Friday, May 28, 2010

ELEVEN YEARS OF DEMOCRACY: Success or Failure?


Day in, day out, a wise man says that a year is just akin to a day. It is now eleven years since the return of civilian and democratic rule or government in Nigeria and simultaneously the incumbent president, Goodluck Jonatan, is now in his third week in office after stepping into the shoes of the former president Late Umaru Musa ‘Yar’adua who died some weeks back, after spending about three years steering the mantle of leadership in Nigeria as its number one citizen from 2007 to 5th May 2010.



It is now desirable for Nigerians, especially those at the grass roots level, to look back and cogitate over this period of decade of democratic rule in Nigeria on what dividend or developments do they achieve or experience. Though they have since expressed their dismay over the catastrophic conditions they had found themselves during the eight years of draconian rule of Mr. Obasanjo.Those conditions/situations of unemployment, high cost of living, melting down industries and factories, e.t.c during those eight years of Obasanjo were some of the reasons that necessitated Nigerians to come out during the 2007 General elections (in order) to bring changes and thereby find a lasting panacea to their worries.



Few Nigerians expect that there could be a meaningful change on the ground of the mannerism of leadership of late Yar’adua at the inception or assumption of office by trying to legitimatize his government to the Nigerians in particular and the whole world in general. This is clearly because he is fully aware that the election that brought him into office was characterized by an unprecedented election malpractices in the history of Nigeria . Respect for the rule of law, independence of the judiciary, unity government, zero-tolerance to corruption, and the like, are some of the reasons why some Nigerians welcomed the late Yar’adua’s government. He (Yar’adua) actually delivered the goods with respect to the independence of the judiciary. This is corroborated from the fact that he remained mute when the election Tribunals and Courts were busy nullifying the elections of P.D.P candidates at the various level of government on the ground of electoral malpractices. Late Yar’adua has, without any iota of doubt, shown a sense of maturity in that respect which was not obtained in the Obasanjo’s era.



The recognition of the autonomy of the judiciary and that of the other branches of government by the Yar’adua’s administration had crucially changed the minds of many Nigerians from expecting to the hoping that a new messiah has come to save Nigeria and Nigerians from the shackles of squalor and poverty which they found themselves in during the Obasanjo’s era.

If we look at the power sector during Obasanjo’s regime, many committees were constituted to address the issue but with little to show. Billions of Naira have been spent fruitlessly. The present administration has also constituted the committees some years back for the same purpose but with little or no success at all. Many problems are still deeply rooted in the country ranging from lack of potable water, defective health system, educational degradation, lack of security and agricultural backwardness, to mention but a few.



It is very unfortunate that despite the vast natural resources that God in his infinite mercy endow Nigeria with, the resources are mismanaged by a very few and the masses are left in squalor and poverty. The national cake is being looted and squandered by few out of Whims and Fancies to the detriment of the majority. In some instances the money is spend not in the right way as in the case where dogs were transported into the country at the price of 2 millions naira. What a madness!



Jonathan should as a matter of urgent, address these issues once and for all to avoid further escalation of the problem, Especially the internal problem surrounding his party (PDP) so as to ensure a credible election come 2011 becouse we need to have a credible, free and fair election not selection. the election that will be accepted by all Nigerians and international observers, so that at the end, he (jonathan) will be trusted more, and also earn reputation both at home and abroad.



Now the question is what is the benefit derivable from the Nigerian democracy, is it a dividend or a loss? Infact there is nothing tangible to show which Nigerians can be said to have been benefited in the fast eleven years of democratic rule. Indeed the poor remain poorer and the reach remain reacher by day. This is therefore a challenge to the Jonathan’s government to do something concrete before the remaining year elapse and it then become too late to cry.

DIMOKURADIYYA A SHEKARU 11: Ina aka Dosa?


Kwanci tashi ba wuya, shekara kuma kwana ne inji masu iya magana. Yau shekaru goma sha daya kenen da mulkin dimokradiyya ya sake dawowa a kasarnan, yayin da kuma shugaba Goodluck Jonathan ke cika ‘yan kwanaki a gadon mulki bayan rasuwar shugaba Umaru ‘yaradua wanda ya kwashe shekaru kusan uku yana mulkin Nijeriya.



Shekaru goma sha daya da aka kwashe ana mulkin dimokradiyya lamari ne daya dace ‘yan Nijeriya musamman ma talakawa suyi waiwaye suga irin ribar da suka samu a wadannan shekaru. Koda yake, tuni ‘yan Nijeriya suka bayyana rashin jin dadinsu da irin bala’i da halin kaka-ni-kayi da suka shiga a karkashin mulkin Obasanjo na shekaru takwas wanda yakare ba tare da sun amfanu ba. Irin wannan hali da talakawa suka samu kansu a lokacin mulkin Obasanjo na rashin aikin yi, tsadar rayuwa, tabarbarewar masana’antu, da sauran matsananci hali yasa sukayi tururuwa don kawo sauyi a lokacin zaben 2007.



Kasancewar marigayi ‘Yar’adua shugaban kasa yasa wasu kalilan daga cikin yan Nijeriya tunanin cewa za’a samu sauyi don ganin yadda marigayi ‘Yar’adua ya dauko salon shugabancin da farko inda ya fara neman halasta gwamnatinsa a idon yan kasa dama duniya baki daya, domin kuwa yasan cewa zabensa cike yake da magudi. An fara maraba da marigayi ‘Yar’adua ne bayan ya bayyana aniyarsa na yin aiki da kowa inda ya fara neman goyon bayan ‘yan adawa dasu shiga a dama dasu don ci gaban Nijeriya, yayi kuma alkawarin sakin mara ga fannin shari’a batare da yi masu katsalandan ba da dai sauransu. Hakan kuwa ya fito fili ne yayinda alkalai suka rika yiwa masu rike da mukaman siyasa karkashin jam’iyar PDP kamar gwamnoni, yan majalisu, da dai sauransu wadanda aka halasta masu zaben da basu sukayi nasara ba tsirara a kotunan zabe, kuma marigayi shugaba ‘Yar’adua baice uffan ba, sabanin yadda Obasanjo ya rika cin karensa ba babbaka a kotunan zabe lokacin mulkinsa.

Baiwa fannin shari’a cin gashin kanta da marigayi ‘Yar’adua yayi da sauran hukumomi ya sauya tunanin yan Nijeriya kan ‘Yar’adua inda kowa ya fara yabamasa da cewa za’a samu kyakkyawar sauyi a gwamnatinsa da kuma kawo karshen halin da yan Nijeriya suka tsinci kansu a zamanin mulkin uban gidansa Obasanjo. Hakan yasa marigayi ‘Yar’adua ya fito da kudurori bakwai wanda yake son cimma a lokacin mulkinsa, wasu daga cikinsu an samu nasarar aiwatarwa, wasu kuma ana kan yinsu, amman Allah bai cika masa burinsa ya kamala sub a, sai dai yanzu zabi ya rage gashi Goodluck Jonathan na ganin an aiwatar da wadanna kudoririn da uban gidansa ya tsara ko akasin hakan.



Idan aka dubi fannin wutar lantarki, wanda shine uwa uba, kuma sanadiyyar sa masana’antu da dama sun durkushe,lamarin ba’a cewa komai. Lokacin Obasanjo ba irin kwamiti da ba’a kafa ba don samun saukin abun amman duk abanza, domin kuwa ankashe biliyoyin naira lokacin Obasanjo amman kwalliya bata biya kudin sabulu ba. Har yau, anada matsalar rashin kyakkyawar ruwan sha, rashin kwakkwaran tsarin kula da lafiyar yan Nijeriya, tabarbarewar tsarin ilimi, rashin tsaro, fannin noma ma duk bata canja zani ba.



Kullum dai abin sai kara tabarbarewa sukeyi duk kuwa da irin arzikin da Allah yayi wa Nijeriya, koda yake arzikin kan komane aljihunan kalilan daga cikin yan kasa sauran kuma a kashesu ta hanyar da bazasu amfani al’umma ba. Kamar dai yadda akeso a sayo wai karnuka kan naira miliyan biyu akan ko waani kare guda daya! Wanna lamari da mai yayi kama ?



Tilas Goodluck sai yayi da gaske don ganin ya sai sai ta sahun lamurran kasar nan musamman ma dai rikicin dake mamaye da jam’iyarsa ta PDP wadda ke fama da rikice rikicen cikin gida, wanda a halin yanzu a Nijeriya ana bukatar gwamnati mai karfi wadda zata fito kai tsaye don fuskantar kalubalen da suka mamaye kasar tun kafin dimokuradiyyar ta durkushe. akwai bukatar a tabbatar da anyi zaben adalci kuma tsarkakakke a 2011, zaben da yan Nijeriya zasu amince dashi da kasashen duniya, ba wai a nada masu wadanda basa so ba.



To wai a tsawon wadannan shekaru suwa suka amfana ko sukaci ribar mulkin dimokradiyyar nan? Shin anci riba ne ko asara akayi? Talaka bai amfana ba ta ko ina kuma baici ribar dimokradiyya ba don kuwa har yanzu yana nan yana ci gaba da dandana kudarsa da ta samo asalin tun mulkin Obasanjo, ba’a aiwatar da ayyukan ci gaban kasa ba, masana’antu sai kara durkushewa sukeyi, ga rashin aiki ga matasa, da dai sauransu. Don haka, wannan wani kalu bale ne ga shugaba Jonathan na ganin yayi kokarin aiwatar da manufofinsa a cikin shekara daya da ya rage ma gwamnatin sa.

Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukan mu na alhairi, amin.

Tuesday, May 11, 2010

BA RABO DA GWANI BA, MAYE GURBINSA.

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Ranar alhamis rana ce da al’ummar Nijeriya suka tashi cikinta tare da samun mummunar labarin rasuwar shugaban kasa Alhaji Umaru musa Yar’adua, Matawallen Kastina. Ko da yake labarin baizo da mamaki ba kasancewar ya dade yana jinya kafin Allah yayi masa cikawa a daren laraba 5/5/10, kuma dama kowa yazo lokacin da aka diba masa, la shakka zai tafi ba tare da an kara masa koda dakika daya ba.
Alal hakika jihar Katsina, Nijeriya, afrika dama duniya baki daya sunyi rashin gwarzo wanda ya dukufa don ganin ya wadatar da al’ummar da yake shugabanci da ababan more rayuwa da inganta harkokinsu da gina kasa, kama daga samar da aikin yi ga matasa, bada ingantaccen Ilimi, inganta harkan tsaro da Noma, samar da wutan lantarki don cigaban masana’antu da dai sauransu. Amman hakansa ba ta kai ga cimma ruwa ba sai mai duka yayi ikonsa. Tabbas, rasuwar yar’adua ta bude wani sabon babi a fannin siyasar Nijeriya wanda a halin yanzu yake cike da rudani kama daga jam’iyarsa ta PDP da ma sauran jam’iyyun hamayya, kuma samun mai maye gurbinsa abune mai matukar wuya idan akayi la’akari da yadda Yar’adua ya sadaukar da kansa kuma mutum ne mai saukin kai wanda kuma yake ba kowa hakkinsa yadda ya kamata. Yar’adua ne shugaban kasa karkashin mulkin farar hulla na farko da ya amince cewa zaben da ya kawoshi gadon mulki cike yake da kura kurai, kuma ya dauki aniyar kawo sauyi kan yadda zabe zai rika gudana don yan Nijeriya su rika na’am da zabubbukan da za’a rika gudanarwa .
Ko shakka babu ansamu cigaba da chanji sosai ta fannin siyasa karkashin jagorancin marigayi Yar’adua. Alal misali, lokacin mulkinsa ne aka sakan ma fannin shari’a mara ba tare da yi masu katsalandan a cikin aikinsu ba da ma sauransu. Hakan kuwa ya fito fili ne yayinda alkalai suka rika yiwa masu rike da mukaman siyasa karkashin jam’iyar PDP kamar gwamnoni, yan majalisu, da dai sauransu wadanda aka halasta masu zaben da basu sukayi nasara ba tsirara a kotunan zabe, kuma shugaba ‘Yar’adua baice uffan ba, sabanin yadda Obasanjo ya rika cin karensa ba babbaka a kotunan zabe lokacin mulkinsa.
Baya ga baiwa fannin shari’a da suaran ma’aikatu cin gashin kansu, marigayi yar’adua ya samu nasarar magance matsalar da aka dade ana fama da ita na shekara da shekaru a yankin Niger-Delta mai arzikin mai, inda akayi ma tsagerun yankin afuwa don samar da zaman lafiya a yankin dama kasa baki daya. Hakika wannan ba karamin nasara bane ganin yadda su tsagerun suka ajjiye makamai suka rungumi afuwar da matawallen katsina yayi masu don kasa taci gaba. Har ila yau, a lokacin mulkinsa ne (Umaru Yar’adua) aka kawo karshen takaddamar da ka kwashe shekaru ana yi tsakanin Nijeriya da Cameroun a kan yankin bakasi.
Yar’adua ya kasance mutum mai son bin doka da oda, mutunta fannin shari’a, bin diddigin al’amurra, har ila yau mutum ne mai son zaman lafiya ba tare da anyi haya ni yaba. Don haka, wadannan abubuwa ne da ’yan Nijeriya bazu taba mantawa dasu ba game da marigayi Umaru Musa Yar’adua. Matawallen katsina ya bar gidan duniya tare da burin ganin ya kawo sauyi kan yadda ake gudanar da zabe da suaran wasu lamurra, Amman Allah bai cika masa wadannan burrorin ba. Sai dai muyi masa Addu’ar samun rahama daga ubangiji, ya kuma baiwa iyalansa, yan uwa da abokan arziki jure wannan babban rashi wanda maye gurbinsa a bu ne mai wuya. Mu kuma in tamu tazo, Allah yasa mu cika da imani.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.

Saturday, May 8, 2010

TRIBUTE TO YAR'ADUA


To Allah we are and to him our return is! President Umaru Musa Yar’adua has been call to glory. That’s ordinary of human lives. He died when his contribution is highly needed in the country . We all believed that what God has destined to happen no human being on this earth can change it. While he lived, President Yar’adua was a cool headed unassuming person who gave everybody his due respect. A philanthropist,a man who stood for justice, fair play and equity. A hardworking and trustworthy man. Katsina state and Nigeria has lost an honest leader who meant well for his people.
President Yar’adua will surely be remembered for his quiet dignity, sincere believe in rule of law, commitment to Deeping democracy and landmark resolution of Niger Delta crisis. No doubt, his death has opened a new chapter in the political journey of Nigeria.
It’s our earnest prayer that the almighty Allah will have mercy on him, together with all the muslims who died before him right from the time of prophet Adam (A.S). May he afford us the will and patience to pray for them and bless us with those who will pray for us when we die. We pray to almighty Allah to continue to give the family, relatives and friends the fortitude to bear the irreplaceable lost. We also pray that his gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.

Saturday, February 20, 2010

TANDJA MOMODOU: Its too late to cry when......



Thursday, 18th day of February, 2010, is one of the turning point in the political and leadership history of Africa in general and Nijar republic in particular. It was on same day and date that the good people of Nijar republic found themselves in a state of commotion at the early noon hours when the illegal and unconstitutional government of Tandja Momodou was toppled by General Adamu Haruna.
If we can recall, it was last year during the tail end of Tandja’s second tenure in office as the president of Nijar republic that he brought an innovation into the political system of Nijar by conducting a referendum that could give him a license to stay in office beyond the constitutional provisions and requirements. That attitude of legalizing what is illegal and constitutionalizing what is unconstitutional made the constitutional court and the legislative arm of Nijar republic to outrightly frowned and rejected it as it is unconstitutional. Tandja was not happy with their stand on the issue and as such he injudiciously used his power and dissolved both the constitutional court and legislative organ of Nijar so that he can achieve what he desired. This was followed by the purported and the so-called “referendum” in August, 2009 where he single-handedly (together with his political boys) organized, conducted, and produced out their desired result to the effect that the innocent people of Nijar republic have agreed by a majority vote, that Tandja should continue with the steering in of the mantle of leadership in Nijar.
Though, all that kind of political mutilations of dissolving the constitutional court, the legislative arm, as well as conducting the said referendum were plan and idea inculcated into Tandja’s mind by nobody other than Abubakar dan Dubai, bin Umar, and some few selfish individual ministers that have no regard for the democratic rule. Dan Dubai was the figure-head in Tandja’s journey to perpetuate himself in power without having recourse to its negative consequences. Tandja failed to appreciate the fact that dan Dubai is nobody other than a business tycoon who is not living in Nijar republic and whose primary aim is how to maximize his profits and nothing less, nothing more.
It has been a well known fact that Tandja had unconstitutionally extended his tenure in office against the will of most of the people of Nijar. It’s very lamentable and highly embarrassing to see how African leaders always want to perpetuate themselves in power and a times considered it as hereditary without respecting the rule of law, fundamental human right, and the rule of the game itself. Life ruler ship is their aims and in their absence they preferred their children to step into their shoes. For God’s sake, is this what we call a democracy? Is this what the developed countries practice or observe their democracy? I will not be taken by surprise to know that most of these African leaders know nothing about what a democracy is all about. Their mission(s) is nothing other than to find themselves in power, siphon the public funds and thereby enrich themselves.
It is now clear that Tandja has now bring to an end the nascent democracy that has come to stay in Nijar. Today, the fifth republic, the sixth unconstitutional republic, and Taandja himself are nowhere to be found. Now, Tandja is in detention as if he was not a president few days before his government was overthrown. He cannot even see his family as he wishes. This is certainly one of the consequences of going against the spirit of a constitution and the wishes of the masses. Tandja ought to have had learnt a lesson on what happened to the former Nijar president, Ba’are mai nasara, Mannuel Zalaya of Honduras, and captain Musa Dadis Camara of Guinea. Was Tandja unaware or has forgotten how those people lost their offices when they tried to perpetuate themselves in power? In fact, Ba’are mai nasara even lost his life in the process. Tandja was dumb, deaf, and blind when the African union and Ecowas appealed to him to respect the constitution and the rule of law by allowing people to elect who they want to govern or rule them. This led to the stoppage of the assistance given to Nijar by the African countries and that from the European Union. With all this situation, Tandja boldly said that there is no going back.
One of the touchy thing in Tandja’s journey to where he is today was how he treated the representative of Ecowas to Nijar. He gave him no single attention over the political tete-a-tete with the politicians on how to resolve the political tension in Nijar. The deed is done, and all become history. The nagging question is when are we going to be matured enough to handle our political problems without waiting for soldiers to handle them for us? Had it been that Mr Tandja had honorably moved aside after the expiration of his second term, I believe that definitely he would be remembered in Nijar in particular and the world at large as one of the successful president Nijar ever had. But reverse is the case. Today, he is only going to be remembered as Tandja whose government was toppled by the military men as a result of his individual selfishness by imposing himself to the people of Nijar and creating a political commotion in Nijar.
The Saturday marching, two days after the coup, by the people of Nijar showing their loyalty and support to the soldiers is a strong and clear testimony that they are fed-up with Tandja and his undemocratic, unconstitutional, and unreasonable extension of tenure in office. Though, hitherto to his time Tandja had insisted that he and he alone can rule Nijar.
The assertion of Tandja in a press conference that he has slaughter a Ram is now proved to the contrary. He might have had slaughtered the Ram from the back of his neck or from his tail. To this end, what happened to Tandja is one of the consequences of breaching the constitution of Nijar coupled with the deliberate refusal to take, consider, and act on the calls from different angles of the world to respect the rule of law and constitutionalism.
At this juncture, we are urging the military in Nijar to dispense justice in their government and to organize a free and fair election within a reasonable time and not to stay in power unreasonably. The embarrassing thing that happened to Mr Tandja should served as a lesson to the African leaders like him whose aim is to rule or stay in power for life at all coast.
Lastly, I am concluding this paper with a prayer, seeking refuge from the Almighty from all evils and harmful acts. May he also be our guardian in all our endeavours, ameen.

GARIN NEMAN KIBA, TANDJA YA NEMO RAMA.


Na tabbata ranar Alhamis wanda tayi daidai da 18/02/2010 ba zata taba gushewa a zukatan al’ummar nahiyar Afrika ba, musamman al’ummar jamhoriyar Nijar sakamakon yanayin da suka tsinci kansu a cikin tsakiyar wannan ranar wanda hakan yakai ga kifar da haramtacciyar jamhoriya ta shida karkashin jagoranci janar Adamu Haruna wanda shugaba Tandja Mamadou ya girka.Tun dai bayan da shugaba Tandja Mamadou na Nijar ya kusa kawo karshen wa’adin mulkinsa karo na biyu a shekarar da ta gabata ne sai ya fito da wani sabon salo nayin kuri’ar jin ra’ayin jama’an kasar Nijar wanda zai iya bashi damar ci gaba da mulkin kasar fiye da yadda kundin tsarin mulkin kasar ya bashi dama. Fito da wannan maita tashi fili da yayi yasa majalisar kasar tare da kotun koli suka ce ko kusa wanna yunkuri da Tandja keyi ya sabama tsarin dokokin kasar. Hakan kuwa baiyiwa Tadja dadi ba ganin cewa ya fara samun cikas daga majalisar kasar, wanda hakan yasa bai bata lokaci ba sai yayi amfani da karfin ikonsa ya rusa majalisar tare da kotun kolin kasar don dai cimma wannan bakin buri nasa, kuma ya wuce kai tsaye a watan agusta na 2009 yayi zaben raba gardama inda yayi kidansa yayi rawansa duk shi kadai yabada sakamaon da yake so, ya bayyana ma duniya cewa al’ummar Nijar sun amince da yaci gaba da mulkansu don ci gabda da aikata ayyukan alheri da ya somo a baya, a cewarsa amman.
Ko da yake duk wadannan abubuwa kama daga kuri’ar jin ra’ayin jama’a, rushe majalisar kasa da sauransu da Tandja ya yi ba kowa ke ingizasa ba sai Abubakar dan Dubai, bin Umar, da suaran ‘yan tsirarun ministocinsa wadanda basu girmama mulkin dimokuradiyya. Dan Dubai shine dirabar motar da Tadja ya shiga don neman tazarce ba tare da kallon irin illolin da hakan ka iya haifarwa ba. Tandja yaki fahimtar cewa dan Dubai fa dan kasuwa ne, kuma bawai yana zaune a kasar Nijar bane, kuma shi burinsa kawai waye zai sake masa mara ya rika cin karensa ba babbaka ba tare da ko al’umma najin dadinsa ko basa jiba. Burinsa kawai idan miyansa ta gyaru, to na gidan uban kowa ma ya bace.
A gaskiya kowa yasan cewa Tandja yayi amfani da karfin ikonsa ne don yaci gaba da mulkin Nijar bawai don ‘yan kasar na da muradin hakan ba, sai dai kawai don bin ra’ayin irin su dan Dubai da sauransu. Abin kunya ne yau yadda shugaban nin Afrika suka maida mulki tamkar gadon gidansu, basa mutunta hakkin al’ummarsu, basu mutunta dokokin mulkin dimokuradiyya. So suke su rika dawwama a madafun iko har sai bayan ransu, idan ma sun mutu to ‘ya’yansu ne sukeson su gaje su. Don Allah wannan shine dimokuradiyya? Haka muka ga kasashen da suka ci gaba ta fannin dimokuradiyya suke yi? Ba zanyi mamakiba idan mafi yawanci wadannan shugabannin basu san abinda ake nufi da dimokuradiiya ba. Burinsu kawai shine su amshi mulki ko ta wani irin hali don su wawure dukiyar talakawansu tare da azurta kansu.
Ta tabbata yau Tandja ya gurgunta mulkin dimokuradiyyar data kamo hanyar zama da kafafunta biyu a jamhoriyar Nijar. Yau babu jamhoriya ta biyar, babu haramtacciyar jamhoriya ta shida da Tandja ya kafa, babu Tandja a shugabancin Nijar, to don Allah wa gari ya waya? Duka yau kwana nawa Tandja ya kara akan mulkin? Yau Tandja yana tsare cikin wulakanci, ganin iyalansa ma yanzu ya zama masa abu mai wuya, babu sauran walwala tare dashi. Yanzu Tandja yaci riba kenan ko ya kaskanta? Ya kamata ace Tandja ya dauki darasi kan abinda ya faru da Ba’are mai nasara na Nijar din, da kuma Mannuel Zalaya na Hundaros, da kaftin Musa Dadis Camara. Shin Tandja ya manta da irin nasu kwadayin mulkin ne wanda hakan yasa duk suka rasa shugabancin kasashensu? Ba’are mai nasara kuwa ba mulkin ya rasaba, ransa baki daya ya rasa. Tandja yayi kunnen uwar shegu, ya zama kurma ya kuma zama makaho ga dukkan irin kiraye kirayen da kungiyar tarayyar afrika da na ECOWAS suka yi masa na da ya mutunta kundin tsarin mulkin kasar, ya sauka ayi zabe amma Tandja ya toshe kunnensa yaki sauraron kowa. Hatta tallafin da kasashen Africa da na tarayyar turai ke ba Nijar sun dakatar da bayarwa amman haka duk bata girgiza Tandja ba, bai sa ya canja gurguwar shawarar dasu dan Dubai suka bashi ba nayin tazarce.
Wani babban abin ban haushi shine yadda Tandja yaki mutunta manzon da kungiyar tattalin arzikin kasashen afrika ta yaamma ta tura zuwa Nijar don kawo karshen dambarwan siyasar da ta ki ci taki cinyewa, Tandja yayi kunnin uwar shegu yaki maida hankali kan tataunawar da akeyi da ‘yan siyasar kasar don kawo maslaha acikin lamarin. To yau dai mai faruwa ta riga ta faru, duk abinda za’a fada sai dai ya zama labari kawai. Ai dama an ce duk wanda ya shiga motar kwadayi, to la shakka ba zai sauka ako ina ba face tashar wulakanci.
Yaushe wai zamu zauna a Afrika mu kasa warware matsalolin siyasar dake damunmu har sai mun jira sojoji sun shiga tsakani? Yau da Tandja ya tsare mutuncinsa ya sauka cikin girma da arziki da ya shiga cikin kundin tarihin Nijar da ma duniya baki daya cewa yayi mulkin Nijar har sau biyu kuma ya kamala sumul. Amman yau fa? Sai dai ace Tandja wanda sojoji suka kifar da gwamnatinsa sakamakon yin tazarce da karfi da yaji, ko kuma ace sakamakon jefa kasar da yayi a yanayin rudani na siyasa, kamar dai yadda kakakin wadanda suka yi juyin mulkin kanar Abdulkarim ya bayyana ma manema labarai cewa sun yanke karbar mulkin ne sakamakon halin rudani na siyasa da ksar ta samu kanta ciki. Zanga zangar da al’ummar Nijar kuwa sukayi ranar Asabar, kwana biyu bayan hambarar da gwamnatin Tandja don yin mubayi’a tare da nuna goyon bayansu ga gwamnatin mulkin soja ya nuna a fili cewa al’ummar Nijar sun gaji da mulkin da Tandja ke musu amman shi yayi keke yana son ya nuna ma duniya cewa in bashi ba to babu mai iya mulkin Nijar.
Yau dai ragon da Tandja ya bayyana ma ‘yan jarida cewa an yankata kuma baza ta tashi ba to ta tashi. Wata kila ta keya Tandja ya yanka ragon ko a bindi ya yanke shi. Dama ai ance duk wanda baiji bari ba to zaiji hoho. Wannan shine sakamakon kin bin dokokin mulkin Nijar da Tandja yayi, tare da kin amsa dukkan irin kiraye kirayen da kasashen duniya sukayi masa na da ya mutunta mulkin dimokuradiyya ya sauka tunda wa’adinsa ya kare amman yaki ji. Fatarmu dai shine wadan nan sojoji suyi mulkin adalci kuma su gagguta maido da gwamnatin farar hula ta hanyar gudanar da zabe sahihi,ingantacce,tsarkakke kuma karbaben ga al’ummar Nijar. Don haka wannan abin kunya da ya faru da Tandja Mamadou ya kamata ya zama darasi da kuma hannunka mai sanda ga sauran takwarorin Tandja na nahiyar Afrika masu son dawwama a mulki ko ta wani rin hali, domin dai ance idan gemun dan uwanka ya kama da wuta, to ka shafama naka ruwa.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.

Thursday, January 28, 2010

CONFERMENT OF SARDAUNAN KANO ON GOV. SHEKARAU


The conferment of sardaunan kano on Mallam (Dr) Ibrahim Shekarau the executive governor of kano state by Emir of kano Alhaji (Dr) Ado Bayero is a plus to the political profile of Mallam Shekarau. However, the conferment of this tittle to Shekarau generates a lot of comments within and outside the state. While some are saying it’s indeed a plus to his Excellency’s political carrier and are rejoicing with him, others are seeing it in the other way round.

Definitely, whatever it is, the Emir of kano make a wiser decision by chosen Mallam Ibrahim Shekarau as sardaunan kano and at the right time, especially taking into consideration the way Mallam Shekarau is continuously transforming and developing the state and its people in different forms.

Foristance, Tamburawa water dam constructed/built by Mallam Shekarau is second to none in Africa, has bring an end to the scarcity of water suffered by the good people of kano state for several years, employment opportunity to youths, helping the physically challenged ones, the less privileges and expansion of the major roads in the city which is currently going on so as to reduce the rate of congestion in the city and also to enhance the commercial activities of the state-also in the past two months, people of kano state experienced or start experiencing uninterrupted power supply. All these are development recorded under Shekarau’s administration.

Dedicating himself tirelessly to the service of humanity and giving everyone his due right irrespective of religious, political or tribal differences, sacrifice, God-fearing, selfless service and many other things are what earned Mallam Ibrahim Shekarau the tittle of sardaunan kano. Because even some states in this country testified the kind of transformation that kano state has recorded and are still achieving under the administration of Mallam Shekarau, and as such he was awarded with the traditional tittle of Onwa Na-Etiri oha1 na Ehaalumono from southern part of this country. This shows that his commitment (Mallam Shekarau) to serve the good people of kano state and indeed Nigeria as a whole is appreciated. Truly, the executive governor of kano state, Imam of societal reorientation, deserves to be called magajin sardaunan Sokoto because his commitment to the service of humanity and development of his people is similar to that of late sardaunan Sokoto Alhaji Sir Ahmadu Bello.

It is well known to everyone that since after it’s creation, kano state did not witness rapid transformation and development like in the seven years ago under the excellent innovative leadership of Mallam Ibrahin Shekarau- This is a blessed development and opportunity that people of kano state should be proud of and thanks the almighty God for blessing them with a governor that pay attention to nothing but development and upliftment of his people. Therefore, his Excellency Mallam (Dr) Ibrahim Shekarau, Imam of societal reorientation, garkuwan Ilimi, sardaunan kano, Onwa Na-Etiri oha1 na Ehaalumono, magajin sardaunan Sokoto needs nothing from people of kano state than prayers for God to grant him his wishes and give him the opportunity to deliver the mandate given to him successfully by people of kano state. We pray that Almighty Allah in His own will and power will one day give Governor Shekarau an opportunity to serve the country at large insha Allah.
Lastly, I am concluding this paper with a prayer, seeking refuge from the Almighty from all evils and harmful acts. May he also be our guardian in all our endeavours, ameen.

Sunday, January 3, 2010

Relationship Between America And rest of the World:

THE RELATIONSHIP BETWEEN U.S.A AND THE REST
OF THE WORLD
The accusation by the American Government on Faruq Umar Abdul-Mutallab, who happen to be a Nigerian, for attempting to bombard a plane in America on the 25th Day of December, 2009, remain the subject of discussion throughout the world, especially the way and manner adopted by both the local and international mass-media in disseminating it, almost everyday.
Similarly, it is of common knowledge and undisputed fact that America is second to none when it comes to the issue of concoction and dissemination of propaganda. Almost always, their (America) mission is to create tension and emotional disorder in the minds of innocent fellow human beings.
Assuming but not conceding that the accusation against Faruq is true, then it is now a time for America to sit and cogitate on why these series of attacks and attempted attacks were aimed at it alone. Because, a wise man says that there can never be a smoke without fire. Obviously, the America and American government should ask theirselve why the attacks were always targeted at America not for instance, Germany, Australia, Denmark, China, Russia, Japan, Togo, or Ghana? Why America is the final bus-stop for everybody with all sorts of grievances, dissatisfactions, and disappointment of life? What kind/sort of relationship exists between America and this kind of people or the world at large? These are few out of many questions that America needs to find out their answers.
However, nothing is new it has been for long time that America and its allies considered us as terrorists. But at this juncture, I am strongly and courageously saying that it is unwise and unjust for America and the western-world to consider the religion of Islam as a religion of terror or the one that support terrorism just because of what Faruq did. This is because some people have already related his alleged act (if time) to the religion of Islam.
I sincerely see no nexus between his alleged act and the religion of Islam which is the religion of peace.
Common sense, good sense, and natural justice can never allow the alleged act to serve as a yardstick for jumping into conclusion that every Muslim is a terrorist.
The worst part of it is how some of the so-called “SENATORS” and “REP-MEMBERS” in America are calling for an immediate transfer of Faruq to their illegal prison in GUANTANOMO. This clearly translates how illiterate they are on what HUMAN RIGHTS are all about. They wittingly ignored the fact that they have a better person to send there but not Faruq. Though, I am not holding a brief for Faruq, but they should know that BUSH W. GEORGE is the rightful person that supposes to be in Guantanomo for the illegal, criminal, and inhuman acts he perpetrated while he was the American president.
He was the brain behind the lost of many innocent lives in Iraq and Afghanistan. To crown it all, the said BUSH is the real causative of all sorts of catastrophic and calamities that are befalling America now a day.
Those law-makers should also be reminded that in almost all the criminal justice in the world, the golden and guiding principle is that AN ACCUSED PERSON IS PRESUMED TO BE INNOCENT UNLESS AND UNTIL HE IS FOUND (PROVED) TO BE GUILTY BY A OCURT OF LAW (and of competent jurisdiction not court of public opinion). Though, his accuser(s) claimed that he confessed or admit the accusation, this is immaterial because we have not yet hear from him.
At this point, the Nigerian government should as a matter of urgency send their officials to America so that they can work in collaboration with a view of doing justice to the issue. This is because up to the time I am writing this paper, I have not seen the Faruq saying a word over the issue in any electronic-media neither hear his voice but always America said this and said that. Until we hear from him or watch his video, we will never agree with the said propaganda.
I have no iota of doubt in my mind that had it been that Faruq is an American the issue would have been forgotten by now. What they will do is nothing more than to declare that the accused person is suffering from mental disorder and nothing more or less. As such, it is mandatory for the Nigerian government as a sovereign country to involve itself in this serious issue to see that the rights of its citizen are not unjustly being infringed and simultaneously to prevent its unrefutable image from the rest of the world.
Lastly, I am concluding this paper with a prayer, seeking refuge from the Almighty from all evils and harmful acts. May he also be our guardian in all our endeavours, ameen.
By:
MUNTAKA ABDUL-HADI DABO,
ANGUWAR FATIKA,ZARIA.
write2muntaka@yahoo.com

Dangantakar Amurka da Kasashen Duniya


Tun bayan da mahukuntan kasar Amurka suka zarigi dan Nijeriyan nan mai suna Farouq Umar abdulmutallab da yunkurin tada bom a sararin samaniyar kasar Amurka ranar 25-12-09 hankalin duniya baki daya ya karkata kan wannan, musamman ma ganin yadda kulli yaumin kafafen yada labarai na gida da na waje ke ci gaba da ruruta yadda lamarin ya auku.
Da farko dai kada ayi tuya a manta da albasa, kowa yasan cewa duk duniya babu kasar da ta shahara kuma ta kware wajen kago labaran karya da zasu dauki hankalin duniya tare da tada zukatan al’umma kamar kasar Amurka. Kullum su burinsu shine kawo rashin kwanciyar hankali a duniya da kuma musguna ma wadanda basu jiba basu gani ba. Sa ma ace wannan zargi da ake ma Umar Farouq gaskiya ne, koda yake ana nan ana binciken don gano gaskiyar lamarin, idan har zargin ta tabbata to wannan wani abu ne da ya kamata kasar Amurka ta zauna tayi ma kanta karatun natsuwa gami da tunani tare da tambayar kanta mai yasa irin wadannan aikin ta’addanci ke faruwar a kasar ta kawai? Don me yasa ba aje kasar Germany, Australia, Denmark, China, Russia, Japan, Togo, ko Ghana an kai irin wadannan hare haren ba? Me yasa kowa idan ya dauko fitintununsa baya sauke su ko ina sai Amurka? Wani irin hulda ko dangantaka ke tsakanin wadannan mutane ko duniya baki daya da kasar Amurka? Wadannan kadan ne daga cikin dimbin tambayoyin da ya kamata kasar Amurka taba kanta amsa.
Ko da yake, duk wadannan abubuwan da Amurka da sauran ‘yan kanzaginta keyi ba sabon abu bane domin kuwa sun dade suna mana kallon ‘yan ta’adda. Bai dace Amurka da sauran kasashen masu jajayen kunnuwa su rika kallon addinin musulunci a matsayin addinin ta’addanci ba sakamakon abinda ake zargin Umar Farouq da aikatawa. Don kuwa tuni wadansun su suka rika danganta wannan lamari da koyarwar addinin musulumci. Gaskiya addinin musulunci kowa yasan cewa addini ne na zaman lafiya wanda kuma baya koyar da duk wani aiki na ta’addanci ko makamantan hakan, kuma kada wannan abu ya zama mizani na daukan dukkan musulmai ‘yan ta’adda ko ‘yan Nijeriya arika masu kallon ‘yan ta’adda.
Wani abin ban haushi da takaici shine yadda wasu sanatoci da ‘yan majalisar wakilai na Amurka da basu san hakki da ‘yancin bil’adama ba suke kiran da a gaggauta tura Umar Farouq zuwa sansanin GUANTANAMO don azabtar dashi, domin acewarsu Farouq cikakken dan ta’addane wanda ya kamat ya fuskanci hukunci. Amma abin tambaya a nan shine, shin wadannan masu wanna kira na atura Farouq zuwa GUANTANAMO basu san cewa suke da babban dan ta’adda da ya dace a garzaya dashi zuwa wannan sansanin ba? Idan basu sa niba to ga sunansa, Bush W. George shine cikakke kuma babban dan ta’addan duniya, domin kuwa yayi sanadiyyar salwantan rayuka bila a dadun a kasashen Iragi da Afghanistan. A takaice dai, duk wata irin fitina dake samun Amurka Bush shine ya haifar sakamakon yadda huldar dangantakar Amurka da sauran kasashen duniya yayi tsami cikin tsawon shekaru takwas din da yayi yana mulkin kama karya a kasar, yayi sanadiyyar mutuwan al’umma a ko ina cikin duniya. To wanna ba laifi ne da yakamata a hukunta wanda ya aikata suba? Farouq fa zarginsa akeyi wanda haryanzu ba a tabbatar da cewar ko wannan zargin gaskiya ne ba, duk kuwa dacewan munji wai bayanai daga Amurka na cewa Farouq ya masa laifin da ake zarginsa dashi amman mu haryanzu bamuji daga bakinsa ba. Don haka baza mu gaskanta wanna labarin ba, domin munsan Amurka na iya zama ta shirya kowani irin labarai don jan hankalin al’ummar duniya.
Ya kamata mahukuntan Nijeriya su tura nasu jami’an zuwa kasar Amurka ayi binciken tare dasu don ganin anyi adalci a rahoton da za’a bayar. Kada su zauna su nade hannayensu su jira Amurka ta rubuta mana sakamakon bogi suce shine sakamakon binciken da suka gudanar. Domin har yanzu sai dai muji kafafen yada labarai na fadin cewa bayanai da suka fito daga Amurka sunce Farouq yace abu kaza ko ya fadi abu kaza wanda har yanzu ba’a taba sa mana muryansa munji lokacin da yake furta wadannan kalamai ba ko asa mana hoton bidiyo da aka dauka lokacin da ake yi masa tambayoyi ba, don haka duk abinda za’a fada mana soki burutsu ne kawai, baza mu taba yarda ba sai munji daga bakinsa. Wallahi yau da dan Amurka ake zargi ya aikata wannan ta’adi da yanzu an manta da maganan. Don Amurka ba zata taba yarda ayi binciken da zai sa a Gano tare da ladabtar da dan kasarta akan irin wadannan laifuffuka ba. Zatayi duk mai yiwuwa wajen ganin maganan ya mutu ko ta halin kaka. In kuma ya zama dole sai an gudanar da binciken, to zuwa zatayi ayi binciken tare da ita, wanda kuma kowa yasan cewa ba binciken za’a yiba, sune zasu zauna su tsara mana abinda za’a fadawa duniya wanda bai wuce daga karshe ace mana wanda ake zargin yana da tabin hankali ba. Don haka ya zama dole gwamnatin Nijeriya ta shiga cikin lamarin nan don kare hakkin yaron nan da kuma kare mutuncin ta a idon duniya don ganin ba’ayi amfani da wannan dama ba wajen musgunama ‘yan Nijeriya dake kasashen waje ko masu muradin fita nan gaba.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.