da sauran manayan baki maza da mata da sukaa sami zarafin halartar wannan taro duk kuwa da irin aikin da ke gabansu. bani da ingantacciyar kalmar da zan iya gode maku illa ince allah yasaka da alhairi kuma yabar zumunci amin. Suma wadanda suka gabatar da shirin, Ado ahmad gidan dabino da Mk Adam muna jinjina masu sosai. haka shima malam nura adamau yayi namijin kokarin yadda ya rinka kaiwa da komowa, ga su shafi'u imam, da dai sauran mutane da dama.
haku suma manbobin kungiyar nan kun cancanci yabo, musamman ma malam Mk Adam, agogo sarkin aiki, buldoza, aiki ga maiyinka, hakika yayi kokari domin tun kwana uku kafin buki ya iso kano don ganin shirye shirye ya kankama yadda ya kamata. itama shugabar mata ta kasa hajiya aisha lawal, da mataimakiyar ma'aji haiya huawa ahmed sunyi aiki kwarai da gaske, Allah ya saka da alhairi. sauran mambobi maza da mata daga dukkan jihohin da suka iso wanna taron ina maku godiya ta musamman da fatan kowa ya koma gidansa lafiya.
ina mai farin cikin shaida maku cewa in Allah ya yarda taro na gaba kamar yadda nayi bayani tun farko, za'ayi sane na garin gwamna, cibiyar ilimi, kasar balaraben sarki, bugu da kari sarkin sarakuna.
nagode Allah yasaka da alhairi, ya bar zumunci. wassalam
MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
NATIONAL CHAIRMAN,
GIZAGO SOCIAL AND CULTURAL CLUB
080-36397682
http://anguwarfatikaonline.blogspot.com

Tuesday, July 28, 2009

TABARBAREWAR ILIMI A NIJERIYA.



TABARBAREWAR ILIMI A NIJERIYA.:ummul aba isin yajin aikin jami'o'i



Yau a Nijeriya, harkan Ilimi ya shiga halin ko in kula da kaka ni kanyi saboda irin rikon sakainar kashi da rashin bashi muhimmanci da wadanda alhakin abun ya rataya a kansu.Akwai abin takaici kwarai da gaske idan mutum yayi la'akari da irin halin kuncin da wasu mutane suke ciki wadanda rayuwarsu ke da matukar tasiri ga kasarmu, amma aka kyalesu cikin bakar wahala sakamakon wani tsari na mulkin mallaka da ba kowa ke cin gajiyarsa ba. Wadannan mutane sun kasance tsani da mutum kan taka har ya kai ga wani matsayi a rayuwarsa. har ila yau wadannan mutane suke dasa harsashin ganin fadi-tashin da mutum keyi a rayuwarsa har ya cimma wani matsayi ko nasara a rayuwa.



wadannan mutane ba wasu bane illa malaman makaranta wadanda dan abin da suke samu bai taka kara ya karya ba in aka kwatantashi da irin aikinsu na sadaukarwa. Matsayin malaman makaranta ga ginin kasa da al'umma al'amari ne da ba ya misaltuwa. Komai matsayin mutum, duk yadda ya kai da daukaka a rayuwa sai da yabi ta hanyar malamai kafin ya cimma wannan matsayi.



yajin gama gari da malaman jami'o'in kasar nan keyi abin kunya ne ga wannan gwamnatin karkashin jagorancin Alhaji Umaru Musa Yar'adua, wanda shima tsohon malamin makaranta ne amman yayi biris da bukatunsu, yaki yaji kukansu balle ayi tunanin share masu hawayensu.

yau a kasarnan, dalibai kan shafe shekara takwas suna karatun da ya kamata ace anyisa a shekara hudu saboda yajin aiki da malam kanshiga lokaci zuwa lokaci, yayinda takwarorin karatunsu da kanje kasar malaysia ko Amurka kan share shekara uku kacal don samun digiri daidai da na nijeriya da akan kwashe shekara takwas ana yinsa sakamakon yajin aikin. malamin makaranta ba'a dauke shi a bakin komai ba a Nijeriya, bashi da daraja a idon shugabanni da su kansu daliban, duk kuwa da cewa duk wani shugaba dake tun kaho a kasar nan dama duniya baki daya malamin makaranta shine tsanin farko da yabi har ya kai ga wannan matsayi da yake.





Wannan karara ya nuna hujjar da malaman jami'o'i ke da ita ta shiga yajin aiki saboda irin halin ko-in-kula da gwamnatocin da aka yi a kasar nan suka rika nunawa game da batun kyautata rayuwar malaman. Don gwamnatin 'Yar'aduwa ma tafi kowacce nuna halin ko-oho game da mummunan matsayin da malaman jami'o'i ke ciki, sai tafi mayar da hankali ga biyawa 'yan majalisu burinsu na wasoso akan dukiyar jama'a. Yayin da aka yarjewa dan majalisa ya rika kwasar Naira miliyan goma (N10,000,000) a kowane wata, wani malamin jami'an idan kaji albashinsa sai ka rike baki kana salati, don kuwa abin ba'a cewa komai. koda yake ba komai ya haifar da rikon saikanar kashi da shugannin keyiwa harkar ilimin kasar nan ba face cewa 'ya 'yan su basa karatu a kasar nan, sun turasu kasashen waje suna biyamasu kudin karatun nasu da dukiyar al'umma.



Ilimi dai shine kashin bayan ci gaban al'umma, amma wadansu na kokarin gurguntashi saboda tsabar keta. Ya kamata Gwanmatin Yar'adua ta gaggauta daukan mataki don kawo karshen wannan yajin aikin gama gari da jami'o'in kasar nan keyi don baiwa dalibai samun zarafin kammala karatunsu a kan lokaci.

Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukanmu na alhairi, amin.

YAWAN MUTUWAR AURE: WAKE DA LAIFI?

HAKIKA

Monday, July 13, 2009

CE-CE KU CE KAN ZIYARAR OBAMA ZUWA GHANA

Tun bayan da shugaba Barack Obama na Amurka ya bayya aniyarsa ta kai ziyara zuwa kasar Ghana, al'ummar Nijeriya keta ce-ku-ce kan wannan ziyarar ganin Obama bai zabi Nijeriya ba duk kuwa da dimbin tattalin arzikin da kasar keda shi fiye da Ghana, sai kuma uwa uba kallon da akeyima kasar (Nijeriya) a matsayin uwa maba da mama a nahiyar afrika.



Sanin kowane bawai wani abu yasa obama ya zabi zuwa Ghana ba face yadda suke mutuntawa da kuma girmama dimokuradiyya. Hakan ya fito filine bayan halastacce kuma tsarkakakken zaben gama gari na kasar, inda jam’iyar hamayya ta sami rinjaye kan jam’iyar dake mulki kuma aka tabbatar mata da nasarar da ta samu (lamarinda yasha banban da Nijeriya). Rashin yin magudin zabe da satar kuri’u da Ghana batayi ba shi ya kara tabbatar mata da mutunci a idon duniya da kuma nuna yadda kasar ta rungumi akidar dimokuradiyya ta ingantacciyar hanya. Wadan nan sune manyan dalilan da yasa shugaba Obama ya zabi zuwa kasar Ghana bai dauki Nijeriya ba (kasar da magudin zabe, satar kuri’u, zaben kaci-baka-ciba ,baka-ciba-kaci,,cin hanci da rashawa da rashin baiwa yan kasa hakkokinsu ya zama abin ado). Don haka, banga dalilin da zaisa al’ummar Nijeriya musammanma mukarraban gwamnati su rika tada muryoyinsu kan wannan ziyarar da Obama ya kai Ghana ba, domin kuwa kamar yadda Obama yace “amurka zata dada karfafa zumunci da kuma taimakon ta ga kasashen da suka rungumi dimokuradiyya ta halastaccen hanya”. Abin tambaya a nan shine,musamman ma ga wadanda suke korafin cewa Obama yaki zuwa Nijeriya- wai mulkin dimokuradiyya akeyi a Nijeria?



Hakika wannan ziyarar da obama ya kai Ghana ya zama kalu bale ga Nijeriya, kuma hannunka mai sanda ne ga sauran kasashe irin Nijeriya wadanda suka maida mulki kamar gadon gidansu da kuma hawa madafun iko ta ko wani irin hanya. In har Nijeriya na son Obama ya kawo irin wannan ziyarar daya kai Ghana to saifa ta inganta hanyoyin zabe ba tare da yin magudiba, rungumar dimokuradiyya ta halastacciyar hanya, baiwa yan kasa hakkokinsu, sakinmara ga jam’iyyun adawa da kafofin yada labarai masu zaman kansu da dai sauransu. Tabbas yaU Ghana ta zama farin wata sha kallo kuma zakaran gwajin dafi a nahiyar afrika. Ghana ta ciri tuta wajen cigaban al’ummarta duk kuwa da cewa kasar tana daya daga cikin kasashen dage baya wajen tattalin arziki a nahiyar afrika, amma saboda da shugabanni masu kishin ci gaban kasar da take dashi yasa a yau sunfi Nijeriya ci gaba ta ko wani hanya amman banda hanyar magudin zabe da satar dukiyan talakawa. Kalu balenku shugabannin Nijeriya.

Allah yai mana jagoranci a dukkan ayyukan mu na alhairi, amin.

Monday, June 8, 2009

ELEVEN YEARS REMEBRANCE OF LATE GEN. SANI ABACHA.


Today June 8,2009, is exactly 11years that Almighty Allah deemed it fit to take back the life of Gen. Sani Abacha.

The death of General Abacha is a great lost not only to his family, but to the entire nation-because he was a great patriot and a brave general who dedicated himself to the service of his country.

history will always remember general Abacha as a hero who did his best for his country. we pray to Almighty Allah to continue to give the family, friends and well wishers the fortitude to bear the irreplaceable lost.

We also pray that your gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.

Abacha we are still with you in spirit and we love you, but God loves you more.

Thursday, June 4, 2009

HEART BREAK !!!


I've been thru hell
Trying to get you out of my life
But after all this time
I can't help myself but miss you.

Now, all alone
Thinking of my life once again
My past is passing me by
I feel a lot of pains
I shed a lot of tears
As I remember all we’ve been through.

You’re once a dream that came true
An illusion that turned to reality
But suddenly, things turned differently.

You give me sleepless night
Coz you keep staying on my mind
I can’t stop crying
Coz I’m missing you…

My life will never be the same again
Now that you’re gone
I will be trapped in this loneliness forever.

I thought this was a poem I would never have to write
I hope my tongue was something I could bite
But realized it’s just something I cannot do
I’m still so in Love with you, after all this time.

Your heart is now with someone else
I’m so jealous
I can’t bear these bullets anymore
The pain of losing you is still fresh in my brain
Every day my heart feels the pain
Will things ever be same again?...

I want you to know I’m heartbroken
I want you to know I’m hurt
But please….
I don’t want you to look at the tears in my eyes as I cry…

Wednesday, May 20, 2009

TEN YEARS OF CIVILIAN RULE..


Its now exactly ten years since the return of civilian rule in Nigeria, but Nigerians have not witness any development over these years. things are even getting more worst than before: no constant electricity power supply, poor roads,falling standards of education, our hospitals are in critical conditions, economic meltdown, nigerian stock exchange is not looking good and there is a problem of unemployment in the country. this adminstaration is nothing but a set back, becouse one of the so called 7-points agenda have not been actualised.
Yar’adua should as a matter of urgency address these issues once and for all to avoid further escalation of the problem. It is very unfortunate that despite the vast natural resources that God in his infinite mercy endow Nigeria with, the resources are mismanaged by a very few and the masses are left in squalor and poverty. The national cake is being looted and squandered by few out of Whims and Fancies to the detriment of the majority.
Anyway, Nigerians, happy ten years of civilian rule not democracy!

Thursday, May 7, 2009

Jang Vs Fula

FULANI SUMA YAN NIGERIA NE:

Budaddiyar wasika ga gwamna Jonah Jang
zaman lafiya da ci gaban ko wace kasa ko al'umma ya dangana ne ga yadda shugabanninsu ke tafiyar da mulkin su ba tare da nuna banbanci kabila, addini ko siyasa ba. Yin hakane kawai zai kawo ci gaban kasa da kuma al’umma. Hukunci da gwamnatin jihar filato ta dauka na Koran Fulani a jihar wani mataki ne da ka iya tada zaune tsaye, musamman ma ganin yadda jihar tayi kaurin suna kan rikice-rikice kama daga na kabilanci, addini, siyasa da dai sauransu.
Sanin kowa ne dokar kasa taba duk dan kasa damar zama inda yake so ba tare da tsangwama ba. Don haka ya kamata gwamna Jang ya gane cewa fulanin filato na da ‘yancin zama a ko ina cikin kasarnan kamar yadda sauran kabilu ke zaune a jihar ba tare da an takura masu ba. Har yanzu dai matsalar dan kasa da bako bata mutu a filato ba, don kuwa in ba haka ba babu dalilin da za’ace za’a kori fulanin dake filato a halin yanzu. Filato, jihar da ake yi mata take da jihar zaman lafiya, yawon bude ido da shakatawa yanzu ana iya cewa ta koma jihar rashin zaman lafiya sanadiyyar shugabanni marasa kishin ci gabanta da take dasu, sai dai kuma yawon bude ido da shakatawan ko yananan ko babu Allah kadai ya sani.
Ba komai ya kawo wannan gurguwar mataki da gwamna Jang ya dauka na Koran fulanin jihar ba illa rashin daukar kwakkwaran mataki da gwamnatin tarayya takiyi kan shi gwamnan bisa rikicin da ya faru na baya bayan nan a jihar inda aka rasa dimbin rayuka, wanda hakan shi ya sake ba gwamnan karfin guiwar kawo wata sabuwar salon da ka iya haifar da rudani a jihar da ma kasa baki daya. Alal hakika, tilastawa Fulani barin filato wani babban lamari ne da ka iya haifar da komai matuka mahukuntan da abin ya shafa basu sa baki ba. Abin bakin cikine yadda gwamnatin tarayya tayi bakan taki cewa uffan kan wannan lamari wanda barazana ne ga zaman lafiya ta fanin tsaro. Wai ma abin tambaya shine; me yasa irin wadanan matsaloli basa faruwa a sauran jihohin kasar nan sai jihar filato kawai? Shin itace kadai jihar da take da kabilu masu dimbin yawa? Tabbas akwai bukatar shugaba yar’adua ya dauki matakan ladabtar da gwamna Jang don ganin bai wuce makadi da rawa ba in har ya dage kan wannan danyen mataki da ya dauka na korar Fulani, domin babu wanda ya fi karfin doka, kuma duk wanda ya nemi yin karan tsaye ga dokokin kasa, la shakka yana bukatar ladabtarwa don ya zama darasi ga ‘yan baya.
Lokaci yayi da shugabanni ya kamata su rika mulkin adalci ga al’ummar da suke mulka ba tare da nuna banbancin addini, kabila, siyasa, fifita wasu bisa wasu, ko asali ba, tayin hakane kawai za’a samu zaman lafiya, ci gaba da daurewar shugabanci na gari.
Alal hakika, akwai bukatar gwamnatin tarayya ta gaggauta daukan mataki kan wannan kazamin aiki da gwamna Jang keson aikatawa don dakile duk wata hargitsi daka iya kunno kai don samun zaman lafiya a jihar da ma kasa baki daya. Watan wata rana kowa zaiyi bayanin yadda ya tafiyar da shugabancin talakawansa a gaban mai duka, don haka kalu balen ku shugabanni.
Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukanmu na alhairi, amin.