Duk dan adam yana da bukatan abubuwan more rayuwa na yau da kullum kamar su wutan lantarki, hanyoyin sufuri masu nagarta,da dai sauransu.amman saidai a yau akasin hakan ake samu. Koda yake, wasu ma ana iya cewa sun zama dole yin amfani dasu. Misali, koda yake ruwa ba’a ce dashi abin more rayuwa ba, amman dukkan mai numfashi na bukatansa a kulli yaumin domin sha, girki da kuma sauran ayyukan yau da kullum
Kash! Saidai labarin a birnin zariya ba haka yake ba. Domin kuwa ruwa ya zama dan gwal. Saboda a yau duk wanda yazo garin zariya daga wata garin, to babu abinda da zasu fara yi masa maraba face ‘yan garuwa. Wadanda suke sayar da ruwan nasu da dan karan tsada, kuma gashi wasu daga cikinsu ruwan nasau bawai yana da kyau bane. Wanda idan hakan ta adaure, to nan gaba ba’a san abinda zai haifarba.
Koda yake wannan matsala na rashin ruwa a birnin zariya bawai sabon lamari bane, saidai kawai yadda rashin nasa yake dada tabarbarewa. Na tabbata duk yaron da ke zariya a yau, wanda shekarunsa basu wuce shabiyar zuwa sha bakwaiba, wallahi bai taba ganin ankawo ruwan famfo a gidansu ba. Wannan matsala kuwa ta wuce duk iya tunanin mutane, domin kuwa kamar yadda nace ne tun farko, al’amarin yana neman wuce gona da iri. Abin ban takaici ne yadda a yau yara kanana cikin dare suke fita ko kuma da subahin fari da sunan suna zuwa neman ruwan da iyayensu zasu yi masu abinci. Wanda hakan kan iya sa yaran shiga wani halin da bai dace ba.
A kwai bukatan hukumomi ko gwamnati data shiga cikin wannan lamari don kawo saukinsa ga al’ummar da suke yiwa shugabanci. Koda yake, mai girma gwamnan kaduna alhaji namadi sambo, ya samar da famfuna masu aiki da hasken rana wadanda zasu iya aiki daga safe har zuwa la’asar ko ace yamma. Saidai labarin ba haka yake ba, domin kuwa famfunan sun zama abin adone kawai a birnin na zariya. Saboda idan famfon yabada ruwa na kamar sa’a uku a rana, to sai yayi kamar mako daya koma fiye da haka bai sake bada ruwa ba duk da cewa da hasken rana yake aiki bada wutan lantarki ba. Wani abin ban haushi ma shine yadda manya da kanan yara ke dambe a wajen diban ruwan, wanda hakan kai haifair da jin raunuka da dama gasu yaran. Koda yake yin damben nasu nada dalili, domin wani bokitinsa takan kwana biyu ko uku a layi, amman lokaci daya wanda yafisu son zuciya sai yazo yace sai ya diba kafin su, wani lokaci kuma sukan tashi a tutan ma’aho.
Don haka ya kamata gwamnatin jihar kaduna data karamar hukumar zariya suyi hubbasa wajen magance wannan fitina data addabi jama’ar nasu, ganin cewa ma yana daya daga cikin alkawuran da suka daukan masu yayin yakin neman zabe. Saboda wanna ruwa da ‘yan garuwa ke sayarwa, mafi yawancinsu bamasu kyau bane, kuma shan irin wadannan ruwan na iya haifar da barkewar wata cuta.
Ya kamata mai girma gwamna alhaji namadi sambo, ya sake duba wadan nan famfuna da aka kafa masu aiki da hasken rana don su rika aiki yadda ya kamata, don kada yazamana anyisu amman babu amfani ganin cewa kudin al’umma aka dauka akayi aikin dashi, don haka yaka mata suga amfanin yin aikin da dukiyarsu.
Amma daga karshe inason fa a fahimceni, bawai ina kashema ma ‘yan garuwa kasuwa ne, a’a gaskiyar lamarine nake fadi, kuma a baya ma nace bawai dukkansu ne ke da ruwa mara kyau ba.
Allah shiyi mana jagora a dukkan ayyukanmu na alhairi amin.
THIS IS THE SITE OF MR.MUNTAKA ABDUL-HADI DABO,WHICH INCLUDES MY HISTORICAL BACKGROUND, SOME OF MY WRITE-UPS THAT ARE PUBLISHED IN THE NATIONAL DAILIES OF NIGERIA AND LOTS MORE...
Saturday, March 22, 2008
Monday, January 7, 2008
सियासर AFURKA
A kullum akatashi yin Magana akan mulkin dimokradiyyar nahiyar afurka sai ace da ita jaririya. To wai yaushe ne zata girma? Ma’ana ta tashi daga jaririya zuwa mai hankali.
Alal hakika a nahiyar afurka anyi mummunar fahimtar abinda ake nufi da dimokradiyya. Koda yake bakomai ya haifar da haka ba illa rashin akidar kasa daya al’umma daya. Mafi yawancin yan siyasan yanzu sunfi maida hankali ne kan addini ko kabila kafin su nunawa duk wani mai neman madafun iko goyan baya. Wani abin muni ma shine yadda a nahiyar afurka aka maida mulkin dimokaraddiya gado. Saikaga dama kasauka, inma kasauka kana iya zaba ma al’ummar kasan wandan zai gajeka mai maikonsu su zabi wanda sukeso.
Koda yake, ina ganin katsalandan din da kasashen turawa sukeyi ga nahiyar afurka na daya daga cikin abubuwan dake haifar da rudani a nahiyar musamman ma dai ‘yar sandan duniya wato kasar amurka. Alal misali idan muka dauki kasar Kenya, wanda akema kallon uwa mabada mama akan sha’anin mulkin dimokradiyya amman a halin yanzu rikicin zaben da yasake ba shugaba Mwai KIBAKI wani wa’adin mulki ya dabaibayeta, zamu ga cewa mafi yawancin kasashen afurka basu amince da zabenba, amman kasar amurka itace kasa ta farko da ta taya shugaba KIBAKI murnan wai samun nasara da yayi, amma kuma daga baya tazo tace ta janye wannan taya murna data yiwa shi KIBAKI saboda annami manci irin na amurka.
Koda yake, ganin yadda al’amura ke sake yamutsewa a kasar ta Kenya, shugaba KIBAKI yasha alwashin gudanar da sabon zaben amman fa in har kotun kasar taki amincewa da sakamakon zaben, kamardai yadda tun farko abokin adawar nasa Raila Odinga ya bukaci da ayi. Amma ana iya cewa wannan furuci na KIBAKI zancen banzane domin kuwa shi yake da iko da kotunar kasar nasa, kuma zai iya tube duk alkalin da baiyi masa yadda yake so ba. Kamar dai yadda takwaransa na Pakistan yakeyi.
Idan muka duba nijeriya kuwa, wanda itama tayi fama da nata rikicin zaben shekarar da ta wuce, zamuga cewa duk kanwar jane. Domin kuwa duk da korafe korafen da masu sa ido na kasa da kasa sukayi cewa zaben na cike da magudi, amurka ita tafara taya mista yar’adua murna kan wai nasaran daya samu. Kai bada dadewa ba bayan kama madafun iko (mista yar’adua) aka gayyace shi taron G8, kana yakai ziyara kasashe da dama.
A kwanakin baya ne mista yar’adua yaki amincewa da sojojin hadin guiwan amurka wato AFRICOM amma nanda nan suka gayyaceshi zuwa kasar ta amurka inda suka kwaba masa kana ya amince. Aman bayan yadawo gida sai yayi amai ya lashe, domin kuwa yace waishi bai amince da bukatun na amurka ba.
Tabbas idan nahiyar afurka sukace wai komai kasashen yammaci dana turai ne zasu rika yanke masu iko, musaman ma kan batun zabubbuka domin duk sanda wata daga cikin kasashen yammaci turai musamman ma amurka tace ta amince da yadda akayi zabe, sai suma al’umman kasar su amince wai don kada a samasu takunkumi, to lashakka suna cikin mummunar tsaka mai wuya wanda kafin su fice daga cikinta sai sunyi da gaske.
Idan muka dubi kasar Pakistan kuwa, zamu ga cewa har ila yau ita dai wannan la’antacciyar kasar ne wato amurka ke daurewa shuga pervez musharraf gindi yake cin karesa ba babbaka. Domin kuwa ko kadan amurka batayi allah wadai da kisan gillar da akayi wa tsohuwar fira ministan kasar kuma shugaban adawa madam Bhutto ba, saboda shi shugaba musharraf yaron tane (amurka). Wani abin ban haushi shine yadda ita amurkan ke ikirarin yaki da ta’addanci,kuma shirye take ta taimakawa duk wata kasa dake da shirin yaki da ta’addancin. Amman sai gashi labarin yasha banban, domin kuwa wadanda suka kasha madam Bhutto sanannune, kuma ansan da zaman wadanda sukayi. Saidai kawai aki yin adalci wajen fidda sakamakon kwamintin dake bincike akan kisan.
To wai abin tambaya a nan shine, yaushe al’ummar nahiyar afurka zasu farka gada barcin da sukeyi ne don su san cewa fa kasashen nahiyar turai ba komai suke tsinana masu ba illa rigingimu da tashe tashen hankula. Kana basa basu wata gudunmuwar alheri sai dai idanfa sunga zasu ci riba da abinda suke basu. Yaka mata ga duk kasashen dake nahiyar afurka su game kansu wuri guda suyi bori ga wannan sansani da amurka keso ta kafa na AFRICOM a nahiyar. Tabbas, duk kasar da tabari akayi mata wannan sansanin, to saidai muce allah yakaresu daga sharrin amurka. Domin kuwa watarana za’ace suna da makamin kare dangi kamar yadda sukace wai kasar iraq nada shi, amman harsuka gama yakinsu da kasar koda makami daya na kare dangin da sukayi ikirarin iraq na dashi basu nunawa duniya ba.
Allah ya taimaki nahiyar afurka, yakuam hade kawunan shugabanin ta baki daya.
Alal hakika a nahiyar afurka anyi mummunar fahimtar abinda ake nufi da dimokradiyya. Koda yake bakomai ya haifar da haka ba illa rashin akidar kasa daya al’umma daya. Mafi yawancin yan siyasan yanzu sunfi maida hankali ne kan addini ko kabila kafin su nunawa duk wani mai neman madafun iko goyan baya. Wani abin muni ma shine yadda a nahiyar afurka aka maida mulkin dimokaraddiya gado. Saikaga dama kasauka, inma kasauka kana iya zaba ma al’ummar kasan wandan zai gajeka mai maikonsu su zabi wanda sukeso.
Koda yake, ina ganin katsalandan din da kasashen turawa sukeyi ga nahiyar afurka na daya daga cikin abubuwan dake haifar da rudani a nahiyar musamman ma dai ‘yar sandan duniya wato kasar amurka. Alal misali idan muka dauki kasar Kenya, wanda akema kallon uwa mabada mama akan sha’anin mulkin dimokradiyya amman a halin yanzu rikicin zaben da yasake ba shugaba Mwai KIBAKI wani wa’adin mulki ya dabaibayeta, zamu ga cewa mafi yawancin kasashen afurka basu amince da zabenba, amman kasar amurka itace kasa ta farko da ta taya shugaba KIBAKI murnan wai samun nasara da yayi, amma kuma daga baya tazo tace ta janye wannan taya murna data yiwa shi KIBAKI saboda annami manci irin na amurka.
Koda yake, ganin yadda al’amura ke sake yamutsewa a kasar ta Kenya, shugaba KIBAKI yasha alwashin gudanar da sabon zaben amman fa in har kotun kasar taki amincewa da sakamakon zaben, kamardai yadda tun farko abokin adawar nasa Raila Odinga ya bukaci da ayi. Amma ana iya cewa wannan furuci na KIBAKI zancen banzane domin kuwa shi yake da iko da kotunar kasar nasa, kuma zai iya tube duk alkalin da baiyi masa yadda yake so ba. Kamar dai yadda takwaransa na Pakistan yakeyi.
Idan muka duba nijeriya kuwa, wanda itama tayi fama da nata rikicin zaben shekarar da ta wuce, zamuga cewa duk kanwar jane. Domin kuwa duk da korafe korafen da masu sa ido na kasa da kasa sukayi cewa zaben na cike da magudi, amurka ita tafara taya mista yar’adua murna kan wai nasaran daya samu. Kai bada dadewa ba bayan kama madafun iko (mista yar’adua) aka gayyace shi taron G8, kana yakai ziyara kasashe da dama.
A kwanakin baya ne mista yar’adua yaki amincewa da sojojin hadin guiwan amurka wato AFRICOM amma nanda nan suka gayyaceshi zuwa kasar ta amurka inda suka kwaba masa kana ya amince. Aman bayan yadawo gida sai yayi amai ya lashe, domin kuwa yace waishi bai amince da bukatun na amurka ba.
Tabbas idan nahiyar afurka sukace wai komai kasashen yammaci dana turai ne zasu rika yanke masu iko, musaman ma kan batun zabubbuka domin duk sanda wata daga cikin kasashen yammaci turai musamman ma amurka tace ta amince da yadda akayi zabe, sai suma al’umman kasar su amince wai don kada a samasu takunkumi, to lashakka suna cikin mummunar tsaka mai wuya wanda kafin su fice daga cikinta sai sunyi da gaske.
Idan muka dubi kasar Pakistan kuwa, zamu ga cewa har ila yau ita dai wannan la’antacciyar kasar ne wato amurka ke daurewa shuga pervez musharraf gindi yake cin karesa ba babbaka. Domin kuwa ko kadan amurka batayi allah wadai da kisan gillar da akayi wa tsohuwar fira ministan kasar kuma shugaban adawa madam Bhutto ba, saboda shi shugaba musharraf yaron tane (amurka). Wani abin ban haushi shine yadda ita amurkan ke ikirarin yaki da ta’addanci,kuma shirye take ta taimakawa duk wata kasa dake da shirin yaki da ta’addancin. Amman sai gashi labarin yasha banban, domin kuwa wadanda suka kasha madam Bhutto sanannune, kuma ansan da zaman wadanda sukayi. Saidai kawai aki yin adalci wajen fidda sakamakon kwamintin dake bincike akan kisan.
To wai abin tambaya a nan shine, yaushe al’ummar nahiyar afurka zasu farka gada barcin da sukeyi ne don su san cewa fa kasashen nahiyar turai ba komai suke tsinana masu ba illa rigingimu da tashe tashen hankula. Kana basa basu wata gudunmuwar alheri sai dai idanfa sunga zasu ci riba da abinda suke basu. Yaka mata ga duk kasashen dake nahiyar afurka su game kansu wuri guda suyi bori ga wannan sansani da amurka keso ta kafa na AFRICOM a nahiyar. Tabbas, duk kasar da tabari akayi mata wannan sansanin, to saidai muce allah yakaresu daga sharrin amurka. Domin kuwa watarana za’ace suna da makamin kare dangi kamar yadda sukace wai kasar iraq nada shi, amman harsuka gama yakinsu da kasar koda makami daya na kare dangin da sukayi ikirarin iraq na dashi basu nunawa duniya ba.
Allah ya taimaki nahiyar afurka, yakuam hade kawunan shugabanin ta baki daya.
Thursday, December 13, 2007
TRIBUTE TO A MAN OF PEOPLE
Chief Sunday Awoniyi,has been called to glory. That is ordinary of human lives. The death of awoniyi is a great lost not only to the family,but to the entire nation. Yes! To the entire nation because he was a great patriot who dedicated himself to the service of humanity.
While he lived, awoniyi was a cool-headed unassuming person who gave everybody his due respect. A philanthropist, a man who stand for justice, fair play and equity.he was a lover of mankind. Awoniyi was complete gentleman,trustworthy and honest to the core. The family, indeed the nation has lost a very good man. The family,friends and well wishers he has left behind will fell the vacuum he has left.
But we all know that what Almighty God has destined we cannot change but we leave it to him to take care of his soul.His departrure no doubt will show the gap he must have left behind.
We pray to Almighty God to give the family,friends and well wishers the fortitude to bear the irreplaceable lost.
While he lived, awoniyi was a cool-headed unassuming person who gave everybody his due respect. A philanthropist, a man who stand for justice, fair play and equity.he was a lover of mankind. Awoniyi was complete gentleman,trustworthy and honest to the core. The family, indeed the nation has lost a very good man. The family,friends and well wishers he has left behind will fell the vacuum he has left.
But we all know that what Almighty God has destined we cannot change but we leave it to him to take care of his soul.His departrure no doubt will show the gap he must have left behind.
We pray to Almighty God to give the family,friends and well wishers the fortitude to bear the irreplaceable lost.
Saturday, October 27, 2007
JAMIYYUN
Ana iya cewa dai a yau jam’iyyun adawa sun zama ‘yan abi yarima asha kida. Mai makon su rika tsayawa da kafafun su, a’a si suka maida hankali wajen ganin sun azurta kawunansu da kuma shiga cikin gwamnatin maici suyi dumu-dumu a cikinta. Koda yake shigan ‘yan adawa cikin gwamnati mai mulki ba laifi bane, in hardai zasu kare mutuncin adawar da sukeyi da kuma gabatar da ayyukan raya kasa ga ita gwamnatin don ta aiwatar dasu.
Kodayake, adaw ba gaba bane. Adawa dai a dimokradiyyance na nufin bangare ne na jam’iyyun siyasa wanda basu ke mulki ba, amma masu akidar ganin anyi aikin gina kasa da kumka baiwa kowa hakkinsa a matsayinsa na dankasa yadda ya kamata.
Saidai wani abin ban mamaki shine, mafi yawancin jam’iyyun adaw a nahiyarmu ta afrika sukan manta da hakkokin da ya rataya a kansu da zaran sun shiga cikin gwamnatin dake mulki. Wanda hakan baya hiafar masu dad a mai ido illa zubar masu da kima, mutunci da daraja a idon talakawansu. Alal hakika akwai ka’idoji da dama dasu ‘yan adawa ya kamata su kiyaye dasu kamar;
1) tsayawa a kan matsayin su na ‘yan adawa don ganin gwamnati tayi aikin raya kasa daba talakawa hakkokinsu.
2) Gabatar da akidojinsu ko manufofinsu ga gwamnati domin ta aiwatar dasu don asami kyakkyawar mulkin dimokradiyya.
3) Yin suka mai ma’ana a duk lokacin da gwamnati tayi ba daidai ba, da kuma yaba mata yayin da tayi aikin cigaban talakawanta.
4) Ba gwamnati shawar wari masu ma’ana na yadda za’a samu ci gaba ba yadda su ‘yan adawan zasu ci gaba ba.
5) Su guji saurin bayyana kwadayinsu ga gwamnati don samun mukaman siyasa.
Tabbas, idan ‘yan adawa suka kiyaye da wadannan ka’idoji, to lashakka darajarsu, kima da kuma mutuncinsu zai daukaka ga ita knta gwamnati da kuma talakawar da suke wakilta.
Wani abin ban haushi shine, kowace jam’iyya nada nata kundin tsarin zabe, amma da zarar zaben ya wuce sai ayi watsi da wannan kundin a kuma mai dashi tabarmar takawa, wanda haka bai daceba kuma ya saba ma tsarin mulki.
To abin tambaya a nan shine, wai taya yane ya kamata su ‘yan adawa zasu kare kimarsu da martabarsu a idon talakwarsu ba tare dasu talakawan na masu ganin ‘yan kalen yarima ba? Musamman ma ganin yadda harkan siyasa da adawa ke tafiya a nahiyar mu ta afrika. To amsar dai bata mai tsawo bane. Ya kamata su ‘yan adawa su san cewafa, ko shunshiga cikin gwamnati mai mulki, sun shigane don cigaban dimokradiyya ban don azurta kawunansu ba, sabanin yadda zakaga wasu sunshiga sun manta da al’umman su sai cin karensu kawai sukeyi ba ko babbaka . Har ila yau su kwana da sanin cewa basu da ‘yancin daukan duk wani mataki ba tare da sun tuntubi wadanda suke wakilta ba, kana kada su rika nuna maitan su ko kwadayi a fili na ganin sun sami kudi ta ko wani hali. Illa kawai su maida hankali ganin sun nuna ma gwamnati ayyukan da talakawa ke bukata ayi masu, kuma su tsaya kai da fata na ganin an aiwatar da wadannan ayyukan. Ina ganin idan sukayi haka, to shakka babu zasu kare mutuncin su da kimarsu. Dafatan allah ya taimaki shuganin mu su samu sukunin sauke nauyin da ya hau kawunansu, kana suyi wa talakawansu ayyukan ci gaba da raya kasa.wassalam
MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
Write2muntaka@yahoo.co.uk
0803-639-7682
0802-636-8492
Kodayake, adaw ba gaba bane. Adawa dai a dimokradiyyance na nufin bangare ne na jam’iyyun siyasa wanda basu ke mulki ba, amma masu akidar ganin anyi aikin gina kasa da kumka baiwa kowa hakkinsa a matsayinsa na dankasa yadda ya kamata.
Saidai wani abin ban mamaki shine, mafi yawancin jam’iyyun adaw a nahiyarmu ta afrika sukan manta da hakkokin da ya rataya a kansu da zaran sun shiga cikin gwamnatin dake mulki. Wanda hakan baya hiafar masu dad a mai ido illa zubar masu da kima, mutunci da daraja a idon talakawansu. Alal hakika akwai ka’idoji da dama dasu ‘yan adawa ya kamata su kiyaye dasu kamar;
1) tsayawa a kan matsayin su na ‘yan adawa don ganin gwamnati tayi aikin raya kasa daba talakawa hakkokinsu.
2) Gabatar da akidojinsu ko manufofinsu ga gwamnati domin ta aiwatar dasu don asami kyakkyawar mulkin dimokradiyya.
3) Yin suka mai ma’ana a duk lokacin da gwamnati tayi ba daidai ba, da kuma yaba mata yayin da tayi aikin cigaban talakawanta.
4) Ba gwamnati shawar wari masu ma’ana na yadda za’a samu ci gaba ba yadda su ‘yan adawan zasu ci gaba ba.
5) Su guji saurin bayyana kwadayinsu ga gwamnati don samun mukaman siyasa.
Tabbas, idan ‘yan adawa suka kiyaye da wadannan ka’idoji, to lashakka darajarsu, kima da kuma mutuncinsu zai daukaka ga ita knta gwamnati da kuma talakawar da suke wakilta.
Wani abin ban haushi shine, kowace jam’iyya nada nata kundin tsarin zabe, amma da zarar zaben ya wuce sai ayi watsi da wannan kundin a kuma mai dashi tabarmar takawa, wanda haka bai daceba kuma ya saba ma tsarin mulki.
To abin tambaya a nan shine, wai taya yane ya kamata su ‘yan adawa zasu kare kimarsu da martabarsu a idon talakwarsu ba tare dasu talakawan na masu ganin ‘yan kalen yarima ba? Musamman ma ganin yadda harkan siyasa da adawa ke tafiya a nahiyar mu ta afrika. To amsar dai bata mai tsawo bane. Ya kamata su ‘yan adawa su san cewafa, ko shunshiga cikin gwamnati mai mulki, sun shigane don cigaban dimokradiyya ban don azurta kawunansu ba, sabanin yadda zakaga wasu sunshiga sun manta da al’umman su sai cin karensu kawai sukeyi ba ko babbaka . Har ila yau su kwana da sanin cewa basu da ‘yancin daukan duk wani mataki ba tare da sun tuntubi wadanda suke wakilta ba, kana kada su rika nuna maitan su ko kwadayi a fili na ganin sun sami kudi ta ko wani hali. Illa kawai su maida hankali ganin sun nuna ma gwamnati ayyukan da talakawa ke bukata ayi masu, kuma su tsaya kai da fata na ganin an aiwatar da wadannan ayyukan. Ina ganin idan sukayi haka, to shakka babu zasu kare mutuncin su da kimarsu. Dafatan allah ya taimaki shuganin mu su samu sukunin sauke nauyin da ya hau kawunansu, kana suyi wa talakawansu ayyukan ci gaba da raya kasa.wassalam
MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
Write2muntaka@yahoo.co.uk
0803-639-7682
0802-636-8492
MUTUWAR
MUTUWAR AURE: LAIFIN MAZA KO MATA?
Masu karatu assalamu alaikum, gaisuwa da fatan kuna cikin koshin lafiya. Yau kuma gamu tafe acikin wanna fili mai tarin albarka, inda za muyi maganan akan yawan mutuwar aure.
Kamar dai yadda akasani ne, aure zamane na zamantakewa, tarayya kana kuma a iya cewa zamane na hakuri tsakanin ma’aurata. Akwai matsaloli da dama da kan taso a tsakanin su ma’auratan a cikin harkokinsu na yau da kullum, wanda a wasu lokuta idan ba ankai hankali nesaba ko kuma anyi hakuri da junaba, sai kaga saki (wato rabuwa) ne sakamakon da zai biyo baya.
To wai me yakesa su mazajen daukan irin wannan mataki nayin saki da gaggawa duk dacewa ya halatta a addinance? Kuma shin laifin wanene a tsakanin su mazan da matan?
Akandai bar ginine tun ranar zane, domin kuwa wasu mazajen suke bata lamarin tun lokacin da suke neman yarinyar da aure. Wadansun su idan sunje zance, maimakon su gayawa yarinyar gaskiya game dasu, a’a saidai su dauki duk karyan duniya su gaya masu, suce iyayensu ne wane da wane, yana da gidaje kaza, motoci kaza, dadai sauransu, itakuma dama yarinyar idan mai halin shazumamine sai tace ai inbashi ba sai rijiya. Har ila yau bayan karerayi da maza keyi wajen neman aure don ganin sun sami matan da sukeso, akwai kuma lallaba budurwa da sukeyi su maida ita yar lele duk abinda tace shine za’ayi.
Saidai abinda yake biyo bayan irin wadannan karerayi shine rabuwa. Domin kuwa da zaran anyi auren idan yarinyar bata ga abubuwan da aka rika zayyanamata a bayaba, sai rigin gimu iri iri su taso. Haka kuma irin daman da ake bata kafin auren duk zasu kau, domin kuwa dazaran sun shiga gidajen mazajen nasu, to saifa yadda akayi dasu don kuwa yanzu wuka da nama na hannun mai gidane. A takaice, ana iya cewa wasu mazan akwaisu da karya, yaudara da kuma wulakanci, wanda hakan na iya haifar da sanadiyyar karewan aure.
Idan muka duba bangaren mata kuwa, zamu ga cewa suma suna da nasu irin laifin. Misali, wasu matan zakaga kwalliya ma basu iya ba don jan ra’ayin mazajen nasu a duk lokacin da suke gida. Basu iya amfani da lafuzza masu sanyaya zucciyar namija ba. Uwa uba shine ace mace bata iya abinci ba, nan ne yafi ko ina matsala, domin idan wasu matan sukayi ma girki, to wallahi baka iya banbance tsakaninsa da dussa. Sai kuma maganar tsabta, mafi yawancin mata zaka ga tsaftar kansu ma yazama masu aiki balle uwa uba na gida, basa iya wanka don mazajensu su gani suji dadi, saidai idan ance akwai biki ko suan fa ai nan fa zakaga ana wanka har aba uku lada.Har ila yau, wasu basusan yadda zasu kwantarwa da mazajensu rai ba a duk lokacin da wani abu na bacin rai ya samesu.
Har yanzu dai ina kan mata, wasu basu san adawo lafiya ba ko barka da zuwa ga mazajensu, ga rashin godiya ga dukkan abin da mai gida zai kawo. Gayawan dogon buri, ga kallon yawangashin wance. Idan suna shan jan miya kullum ne, to suma fa sai sun sha kullum. To duk irin wadannan abubuwanne a lokuta da dama ke haifar da saki, inda idan aka duba da kyau, za’a iya gane ko waye ke da laifi a tsakanin maza ko mata.
To wai me yakamata ayi ne don shawo kan wadannan matsaloli? To ai bawani abune mai wuya ba, illa dai su maza su sanifa cewa ko wani tsuntsu kukan gidansu ya keyi. Kuma daidai ruwa daidai kurji, har ilayau su sani cewa ramin fa karya kurarriyace (koda yake wasu matan sai an hada masu da kyarya saboda kwadayinsu). Ba’ataba cewa gaskiyar mutun ta kare saidai ace karyansa ta kare. Don haka maza a rika fadin gaskiya a dukkan al’amuran da za’asa a gaba.ku kuma sanifa karya bazata taba haifar da sakamako mai amfani ba.
Ga mata kuwa, a daina rawan ido, kwadayi da son abin duniya. A daina duban mai zuwa a mota da mai zuwa a kasa ko a babur. Banda duban wayafi sa kaya masu tsada. Abinda ya kamat ku duba kawai shine waye zai kare maku mutuncin ku, ya kuma baku hakkinku da dai sauran nauyin da ka iya hawa kansa a matsayinsa na mai gida. Dsa fatan Allah yaci gaba da yimana jagora adukkan ayyukan mu na yau da kullum.wassalam
MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
Write2muntaka@yahoo.co.uk
0803-639-7682, 0802-636-8492
Masu karatu assalamu alaikum, gaisuwa da fatan kuna cikin koshin lafiya. Yau kuma gamu tafe acikin wanna fili mai tarin albarka, inda za muyi maganan akan yawan mutuwar aure.
Kamar dai yadda akasani ne, aure zamane na zamantakewa, tarayya kana kuma a iya cewa zamane na hakuri tsakanin ma’aurata. Akwai matsaloli da dama da kan taso a tsakanin su ma’auratan a cikin harkokinsu na yau da kullum, wanda a wasu lokuta idan ba ankai hankali nesaba ko kuma anyi hakuri da junaba, sai kaga saki (wato rabuwa) ne sakamakon da zai biyo baya.
To wai me yakesa su mazajen daukan irin wannan mataki nayin saki da gaggawa duk dacewa ya halatta a addinance? Kuma shin laifin wanene a tsakanin su mazan da matan?
Akandai bar ginine tun ranar zane, domin kuwa wasu mazajen suke bata lamarin tun lokacin da suke neman yarinyar da aure. Wadansun su idan sunje zance, maimakon su gayawa yarinyar gaskiya game dasu, a’a saidai su dauki duk karyan duniya su gaya masu, suce iyayensu ne wane da wane, yana da gidaje kaza, motoci kaza, dadai sauransu, itakuma dama yarinyar idan mai halin shazumamine sai tace ai inbashi ba sai rijiya. Har ila yau bayan karerayi da maza keyi wajen neman aure don ganin sun sami matan da sukeso, akwai kuma lallaba budurwa da sukeyi su maida ita yar lele duk abinda tace shine za’ayi.
Saidai abinda yake biyo bayan irin wadannan karerayi shine rabuwa. Domin kuwa da zaran anyi auren idan yarinyar bata ga abubuwan da aka rika zayyanamata a bayaba, sai rigin gimu iri iri su taso. Haka kuma irin daman da ake bata kafin auren duk zasu kau, domin kuwa dazaran sun shiga gidajen mazajen nasu, to saifa yadda akayi dasu don kuwa yanzu wuka da nama na hannun mai gidane. A takaice, ana iya cewa wasu mazan akwaisu da karya, yaudara da kuma wulakanci, wanda hakan na iya haifar da sanadiyyar karewan aure.
Idan muka duba bangaren mata kuwa, zamu ga cewa suma suna da nasu irin laifin. Misali, wasu matan zakaga kwalliya ma basu iya ba don jan ra’ayin mazajen nasu a duk lokacin da suke gida. Basu iya amfani da lafuzza masu sanyaya zucciyar namija ba. Uwa uba shine ace mace bata iya abinci ba, nan ne yafi ko ina matsala, domin idan wasu matan sukayi ma girki, to wallahi baka iya banbance tsakaninsa da dussa. Sai kuma maganar tsabta, mafi yawancin mata zaka ga tsaftar kansu ma yazama masu aiki balle uwa uba na gida, basa iya wanka don mazajensu su gani suji dadi, saidai idan ance akwai biki ko suan fa ai nan fa zakaga ana wanka har aba uku lada.Har ila yau, wasu basusan yadda zasu kwantarwa da mazajensu rai ba a duk lokacin da wani abu na bacin rai ya samesu.
Har yanzu dai ina kan mata, wasu basu san adawo lafiya ba ko barka da zuwa ga mazajensu, ga rashin godiya ga dukkan abin da mai gida zai kawo. Gayawan dogon buri, ga kallon yawangashin wance. Idan suna shan jan miya kullum ne, to suma fa sai sun sha kullum. To duk irin wadannan abubuwanne a lokuta da dama ke haifar da saki, inda idan aka duba da kyau, za’a iya gane ko waye ke da laifi a tsakanin maza ko mata.
To wai me yakamata ayi ne don shawo kan wadannan matsaloli? To ai bawani abune mai wuya ba, illa dai su maza su sanifa cewa ko wani tsuntsu kukan gidansu ya keyi. Kuma daidai ruwa daidai kurji, har ilayau su sani cewa ramin fa karya kurarriyace (koda yake wasu matan sai an hada masu da kyarya saboda kwadayinsu). Ba’ataba cewa gaskiyar mutun ta kare saidai ace karyansa ta kare. Don haka maza a rika fadin gaskiya a dukkan al’amuran da za’asa a gaba.ku kuma sanifa karya bazata taba haifar da sakamako mai amfani ba.
Ga mata kuwa, a daina rawan ido, kwadayi da son abin duniya. A daina duban mai zuwa a mota da mai zuwa a kasa ko a babur. Banda duban wayafi sa kaya masu tsada. Abinda ya kamat ku duba kawai shine waye zai kare maku mutuncin ku, ya kuma baku hakkinku da dai sauran nauyin da ka iya hawa kansa a matsayinsa na mai gida. Dsa fatan Allah yaci gaba da yimana jagora adukkan ayyukan mu na yau da kullum.wassalam
MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
Write2muntaka@yahoo.co.uk
0803-639-7682, 0802-636-8492
Tuesday, October 2, 2007
पत्रिकia
Masu iya Magana sukace wai kudi masu gidan rana, kudi na iya hada ka fada da kowa hatta iyayaen ka.wannan kam haka yake. Alal hakika abin kunyan da uwargida patricia olubunmi etteh tayi abin dubawa ne da idon basira. Musamman ma ganin yadda yan nijeriya ke rayuwa kasa da $3, amman sai gashi wai ta dauki zunzurutun kudi wuri na gugar wuri har sama da naira miliyan dari shida don gyaran gidanta kawai dana mataikakinta.
Hausawa sunce, wai idan kaga jariri akan gado to daura shi akayi, kuma za’a iya sauko dashi a duk lokacin da akaso a saukeshi,kuma ba zai taba cewa don meba domin bashi ya daura kanshiba daura shi akayi. Yakamata yan majalisan kasa da sauran wadan da alhakin duba wannan al’amari ya rataya a wuyansu da su zauna suyi tuna ni yadda yakama don ganin sun fitad da kasan nan cikin abin kunya da uwargida patricia to jefa mu ciki na yin almubazaranci da dukiyar jama’a ta hanyar tsigeta. Kwarai kuwa, tsigeta, domin hakane kawai za’a a tabbatar ma da talakawan kasannan cewa gwamnatin, kamar yadda tace, baza ta laminci duk wani dangogin cin hanci da rashawa ba tareda da al mubazzaranci da dukiyar al’umma ba. Tabbas idan akayi haka, yanuna cewa a fili, basani ba sabo, gwamnati bazata dagawa kowaye akasamu da yin irin wadannan laifi kafaba.
Abin ban takaici ma shine, yadda su yan majalisan suke kwashe lokutansu suna cacan baki wani lokacima harda danbe a tsakaninsu a yayin da sukaje yin mahawara akan al’amarin ita uwargida patricia.maimakon su maida hankali suga sunyi abin daya kamacesu, a’a sai su tsaya suna shashanci, wanda kuma hakan na iya nuni ga talakawa cewa suma kamar suna goyon bayan abin da ita shugaban nasu tayi, don inba haka ba kuwa, kamata yayi ace tunni an dauki matakin daya dace akanta.
Wai abin ma tambaya anan shine,shin ina hukumar nan ta EFCC take? Kokuwa tana son tabbatar ma duniya cewa fa ita Karen farautar yan adawane? Don in bahaka ba kuwa me yahana ta gaggauta shiga cikin maganar uwargida patricia? Tabbas wanna kalu bale ne ga ita hukumar hana cin hanci da rashawa da kuma albubazzaranci da dukiyankasa, EFCC.
Ya kamata fa shugabannin mu su sani cewa, ranar gobe kiyama zasu yi bayani dalla-dalla kan yadda suka tafiyar da nauyinmu daya hau kansu. Kada suyi tunan cewa mun mika masu amanarmu ne don kawai su gina kawunansu, a’a saidai don suyi mana aikin cigaba da raya kasa.
Daga karshe, ina mai kira da babbar murya ga yan majalisar wakilai, da kada suyi kasa a gwuiwa, su tabbata sunyi aiki tsakaninsu da allah,kuma su gagauta tsika uwargida paatricia olubunmi etteh. Domin kuwa yin haka shine sakama kon daya dace da ita, don yan baya su dauki darasi.
Hausawa sunce, wai idan kaga jariri akan gado to daura shi akayi, kuma za’a iya sauko dashi a duk lokacin da akaso a saukeshi,kuma ba zai taba cewa don meba domin bashi ya daura kanshiba daura shi akayi. Yakamata yan majalisan kasa da sauran wadan da alhakin duba wannan al’amari ya rataya a wuyansu da su zauna suyi tuna ni yadda yakama don ganin sun fitad da kasan nan cikin abin kunya da uwargida patricia to jefa mu ciki na yin almubazaranci da dukiyar jama’a ta hanyar tsigeta. Kwarai kuwa, tsigeta, domin hakane kawai za’a a tabbatar ma da talakawan kasannan cewa gwamnatin, kamar yadda tace, baza ta laminci duk wani dangogin cin hanci da rashawa ba tareda da al mubazzaranci da dukiyar al’umma ba. Tabbas idan akayi haka, yanuna cewa a fili, basani ba sabo, gwamnati bazata dagawa kowaye akasamu da yin irin wadannan laifi kafaba.
Abin ban takaici ma shine, yadda su yan majalisan suke kwashe lokutansu suna cacan baki wani lokacima harda danbe a tsakaninsu a yayin da sukaje yin mahawara akan al’amarin ita uwargida patricia.maimakon su maida hankali suga sunyi abin daya kamacesu, a’a sai su tsaya suna shashanci, wanda kuma hakan na iya nuni ga talakawa cewa suma kamar suna goyon bayan abin da ita shugaban nasu tayi, don inba haka ba kuwa, kamata yayi ace tunni an dauki matakin daya dace akanta.
Wai abin ma tambaya anan shine,shin ina hukumar nan ta EFCC take? Kokuwa tana son tabbatar ma duniya cewa fa ita Karen farautar yan adawane? Don in bahaka ba kuwa me yahana ta gaggauta shiga cikin maganar uwargida patricia? Tabbas wanna kalu bale ne ga ita hukumar hana cin hanci da rashawa da kuma albubazzaranci da dukiyankasa, EFCC.
Ya kamata fa shugabannin mu su sani cewa, ranar gobe kiyama zasu yi bayani dalla-dalla kan yadda suka tafiyar da nauyinmu daya hau kansu. Kada suyi tunan cewa mun mika masu amanarmu ne don kawai su gina kawunansu, a’a saidai don suyi mana aikin cigaba da raya kasa.
Daga karshe, ina mai kira da babbar murya ga yan majalisar wakilai, da kada suyi kasa a gwuiwa, su tabbata sunyi aiki tsakaninsu da allah,kuma su gagauta tsika uwargida paatricia olubunmi etteh. Domin kuwa yin haka shine sakama kon daya dace da ita, don yan baya su dauki darasi.
Friday, July 6, 2007
HADIN KAN 'YAN ADAWA YANA DA ALFANU A WANNAN GWAMNATIN
A duk lokacin da gwamnati ta nemi hadin kan talakawanta don su bada tasu gudunmuwa kan yadda ya dace a tafiyar da ragamar mulkin su, to lallai babu shakka wannan gwamnatin da alamun zata yi adalci a tsawon wa’adin mulkinta. Alal hakika kiran ‘yan adawa da gwamnatin yar’adua tayi don su zo a hada kai a gina jaririyar dimokradiyyar kasan nan yana da amfani sosai. Domin kuwa, hadin kan na su ‘yan adawa zai dada baiwa gwamnati kwarin guiwa da kuma sukunin gudanar da aikin raya kasa da ci gaba.
Duk da cewa mafi yawancin yan nijeriya dasu ‘yan adawa basu gamsu da yadda aka gudanar da zaben daya gabata ba, inda wasu ma ke danganta gwamnatin da haramtacciyar gwamnati, amma tunda dai gwamnatin ta nuna cewa baza ta iya yin komai ba saida hadin kan yan adawa da kuma goyan bayan yan nijeriya, to alal hakika ta cancanci a bata duk irin goyon bayan da take bukata domin ta sauke nauyin daya rataya a kanta.
Ya kamata ‘yan adawan kasan nan suyi tunani mai zurfi, ganin cewa har yanzu fa al’amuran kasannan basu daidai taba tun bayan da sabuwar gwamnati ta kama aiki a sanadiyyar rashin hadin kan da yan adawa suka ki baiwa gwamnati. Ita kuwa gwamnatin taga cewa saka ‘yan adawan yana da matukar amfani ne a sha’anin mulkin kasanan. Domin kuwa idan mukayi la’akari da wasu kasashen duniya, zamu ga cewa ba’a sakin ma ‘yan adawa mara balle ma suce zasu yi fitasri. Ganin yadda ko dama ba’a basu balle suce zasu tsoma baki akan sha’anin mulkin. Don haka kiran da gwamnatin yar’adua tayi wa yan adawa wani damane garesu na da su zo don a yi aikin raya kasa da ciyar da al’umma, ganin cewa gwamnatin ta dauki kowa na tane ba tare da nuna bamban cin jam’iyya ba ko ra’ayoyi.
Tabbas ya kamata ‘yan nijeriya da kuma ‘yan adawa su fahimci manufar wannan gwamnati na yar’adua, ganin yadda take kokarin hada kan yankasa don a samar da dimokradiyya mai adalci, sabanin gwamnatin da ta shude. Idan akayi la’akari da cewa yau sama da wata daya kenan da wannan gwamnatin ta kama mulki, amma har yau bata da ministoci da masu bada shawara duk ta sanadiyyar rashin samun goyan bayan ‘yan adawa. Koda yake, bawai hakan na nufin baza a nada ministocin da masu bada shawaran bane, amma ana son a nuna wa ‘yan adawa cewa shigarsu cikin wannan gwmnatin yana da matukar muhimmanci.
Kamata yayi a manta da koma me ya faru a baya, a zo a hada kai don ganin nijeriya ta ci gaba ta fannoni daban, tunda dai ita gwamnati ta nuna a fili cewa a shirye take da ta yi aiki tare da ‘yan adawa ganin cewa suma zasu iya bada tasu gudunmuwa don cigaban kasan nan. Don haka ‘yan adawa ya kamata su dangana komai ga mahalicci Allah, su amsa kiran wannan gwamnatin don kasar nan tamu tasami ci gaba mai ma’ana.
Daga karshe, zanso in jawo hankalin ‘yan nijeriya cewa, batanci da tozarta shugabannin mu bashi zaisa su canja haleyensu ba, addu’a ya kamata mu rika yi masu ko allah yasa su sauya halayen nasu zuwa yadda ya kamata. Tabbas wannan shine hanyar da ya dace mubi in har bamu gamsu da shugabancin shuwagabannin namu ba.wassalam
Duk da cewa mafi yawancin yan nijeriya dasu ‘yan adawa basu gamsu da yadda aka gudanar da zaben daya gabata ba, inda wasu ma ke danganta gwamnatin da haramtacciyar gwamnati, amma tunda dai gwamnatin ta nuna cewa baza ta iya yin komai ba saida hadin kan yan adawa da kuma goyan bayan yan nijeriya, to alal hakika ta cancanci a bata duk irin goyon bayan da take bukata domin ta sauke nauyin daya rataya a kanta.
Ya kamata ‘yan adawan kasan nan suyi tunani mai zurfi, ganin cewa har yanzu fa al’amuran kasannan basu daidai taba tun bayan da sabuwar gwamnati ta kama aiki a sanadiyyar rashin hadin kan da yan adawa suka ki baiwa gwamnati. Ita kuwa gwamnatin taga cewa saka ‘yan adawan yana da matukar amfani ne a sha’anin mulkin kasanan. Domin kuwa idan mukayi la’akari da wasu kasashen duniya, zamu ga cewa ba’a sakin ma ‘yan adawa mara balle ma suce zasu yi fitasri. Ganin yadda ko dama ba’a basu balle suce zasu tsoma baki akan sha’anin mulkin. Don haka kiran da gwamnatin yar’adua tayi wa yan adawa wani damane garesu na da su zo don a yi aikin raya kasa da ciyar da al’umma, ganin cewa gwamnatin ta dauki kowa na tane ba tare da nuna bamban cin jam’iyya ba ko ra’ayoyi.
Tabbas ya kamata ‘yan nijeriya da kuma ‘yan adawa su fahimci manufar wannan gwamnati na yar’adua, ganin yadda take kokarin hada kan yankasa don a samar da dimokradiyya mai adalci, sabanin gwamnatin da ta shude. Idan akayi la’akari da cewa yau sama da wata daya kenan da wannan gwamnatin ta kama mulki, amma har yau bata da ministoci da masu bada shawara duk ta sanadiyyar rashin samun goyan bayan ‘yan adawa. Koda yake, bawai hakan na nufin baza a nada ministocin da masu bada shawaran bane, amma ana son a nuna wa ‘yan adawa cewa shigarsu cikin wannan gwmnatin yana da matukar muhimmanci.
Kamata yayi a manta da koma me ya faru a baya, a zo a hada kai don ganin nijeriya ta ci gaba ta fannoni daban, tunda dai ita gwamnati ta nuna a fili cewa a shirye take da ta yi aiki tare da ‘yan adawa ganin cewa suma zasu iya bada tasu gudunmuwa don cigaban kasan nan. Don haka ‘yan adawa ya kamata su dangana komai ga mahalicci Allah, su amsa kiran wannan gwamnatin don kasar nan tamu tasami ci gaba mai ma’ana.
Daga karshe, zanso in jawo hankalin ‘yan nijeriya cewa, batanci da tozarta shugabannin mu bashi zaisa su canja haleyensu ba, addu’a ya kamata mu rika yi masu ko allah yasa su sauya halayen nasu zuwa yadda ya kamata. Tabbas wannan shine hanyar da ya dace mubi in har bamu gamsu da shugabancin shuwagabannin namu ba.wassalam
MATASA MANYAN GOBE
Matasa akace manyan gobe, kuma tushen cigaban kowace al’umma. Hakika wannan zancen haka yake, domin kuwa suna da babbar rawar dasuke takawa wajen tafiyar da harkokin yau da kullum. Saidai wani babbar matsala dake tare dasu shine rashin nuna halin ko inkula da gwamnati keyi masu. Rashin sanin muhimmancin matasan yasa haka ko kuwa rashin sanin su wanene matasa? To yadai kamata kowa yasan cewa matasa sune manyan gobe kamar yadda aka sani, kuma suna da babbar gudun muwa da zasu iya bayarwa wajen aikin raya kasa. Shin menene kalmar masata take nufi? Kan wanene hakkin matasa ya rataya? Menene kalmar manyan gobe take nufi, kamar dai yadda akance matasa manyan gobe? Wani irin kalu balene yake gaban su matasan? Menene zai iya faruwa kan irin rikon sakainar kashi da akeyiwa su matasan?
Ita dai kalmar matasa na nufin samari ne wadanda shekarunsu ya fara daga 18-25, kokuma daga 18-30 kamar yadda wadansu suke gani, yakuma ma danganta ne da yadda kowa yake ganin lokacin da yakamata a kira mutum a matashi, wato daga shekara 18 zuwa yadda yasamu. Idan kuma muka duba shin kowane ne hakkin matasa ya rataya akansa, zamu ga cewa hakkin nasu bawai ya rataya akan gwamnati bane kawai, harma da iyaye da sauran al’umma, koda yake ana iya cewa gwamnati ita keda babbar hakki. Abinda gwanmati yaka mata tayi wa matasa shine, samar da ilimi bai daya garesu, tsaro, kula da lafiyan su, sai uwa uba aikin yi domin kuwa wannan hakkine wanda ya rataya akanta. Sukuwa iyaye da sauran al’umma, hakkin sune suga cewa sunba matasa tarbiyya mai kyau, kuma sun basu horon daya dace dasu wajen tafiyar da ayyukansu na yau da kullum. Domin kuwa duk wata al’umma da take son cigaba, sai tabayar da cikakkiyar kulawa ga matasanta da basu kyakkyawar horon daya dace dasu don zama wakilansu na gari bana banza ba a duk inda suka shiga.
Allah sarki! Bahaushe yace wai matasa manyan gobe, kuma ko shakka babu wannan Magana haka take, kamar yadda nace a baya. Domin dai ita kalmar manyan gobe na nufin matasa ne zasu amshi tafiyar da ragamar mulki a duk lokacin da wadanda suke mulkin a yau suka tsufa ko wa adin barin aikin su yayi. Saidai labarin a kasar nan tamu tasha bamban. Domin kuwa, idan aka duba tun daga matakin kananan hukumomi har izuwa ta gwamnatin tarayya, za’a ga cewa duk wadan da shekarun su yafara daga 45-60 koma fiye da haka sune a madafin iko. Ba za’a ga matasa wadanda shekarunsu ya fara daga 25-40 ba, duk dacewa suna da babbar gudun muwar da zasu iya bayarwa wajen ci gaban kasannan.
Matasa a yau sun zama kashin bayan ci gaban kowace al’umma, batare da la’akari da muhimmancin su a cikin al’umma ba, dakuma rawar da zasu taka ta fannin gina kasa. Hakika wannan yaka mata yazama kalu bale gasu matasan don ganin martabarsu ya karbu a ko ina, ta hanyar kaura cema duk wani aikin ash-sha, shaye-shaye da dai suransu, ganin cewa akwai bata gari acikinsu, kuma bahaushe yace wake daya shi ke bata gari. Saboda haka yaza ma wajibi ga matasa da su gyara kansu, sukuma san cewa dabi’ar banza bazata haifar masu da da mai ido ba. Har ila yau kada matasa su yadda su zama ‘yan bangan siyasa, abin nufi anan shine, kada wasu ‘yan tsirarun mutane su rika amfani dasu wajen tada zaune tsaye don kawai cimma burinsu, wanda bayan su wadannan mutane sun samu abin da sukeso basa yiwa su matasan komai illa su watsar dasu. Matasa susan cewa fa su wakilai ne na samar da zaman lafiya ba hargitsi ba a cikin al’umma. Komai na iya faruwa a duk lokacin da aka tauye ma matasa hakkinsu ko akaci gaba da nuna halin ko inkula dangane da rayuwarsu, musamman ma idan babu cikakken tsaro, ilimi, da uwa uba aikinyi da kuma sauran abubuwan more rayuwa wanda yazama hakkine na hukuma ta samara dasu. Rashin wadan nan abubuwa zai iya jefa matasa a tsaka mai wuya, kamar dai sace-sace, yawon banza da sauran aikin ashsha da baza’a rasaba, wanda kuma bama fatan hakan ya faru ga su manyan goben.
Daga karshe, ya kamata gwamnati da sauran hukumomin da abun yashafa da su san cewa fa matasa abin wasa bane a kowace irin al’umma. Musamman ma ganin cewa sune manyan gobe kamr yadda nayi bayani a baya, kuma suna da gudun muwa na cigaba da zasu iya bayarwa. Don haka yana da kyau a rika duba duk wata irin matsaloli dake damunsu, da kuma yin kokarin samar masu da maganinsa. Kana duk wata al’umama ko gwamnati data ga ayukanta na samun cikas ko rashin ci gaba, to ta waiwaya ta dubi matasanta taga yadda al’amuransu yake tafiya.
Ita dai kalmar matasa na nufin samari ne wadanda shekarunsu ya fara daga 18-25, kokuma daga 18-30 kamar yadda wadansu suke gani, yakuma ma danganta ne da yadda kowa yake ganin lokacin da yakamata a kira mutum a matashi, wato daga shekara 18 zuwa yadda yasamu. Idan kuma muka duba shin kowane ne hakkin matasa ya rataya akansa, zamu ga cewa hakkin nasu bawai ya rataya akan gwamnati bane kawai, harma da iyaye da sauran al’umma, koda yake ana iya cewa gwamnati ita keda babbar hakki. Abinda gwanmati yaka mata tayi wa matasa shine, samar da ilimi bai daya garesu, tsaro, kula da lafiyan su, sai uwa uba aikin yi domin kuwa wannan hakkine wanda ya rataya akanta. Sukuwa iyaye da sauran al’umma, hakkin sune suga cewa sunba matasa tarbiyya mai kyau, kuma sun basu horon daya dace dasu wajen tafiyar da ayyukansu na yau da kullum. Domin kuwa duk wata al’umma da take son cigaba, sai tabayar da cikakkiyar kulawa ga matasanta da basu kyakkyawar horon daya dace dasu don zama wakilansu na gari bana banza ba a duk inda suka shiga.
Allah sarki! Bahaushe yace wai matasa manyan gobe, kuma ko shakka babu wannan Magana haka take, kamar yadda nace a baya. Domin dai ita kalmar manyan gobe na nufin matasa ne zasu amshi tafiyar da ragamar mulki a duk lokacin da wadanda suke mulkin a yau suka tsufa ko wa adin barin aikin su yayi. Saidai labarin a kasar nan tamu tasha bamban. Domin kuwa, idan aka duba tun daga matakin kananan hukumomi har izuwa ta gwamnatin tarayya, za’a ga cewa duk wadan da shekarun su yafara daga 45-60 koma fiye da haka sune a madafin iko. Ba za’a ga matasa wadanda shekarunsu ya fara daga 25-40 ba, duk dacewa suna da babbar gudun muwar da zasu iya bayarwa wajen ci gaban kasannan.
Matasa a yau sun zama kashin bayan ci gaban kowace al’umma, batare da la’akari da muhimmancin su a cikin al’umma ba, dakuma rawar da zasu taka ta fannin gina kasa. Hakika wannan yaka mata yazama kalu bale gasu matasan don ganin martabarsu ya karbu a ko ina, ta hanyar kaura cema duk wani aikin ash-sha, shaye-shaye da dai suransu, ganin cewa akwai bata gari acikinsu, kuma bahaushe yace wake daya shi ke bata gari. Saboda haka yaza ma wajibi ga matasa da su gyara kansu, sukuma san cewa dabi’ar banza bazata haifar masu da da mai ido ba. Har ila yau kada matasa su yadda su zama ‘yan bangan siyasa, abin nufi anan shine, kada wasu ‘yan tsirarun mutane su rika amfani dasu wajen tada zaune tsaye don kawai cimma burinsu, wanda bayan su wadannan mutane sun samu abin da sukeso basa yiwa su matasan komai illa su watsar dasu. Matasa susan cewa fa su wakilai ne na samar da zaman lafiya ba hargitsi ba a cikin al’umma. Komai na iya faruwa a duk lokacin da aka tauye ma matasa hakkinsu ko akaci gaba da nuna halin ko inkula dangane da rayuwarsu, musamman ma idan babu cikakken tsaro, ilimi, da uwa uba aikinyi da kuma sauran abubuwan more rayuwa wanda yazama hakkine na hukuma ta samara dasu. Rashin wadan nan abubuwa zai iya jefa matasa a tsaka mai wuya, kamar dai sace-sace, yawon banza da sauran aikin ashsha da baza’a rasaba, wanda kuma bama fatan hakan ya faru ga su manyan goben.
Daga karshe, ya kamata gwamnati da sauran hukumomin da abun yashafa da su san cewa fa matasa abin wasa bane a kowace irin al’umma. Musamman ma ganin cewa sune manyan gobe kamr yadda nayi bayani a baya, kuma suna da gudun muwa na cigaba da zasu iya bayarwa. Don haka yana da kyau a rika duba duk wata irin matsaloli dake damunsu, da kuma yin kokarin samar masu da maganinsa. Kana duk wata al’umama ko gwamnati data ga ayukanta na samun cikas ko rashin ci gaba, to ta waiwaya ta dubi matasanta taga yadda al’amuransu yake tafiya.
Subscribe to:
Posts (Atom)