Saturday, February 20, 2010

GARIN NEMAN KIBA, TANDJA YA NEMO RAMA.


Na tabbata ranar Alhamis wanda tayi daidai da 18/02/2010 ba zata taba gushewa a zukatan al’ummar nahiyar Afrika ba, musamman al’ummar jamhoriyar Nijar sakamakon yanayin da suka tsinci kansu a cikin tsakiyar wannan ranar wanda hakan yakai ga kifar da haramtacciyar jamhoriya ta shida karkashin jagoranci janar Adamu Haruna wanda shugaba Tandja Mamadou ya girka.Tun dai bayan da shugaba Tandja Mamadou na Nijar ya kusa kawo karshen wa’adin mulkinsa karo na biyu a shekarar da ta gabata ne sai ya fito da wani sabon salo nayin kuri’ar jin ra’ayin jama’an kasar Nijar wanda zai iya bashi damar ci gaba da mulkin kasar fiye da yadda kundin tsarin mulkin kasar ya bashi dama. Fito da wannan maita tashi fili da yayi yasa majalisar kasar tare da kotun koli suka ce ko kusa wanna yunkuri da Tandja keyi ya sabama tsarin dokokin kasar. Hakan kuwa baiyiwa Tadja dadi ba ganin cewa ya fara samun cikas daga majalisar kasar, wanda hakan yasa bai bata lokaci ba sai yayi amfani da karfin ikonsa ya rusa majalisar tare da kotun kolin kasar don dai cimma wannan bakin buri nasa, kuma ya wuce kai tsaye a watan agusta na 2009 yayi zaben raba gardama inda yayi kidansa yayi rawansa duk shi kadai yabada sakamaon da yake so, ya bayyana ma duniya cewa al’ummar Nijar sun amince da yaci gaba da mulkansu don ci gabda da aikata ayyukan alheri da ya somo a baya, a cewarsa amman.
Ko da yake duk wadannan abubuwa kama daga kuri’ar jin ra’ayin jama’a, rushe majalisar kasa da sauransu da Tandja ya yi ba kowa ke ingizasa ba sai Abubakar dan Dubai, bin Umar, da suaran ‘yan tsirarun ministocinsa wadanda basu girmama mulkin dimokuradiyya. Dan Dubai shine dirabar motar da Tadja ya shiga don neman tazarce ba tare da kallon irin illolin da hakan ka iya haifarwa ba. Tandja yaki fahimtar cewa dan Dubai fa dan kasuwa ne, kuma bawai yana zaune a kasar Nijar bane, kuma shi burinsa kawai waye zai sake masa mara ya rika cin karensa ba babbaka ba tare da ko al’umma najin dadinsa ko basa jiba. Burinsa kawai idan miyansa ta gyaru, to na gidan uban kowa ma ya bace.
A gaskiya kowa yasan cewa Tandja yayi amfani da karfin ikonsa ne don yaci gaba da mulkin Nijar bawai don ‘yan kasar na da muradin hakan ba, sai dai kawai don bin ra’ayin irin su dan Dubai da sauransu. Abin kunya ne yau yadda shugaban nin Afrika suka maida mulki tamkar gadon gidansu, basa mutunta hakkin al’ummarsu, basu mutunta dokokin mulkin dimokuradiyya. So suke su rika dawwama a madafun iko har sai bayan ransu, idan ma sun mutu to ‘ya’yansu ne sukeson su gaje su. Don Allah wannan shine dimokuradiyya? Haka muka ga kasashen da suka ci gaba ta fannin dimokuradiyya suke yi? Ba zanyi mamakiba idan mafi yawanci wadannan shugabannin basu san abinda ake nufi da dimokuradiiya ba. Burinsu kawai shine su amshi mulki ko ta wani irin hali don su wawure dukiyar talakawansu tare da azurta kansu.
Ta tabbata yau Tandja ya gurgunta mulkin dimokuradiyyar data kamo hanyar zama da kafafunta biyu a jamhoriyar Nijar. Yau babu jamhoriya ta biyar, babu haramtacciyar jamhoriya ta shida da Tandja ya kafa, babu Tandja a shugabancin Nijar, to don Allah wa gari ya waya? Duka yau kwana nawa Tandja ya kara akan mulkin? Yau Tandja yana tsare cikin wulakanci, ganin iyalansa ma yanzu ya zama masa abu mai wuya, babu sauran walwala tare dashi. Yanzu Tandja yaci riba kenan ko ya kaskanta? Ya kamata ace Tandja ya dauki darasi kan abinda ya faru da Ba’are mai nasara na Nijar din, da kuma Mannuel Zalaya na Hundaros, da kaftin Musa Dadis Camara. Shin Tandja ya manta da irin nasu kwadayin mulkin ne wanda hakan yasa duk suka rasa shugabancin kasashensu? Ba’are mai nasara kuwa ba mulkin ya rasaba, ransa baki daya ya rasa. Tandja yayi kunnen uwar shegu, ya zama kurma ya kuma zama makaho ga dukkan irin kiraye kirayen da kungiyar tarayyar afrika da na ECOWAS suka yi masa na da ya mutunta kundin tsarin mulkin kasar, ya sauka ayi zabe amma Tandja ya toshe kunnensa yaki sauraron kowa. Hatta tallafin da kasashen Africa da na tarayyar turai ke ba Nijar sun dakatar da bayarwa amman haka duk bata girgiza Tandja ba, bai sa ya canja gurguwar shawarar dasu dan Dubai suka bashi ba nayin tazarce.
Wani babban abin ban haushi shine yadda Tandja yaki mutunta manzon da kungiyar tattalin arzikin kasashen afrika ta yaamma ta tura zuwa Nijar don kawo karshen dambarwan siyasar da ta ki ci taki cinyewa, Tandja yayi kunnin uwar shegu yaki maida hankali kan tataunawar da akeyi da ‘yan siyasar kasar don kawo maslaha acikin lamarin. To yau dai mai faruwa ta riga ta faru, duk abinda za’a fada sai dai ya zama labari kawai. Ai dama an ce duk wanda ya shiga motar kwadayi, to la shakka ba zai sauka ako ina ba face tashar wulakanci.
Yaushe wai zamu zauna a Afrika mu kasa warware matsalolin siyasar dake damunmu har sai mun jira sojoji sun shiga tsakani? Yau da Tandja ya tsare mutuncinsa ya sauka cikin girma da arziki da ya shiga cikin kundin tarihin Nijar da ma duniya baki daya cewa yayi mulkin Nijar har sau biyu kuma ya kamala sumul. Amman yau fa? Sai dai ace Tandja wanda sojoji suka kifar da gwamnatinsa sakamakon yin tazarce da karfi da yaji, ko kuma ace sakamakon jefa kasar da yayi a yanayin rudani na siyasa, kamar dai yadda kakakin wadanda suka yi juyin mulkin kanar Abdulkarim ya bayyana ma manema labarai cewa sun yanke karbar mulkin ne sakamakon halin rudani na siyasa da ksar ta samu kanta ciki. Zanga zangar da al’ummar Nijar kuwa sukayi ranar Asabar, kwana biyu bayan hambarar da gwamnatin Tandja don yin mubayi’a tare da nuna goyon bayansu ga gwamnatin mulkin soja ya nuna a fili cewa al’ummar Nijar sun gaji da mulkin da Tandja ke musu amman shi yayi keke yana son ya nuna ma duniya cewa in bashi ba to babu mai iya mulkin Nijar.
Yau dai ragon da Tandja ya bayyana ma ‘yan jarida cewa an yankata kuma baza ta tashi ba to ta tashi. Wata kila ta keya Tandja ya yanka ragon ko a bindi ya yanke shi. Dama ai ance duk wanda baiji bari ba to zaiji hoho. Wannan shine sakamakon kin bin dokokin mulkin Nijar da Tandja yayi, tare da kin amsa dukkan irin kiraye kirayen da kasashen duniya sukayi masa na da ya mutunta mulkin dimokuradiyya ya sauka tunda wa’adinsa ya kare amman yaki ji. Fatarmu dai shine wadan nan sojoji suyi mulkin adalci kuma su gagguta maido da gwamnatin farar hula ta hanyar gudanar da zabe sahihi,ingantacce,tsarkakke kuma karbaben ga al’ummar Nijar. Don haka wannan abin kunya da ya faru da Tandja Mamadou ya kamata ya zama darasi da kuma hannunka mai sanda ga sauran takwarorin Tandja na nahiyar Afrika masu son dawwama a mulki ko ta wani rin hali, domin dai ance idan gemun dan uwanka ya kama da wuta, to ka shafama naka ruwa.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.

Thursday, January 28, 2010

CONFERMENT OF SARDAUNAN KANO ON GOV. SHEKARAU


The conferment of sardaunan kano on Mallam (Dr) Ibrahim Shekarau the executive governor of kano state by Emir of kano Alhaji (Dr) Ado Bayero is a plus to the political profile of Mallam Shekarau. However, the conferment of this tittle to Shekarau generates a lot of comments within and outside the state. While some are saying it’s indeed a plus to his Excellency’s political carrier and are rejoicing with him, others are seeing it in the other way round.

Definitely, whatever it is, the Emir of kano make a wiser decision by chosen Mallam Ibrahim Shekarau as sardaunan kano and at the right time, especially taking into consideration the way Mallam Shekarau is continuously transforming and developing the state and its people in different forms.

Foristance, Tamburawa water dam constructed/built by Mallam Shekarau is second to none in Africa, has bring an end to the scarcity of water suffered by the good people of kano state for several years, employment opportunity to youths, helping the physically challenged ones, the less privileges and expansion of the major roads in the city which is currently going on so as to reduce the rate of congestion in the city and also to enhance the commercial activities of the state-also in the past two months, people of kano state experienced or start experiencing uninterrupted power supply. All these are development recorded under Shekarau’s administration.

Dedicating himself tirelessly to the service of humanity and giving everyone his due right irrespective of religious, political or tribal differences, sacrifice, God-fearing, selfless service and many other things are what earned Mallam Ibrahim Shekarau the tittle of sardaunan kano. Because even some states in this country testified the kind of transformation that kano state has recorded and are still achieving under the administration of Mallam Shekarau, and as such he was awarded with the traditional tittle of Onwa Na-Etiri oha1 na Ehaalumono from southern part of this country. This shows that his commitment (Mallam Shekarau) to serve the good people of kano state and indeed Nigeria as a whole is appreciated. Truly, the executive governor of kano state, Imam of societal reorientation, deserves to be called magajin sardaunan Sokoto because his commitment to the service of humanity and development of his people is similar to that of late sardaunan Sokoto Alhaji Sir Ahmadu Bello.

It is well known to everyone that since after it’s creation, kano state did not witness rapid transformation and development like in the seven years ago under the excellent innovative leadership of Mallam Ibrahin Shekarau- This is a blessed development and opportunity that people of kano state should be proud of and thanks the almighty God for blessing them with a governor that pay attention to nothing but development and upliftment of his people. Therefore, his Excellency Mallam (Dr) Ibrahim Shekarau, Imam of societal reorientation, garkuwan Ilimi, sardaunan kano, Onwa Na-Etiri oha1 na Ehaalumono, magajin sardaunan Sokoto needs nothing from people of kano state than prayers for God to grant him his wishes and give him the opportunity to deliver the mandate given to him successfully by people of kano state. We pray that Almighty Allah in His own will and power will one day give Governor Shekarau an opportunity to serve the country at large insha Allah.
Lastly, I am concluding this paper with a prayer, seeking refuge from the Almighty from all evils and harmful acts. May he also be our guardian in all our endeavours, ameen.

Sunday, January 3, 2010

Relationship Between America And rest of the World:

THE RELATIONSHIP BETWEEN U.S.A AND THE REST
OF THE WORLD
The accusation by the American Government on Faruq Umar Abdul-Mutallab, who happen to be a Nigerian, for attempting to bombard a plane in America on the 25th Day of December, 2009, remain the subject of discussion throughout the world, especially the way and manner adopted by both the local and international mass-media in disseminating it, almost everyday.
Similarly, it is of common knowledge and undisputed fact that America is second to none when it comes to the issue of concoction and dissemination of propaganda. Almost always, their (America) mission is to create tension and emotional disorder in the minds of innocent fellow human beings.
Assuming but not conceding that the accusation against Faruq is true, then it is now a time for America to sit and cogitate on why these series of attacks and attempted attacks were aimed at it alone. Because, a wise man says that there can never be a smoke without fire. Obviously, the America and American government should ask theirselve why the attacks were always targeted at America not for instance, Germany, Australia, Denmark, China, Russia, Japan, Togo, or Ghana? Why America is the final bus-stop for everybody with all sorts of grievances, dissatisfactions, and disappointment of life? What kind/sort of relationship exists between America and this kind of people or the world at large? These are few out of many questions that America needs to find out their answers.
However, nothing is new it has been for long time that America and its allies considered us as terrorists. But at this juncture, I am strongly and courageously saying that it is unwise and unjust for America and the western-world to consider the religion of Islam as a religion of terror or the one that support terrorism just because of what Faruq did. This is because some people have already related his alleged act (if time) to the religion of Islam.
I sincerely see no nexus between his alleged act and the religion of Islam which is the religion of peace.
Common sense, good sense, and natural justice can never allow the alleged act to serve as a yardstick for jumping into conclusion that every Muslim is a terrorist.
The worst part of it is how some of the so-called “SENATORS” and “REP-MEMBERS” in America are calling for an immediate transfer of Faruq to their illegal prison in GUANTANOMO. This clearly translates how illiterate they are on what HUMAN RIGHTS are all about. They wittingly ignored the fact that they have a better person to send there but not Faruq. Though, I am not holding a brief for Faruq, but they should know that BUSH W. GEORGE is the rightful person that supposes to be in Guantanomo for the illegal, criminal, and inhuman acts he perpetrated while he was the American president.
He was the brain behind the lost of many innocent lives in Iraq and Afghanistan. To crown it all, the said BUSH is the real causative of all sorts of catastrophic and calamities that are befalling America now a day.
Those law-makers should also be reminded that in almost all the criminal justice in the world, the golden and guiding principle is that AN ACCUSED PERSON IS PRESUMED TO BE INNOCENT UNLESS AND UNTIL HE IS FOUND (PROVED) TO BE GUILTY BY A OCURT OF LAW (and of competent jurisdiction not court of public opinion). Though, his accuser(s) claimed that he confessed or admit the accusation, this is immaterial because we have not yet hear from him.
At this point, the Nigerian government should as a matter of urgency send their officials to America so that they can work in collaboration with a view of doing justice to the issue. This is because up to the time I am writing this paper, I have not seen the Faruq saying a word over the issue in any electronic-media neither hear his voice but always America said this and said that. Until we hear from him or watch his video, we will never agree with the said propaganda.
I have no iota of doubt in my mind that had it been that Faruq is an American the issue would have been forgotten by now. What they will do is nothing more than to declare that the accused person is suffering from mental disorder and nothing more or less. As such, it is mandatory for the Nigerian government as a sovereign country to involve itself in this serious issue to see that the rights of its citizen are not unjustly being infringed and simultaneously to prevent its unrefutable image from the rest of the world.
Lastly, I am concluding this paper with a prayer, seeking refuge from the Almighty from all evils and harmful acts. May he also be our guardian in all our endeavours, ameen.
By:
MUNTAKA ABDUL-HADI DABO,
ANGUWAR FATIKA,ZARIA.
write2muntaka@yahoo.com

Dangantakar Amurka da Kasashen Duniya


Tun bayan da mahukuntan kasar Amurka suka zarigi dan Nijeriyan nan mai suna Farouq Umar abdulmutallab da yunkurin tada bom a sararin samaniyar kasar Amurka ranar 25-12-09 hankalin duniya baki daya ya karkata kan wannan, musamman ma ganin yadda kulli yaumin kafafen yada labarai na gida da na waje ke ci gaba da ruruta yadda lamarin ya auku.
Da farko dai kada ayi tuya a manta da albasa, kowa yasan cewa duk duniya babu kasar da ta shahara kuma ta kware wajen kago labaran karya da zasu dauki hankalin duniya tare da tada zukatan al’umma kamar kasar Amurka. Kullum su burinsu shine kawo rashin kwanciyar hankali a duniya da kuma musguna ma wadanda basu jiba basu gani ba. Sa ma ace wannan zargi da ake ma Umar Farouq gaskiya ne, koda yake ana nan ana binciken don gano gaskiyar lamarin, idan har zargin ta tabbata to wannan wani abu ne da ya kamata kasar Amurka ta zauna tayi ma kanta karatun natsuwa gami da tunani tare da tambayar kanta mai yasa irin wadannan aikin ta’addanci ke faruwar a kasar ta kawai? Don me yasa ba aje kasar Germany, Australia, Denmark, China, Russia, Japan, Togo, ko Ghana an kai irin wadannan hare haren ba? Me yasa kowa idan ya dauko fitintununsa baya sauke su ko ina sai Amurka? Wani irin hulda ko dangantaka ke tsakanin wadannan mutane ko duniya baki daya da kasar Amurka? Wadannan kadan ne daga cikin dimbin tambayoyin da ya kamata kasar Amurka taba kanta amsa.
Ko da yake, duk wadannan abubuwan da Amurka da sauran ‘yan kanzaginta keyi ba sabon abu bane domin kuwa sun dade suna mana kallon ‘yan ta’adda. Bai dace Amurka da sauran kasashen masu jajayen kunnuwa su rika kallon addinin musulunci a matsayin addinin ta’addanci ba sakamakon abinda ake zargin Umar Farouq da aikatawa. Don kuwa tuni wadansun su suka rika danganta wannan lamari da koyarwar addinin musulumci. Gaskiya addinin musulunci kowa yasan cewa addini ne na zaman lafiya wanda kuma baya koyar da duk wani aiki na ta’addanci ko makamantan hakan, kuma kada wannan abu ya zama mizani na daukan dukkan musulmai ‘yan ta’adda ko ‘yan Nijeriya arika masu kallon ‘yan ta’adda.
Wani abin ban haushi da takaici shine yadda wasu sanatoci da ‘yan majalisar wakilai na Amurka da basu san hakki da ‘yancin bil’adama ba suke kiran da a gaggauta tura Umar Farouq zuwa sansanin GUANTANAMO don azabtar dashi, domin acewarsu Farouq cikakken dan ta’addane wanda ya kamat ya fuskanci hukunci. Amma abin tambaya a nan shine, shin wadannan masu wanna kira na atura Farouq zuwa GUANTANAMO basu san cewa suke da babban dan ta’adda da ya dace a garzaya dashi zuwa wannan sansanin ba? Idan basu sa niba to ga sunansa, Bush W. George shine cikakke kuma babban dan ta’addan duniya, domin kuwa yayi sanadiyyar salwantan rayuka bila a dadun a kasashen Iragi da Afghanistan. A takaice dai, duk wata irin fitina dake samun Amurka Bush shine ya haifar sakamakon yadda huldar dangantakar Amurka da sauran kasashen duniya yayi tsami cikin tsawon shekaru takwas din da yayi yana mulkin kama karya a kasar, yayi sanadiyyar mutuwan al’umma a ko ina cikin duniya. To wanna ba laifi ne da yakamata a hukunta wanda ya aikata suba? Farouq fa zarginsa akeyi wanda haryanzu ba a tabbatar da cewar ko wannan zargin gaskiya ne ba, duk kuwa dacewan munji wai bayanai daga Amurka na cewa Farouq ya masa laifin da ake zarginsa dashi amman mu haryanzu bamuji daga bakinsa ba. Don haka baza mu gaskanta wanna labarin ba, domin munsan Amurka na iya zama ta shirya kowani irin labarai don jan hankalin al’ummar duniya.
Ya kamata mahukuntan Nijeriya su tura nasu jami’an zuwa kasar Amurka ayi binciken tare dasu don ganin anyi adalci a rahoton da za’a bayar. Kada su zauna su nade hannayensu su jira Amurka ta rubuta mana sakamakon bogi suce shine sakamakon binciken da suka gudanar. Domin har yanzu sai dai muji kafafen yada labarai na fadin cewa bayanai da suka fito daga Amurka sunce Farouq yace abu kaza ko ya fadi abu kaza wanda har yanzu ba’a taba sa mana muryansa munji lokacin da yake furta wadannan kalamai ba ko asa mana hoton bidiyo da aka dauka lokacin da ake yi masa tambayoyi ba, don haka duk abinda za’a fada mana soki burutsu ne kawai, baza mu taba yarda ba sai munji daga bakinsa. Wallahi yau da dan Amurka ake zargi ya aikata wannan ta’adi da yanzu an manta da maganan. Don Amurka ba zata taba yarda ayi binciken da zai sa a Gano tare da ladabtar da dan kasarta akan irin wadannan laifuffuka ba. Zatayi duk mai yiwuwa wajen ganin maganan ya mutu ko ta halin kaka. In kuma ya zama dole sai an gudanar da binciken, to zuwa zatayi ayi binciken tare da ita, wanda kuma kowa yasan cewa ba binciken za’a yiba, sune zasu zauna su tsara mana abinda za’a fadawa duniya wanda bai wuce daga karshe ace mana wanda ake zargin yana da tabin hankali ba. Don haka ya zama dole gwamnatin Nijeriya ta shiga cikin lamarin nan don kare hakkin yaron nan da kuma kare mutuncin ta a idon duniya don ganin ba’ayi amfani da wannan dama ba wajen musgunama ‘yan Nijeriya dake kasashen waje ko masu muradin fita nan gaba.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.

Monday, December 28, 2009

SHEKARA DAYA BAYAN KISAN PALASDINAWA: INA AKA KWANA?

Harin bama bamai da israela ta kaddamar a karshen watan disamban shekarar 2008 zuwa farkon shekarar 2009 a yankin zirin Gaza ya cika shekara daya yanzu haka ba tare da an gurfanar da wadanda suke da hannu a cikan wannan mummunar ta’asar ba a kotun hukunta masu laifukan yaki na duniya. Wannan fitina da ta afku abin ayi tir da kuma Allah wadai da ita ne. Domin kuwa yakin ya jefa palasdinawa cikin halin kaka nakayi na rashin abinci, ruwan sha, wutar lantarki da dai sauransu baya ga hasaran rayuka da dukiyoyi, duk a sakamakon amfani da makamai masu kazamin guba da bani yahudun sukayi. Hatta harkar sadarwa ta yanke a lokacin saboda rashin wutan lantarki, wadanda kuma suka jikkata a lokacin basu samun cikakken kula a asibiti ba, wanda hakan yasa suka mutu daga karshe. Wannan danyen aiki da Isra’ila ta aikata a Zirin Gaza ya kai intaha, domin kuwa yayi sandiyyar maida yara da dama marayu, wasu matan sun rasa mazajensu, a wani bangaren kuma maza sun rasa matayensu da ‘ya ‘yansu, gidajen jama’a sun salwanta da kuma dukiyoyi inda jama’a da dama suka rika gararanba a gari suna neman wajen tsugunawa duk a sanadiyyar wannan kazamin fada.
Wani abin ban haushi da takaici shine yadda majalisar dinkin duniya ta nuna halin ko inkula ga mummunar ta’adin da Isra’ila ta aikatawa palasdinawa, tayi gum taki cewa komai. Hakan kuwa bai dace ba domin kuwa majalisar dinkin duniya tana da cikakken ikon tsawatarwa Isra’ila don dakatar da lugudan wuta da harin bama bamai da takaiwa palasdinawa, amma taki yin hakan. Yanzu ya fito fili kuma kowa ya fahimta, musamman ma ganin yadda yar sandan duniya wato kasar amuruka taki cewa uffan a lokacin da Isra’ila ta rika yima palasdinawa kisan kiyashi, da kuma halin ko oho da majalisar dinkin duniya ta nuna cewa suna da ra’ayi akan lamarin. Domin kuwa, hakkin majalisar dinkin duniya ne ta sasanta kasashen cikin lumana da diflomaciyya, amman taki yin hakan ta zurawa Isra’ila ido ta ci karenta ba babbaka a Zirin Gaza. Akwai bukatan majalisar dinkin duniya ta sake salon yadda take tafiyar da lammuranta, ma’ana ta rikayin adalci da kuma cin gashin kanta ba sai ta jira wata kasa ta bata umurni ba. Kodayake, kin daukan mataki da majalisar tayi a kan Isra’ila wani umurni ne daga Amurka a karkashin mulkin kama karya na George Bush. Domin kuwa Amurka ce ke tafiyar da harkokin majalisar dinkin duniya, har ila yau hedkwatar majalisar na kasar Amurka, don haka shiyasa Amurka ke taka rawar da taga dama sakamakon sake da nuna rashin iya aiki da majalisar dinkin duniya tayi.
Yin biris kuwa da kasashen larabawa sukayi kan wannan lamari, suka ki taimakawa palasdinawa don tsoron kada Amurka tasa masu takunkumi ko ta kirasu yan ta’adda wallahi yazamo babban abin kunya da kuma hasara garesu. Domin kuwa Isra’ila ba ita kadai ta aikata wannan kisan kiyashin da tayi a zirin Gaza ba, tasamu taimako amma su larabawa sunkasa taimakawa yan uwansu don neman suna a gun Amurka. Tabbasa dole a jinjinawa kasashen masar da faransa kan namijin kokarin da sukayi lokacin da yakin yaki ci yaki cinyewa, domin kuwa sune sukayi kokari wajen ganin an kawo karshen wannan zibda jini da akayi. Hakika kiran dakatar da ruwan bama bamai a zirin Gaza da kasashen biyu sukayi a lokacin da Isra’ila ke faman lugudan wuta a yankin zirin Gaza, dakuma kiran a zauna a teburin shawarwari abin a yaba masu ne matuka gaya.Domin kuwa hakan ya haifar da da mai idon inda Isra’ila ta tsagaita wannan danyen aiki data kwashe kwana da kwanaki tana aikatawa a zirin Gaza. Babban abin ban mamaki shine yadda majalisar dinkin duniya da kuma wadanda ke da alhakin gurfanar da masu laifin yaki a kotun duniya sukayi kememe sukaki sammacin wadanda suka jagoranci wannan ta’asa a Zirin Gaza, amman sai gashi a watan maris na wannan shekarar ta 2009 kotun masu laifukan yaki dake birnin Hague tayi sammacin shugaban kasar Sudan Omar Hassan Al-bashir ya gurfana a gabanta don amsa laifukan kisan kare dangi a Sudan da ake zargin wai yana da hannu dumu dumu a cikin. Sanin kowa ne, sai dai aki fadin gaskiya, rikicin kasar Sudan bakowa ya haifar dashi ba illa kasar Amurka, sakamakon rashin samun damar ta taka rawa kan al’amurar man fetur da allah ya albarkaci kasar Sudan dashi.
To babbar ayar tambaya itace, shin majalisar dinkin duniya da kotun kasa da kasa dake hukunta msau laifukan yaki na tsoron cafkewa da kuma gurfanan da wadanda suka aikata kisan kare dangi a zirin Gaza ne? ko kuwa su ‘yan lele ne baza a yi sammacinsu don su fuskanci shari’a ba? Wani hujja suke dashi nakin gurfanar da wadannan azzalumai a gaban kuliya? Shin ta hakane za a rika kawo karshen rashin jituwa tsakanin kasashen masu gaba da juna ta kin ladabtar da mai laifi don ya zama darasi ga ‘yan baya? Wani mataki majalisar dinkin duniya take dauka a halin yanzu kan ci gaba da shiga yankin palasdinawa da bani yahudu keyi don ganin wannan mummunar rikici tsakanin bangarorin biyu bai sake afkuwa ba? Wadannan kadan ne daga cikin dimbobin tambayoyin day a kamata majalisar dinkin duniya ta amsa don sanin matsayin al’ummar palasdinawa a idonta dama duniya baki daya.
Hakika al’ummar palasdinawa sun shiga wani hali na kunci, rashi da kuma tausayi duk sakamakon wannan bala’in da Isra’ila ta jefasu ciki. Don haka muna tayasu addu’ar allah ya dada karesu da karewarsa, ya tsaresu da tsarewarsa, ya kuma fidda su daga cikin wannan halin kunci da suka samu kansu a cikin skekara daya da ta wuce tare da fatan Allah SWT zai mayarmasu da dukiyoyin da sukayi asara a wannan lokaci.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.

Friday, December 18, 2009

FOUR YEARS REMEBRANCE...

December 18, 2005 will remain unforgettable to our family. It was on the early hours of that fateful day that our beloved father Justice Abdul-Hadi Dabo left this sinful world to rest in the bosom of Allah. Four years has gone now, but you are still fresh in our memory as if it was just yesterday you departed.
You came to earth with nothing and left with nothing, but rather left a legacy that others resisted. You triumphed over hard work which has been our watchword.
The eyes cannot see you, the nose cannot sense you, the mouth neither can talk to you, but what about the ears, they both cannot hear you...
Prayers cannot awaken you from the deep slumber you have fallen; it will only elevate you to the most high and bury your past earthly mistakes.
It's our prayers that the Almighty Allah will have mercy on your soul, together with all the muslims who died before you right from the time of prophet Adam (A.S). May He afford us the will and patience to pray for them and bless us with those who will pray for us when we die...
May Allah's infinite mercy shower you an infinitum forgiveness of your past mistakes. May He also grant you the eternal rest. Ameen... Continue to rest in peace till we meet in ALJANNA FIRDAUSI...

Friday, December 4, 2009

YABO GA RUNDUNAR YAN SANDAN JIHAR KADUNA

Yabon gwani akace ya zama dole, kuma kowa yayi aiki na gari dole a yaba masa. Hakan yasa ya zama dole a jinjina ma hukumar ‘yan sandan Jihar Kaduna karkashin jagoranci kwamishinan ‘yan sanda agogo sarkin aiki Alhaji Tambari Yabo Muhammed, ganin yadda jami’an shi ke aiki tukuru ba dare ba rana don ganin sun fatattaki miyagun da ke addabar jihar Kaduna dakuma kare rayuka da dukiyar al’ummar ta jihar Kaduna.
Murkushe shirin fashi da makami a jajibirin sallah da ta gabata a hanyoyin Kaduna zuwa Birnin Gwari da kuma Kaduna zuwa Zaria da ‘yan sanda sukayi abin a yaba masu ne matuka, domin kuwa baicin daukin gaggawa da jami’an suka kawo da Allah kadai yasan irin barnar da ‘yan fashin zasu yi a hanyoyin ganin cewa jama’a da dama na ribibin komawa kauyukansu don yin sallah tare da iyalansu dakuma ‘yan uwa da abokan arziki. Harkar tsaro dai a jihar Kaduna kullum sai kara karuwa takeyi saboda kyakkyawar kulawa da maigirma gwaman jihar Alhaji Namadi Sambo yaba fannin tsaro tare da samar da kayan aiki. Domin kuwa jihar Kaduna ta zarce sauran takwarorinta a fannin tsaro, don haka ya zama dole a yabama wannan hubbasa da mai girma gwamna keyi don ganin tsaro ya inganta a jihar Kaduna. Suma ‘yan sanda dole a dada yaba masu ganin yadda suka dage wajen dakule duk wata hatsaniya da shirin aikin ‘yan zauna gari banza da bata gari keyi don ganin Jihar Kaduna ta zama abin koyi ga suaran jihohi.
Don haka ya kamata hukumomin da abin ya rataya a kansu su dada samar da kayan aiki ga jami’an tsaro don suji dadin sauke nauyin daya rataya a kansu a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, kuma a ci gaba da basu horo tare da turasu kwasa kwasai cikin gida da kasashen ketare don dada gogewa a aikinsu da kuma yin gogayya da takwarorinsu na waje. Sukuma jama’an gari suci gaba da ba ‘yan sanda hadin kai a duk lokacin da bukatar hakan ta taso tare da basu muhimman bayanai kan duk wani mutum da basu gamsu da take takensa ba. Da fatan sauran jihohi zasuyi koyi da jihar Kaduna don samar da cikakken tsaro a jihohinsu.

Sunday, November 22, 2009

Hukumar EFCC: Ba girin girin ba....


Shugabar hukumar EFCC madam faida waziri ta fito tayi wasu maganganu da suka ja hankalin ‘yan kasar nan da dama kan malam Nuhu Ribadu, ciki kuwa hardani. Duk da cewa banso cewa komai ba kan maganganun da tayi, amman ya zama dole don ganin yadda ta rika hawa tanasauka gami da kushe duk wani irin nasara da malam Nuhu Ribadu ya samu lokacin aikinsa. A sanin ‘yan Nijeriya dai babba da yaro, tsoho da matashi ya san cewa hukumar EFCC na yaki ne da masu almubazzaranci da ta’annati da dukiyar kasa ne. yaki da masu wawushe dukiyar talakawa zuwa aljihunansu yana daya daga cikin ayyukan hukumar na EFCC kamar yadda kowa ya sani. Don haka yin aiki akasin haka ya sabama manufofin wannan hukumar.
Amma da dukkan alamu wannan hukuma ta EFCC a halin yanzu bata aikinta yadda ya kamata, domin kuwa shugabar hukumar tayi wani maganganu wadanda suka bada mamaki matuka, domin inda wani ne yayi wannan Magana ba ita shugabar EFCC dinba, to a iya cewa saboda baisan aikin hukumar ta EFCC ne yasa haka. Madam Farida Waziri ta fito fili ta shaidawa duniya a wani shiri da akayi da ita a sashen hausa na muryra Amurka mai suna sai bango ya tsage, ranar 19-11-2009 cewa “ muna neman malam Nuhu Ribadu ne saboda ya je yana bata min suna da sunan Nijeriya a kasashen waje saboda yanajin haushina, kuma yace duk shugabannin Nijeriya masu rashawa ne……..” wannan dalilai ne yasa a cewar madam Waziri ya zama tilas ga hukumarta ta damke malam Nuhu Ribadu in har sunyi tozali das hi. Amman da akayi mata tambayar cewa mai zaisa baza su tuhumi Ibrahim Lamorde ba, tsohon shugaban hukumar ta EFCC daya gaji malam Nuhu Ribadu kafin zuwan ita madam Waziri, gogar taku sai ta sake kada baki tace “ ai shi Lamorde ba za mu kamashi ba ko mu bincikeshi ba domin yayi shiru bai zagi kowa ba, shikuwa Ribadu sai bata min suna kawai yakeyi domin an bani mukaminsa” wadannan kalamai na Madam Waziri cike suke da ban mamaki, domin kuwa bai kamace ta a matsayinta na wacce tasan aikin taba (in harta sanin ma kenan) ta fito tana irin wadannan maganganun cewa hukumarta zata kama Nuhu Ribadu ne kan wai yana bata mata suna! Wannan bayanai nata na nuni da cewa kenan zasu kama Ribadu ba kan yana da laifin cin hanci da rashawa ba ke nan. To, abin tambaya a nan shine, shin hukumar EFCC ta daina yaki da cin hanci da rashawa ne ta koma farauta masu batama Nijeriya suna a kasashen duniya? Lallai wannan tambaya ne da madam Waziri ya kamata ta amsashi don ‘yan Nijeriya su san alkiblar da EFCC ta nufa yanzu idan ta canza ne daga damkewa da cafko masu karya tattalin arzikin kasa.
Har ila yau, madam Waziri tayi ikirarin cewa malam Nuhu Ribadu ya shirya manakisan hanasu yin wani taro da sukayi a can kasar Amurka. Don Allah jama’a kuji irin wannan Magana fa, ta yaya mutumin daba dan kasar Amurka ba zaiyi tattaki zuwa Amurka har ya tara yan zauna gari banza don su hana madam Waziri da sauran tawagarta gudanar da taronsu? Amurka fa bata da ‘yan zauna gari banza kamar yadda ake dasu a Nijeriya, idan ma akwaisu ta ya Ribadu zai iya tarasu domin su hana wannan taron da madam Waziri tayi ikirarin cewa yayi makarkashiyar hanawa?
Ya kamata madam Waziri taji tsoron Allah tayi aiki tsakani da Allah, idan mutum baici ba bai shaba, to kada a rika yi masa bita da kulli. Kada a dauki tsanan duniyannan a daura masa idan anga yana samun ci gaba a rayuwarsa. Ba zai kyautu ba in har madam Waziri tayi amfani da kujeranta don musgunama malam Nuhu Ribadu kan laifin da baiji ba bai gani ba. Gaskiya dai daya ne, kuma daga kinta sai bata. Kowa a kasarnan yasan irin yadda wannan bawan Allah Ribadu ya sadaukar da kansa ya bautawa kasarna, don haka in har baza’a sakamasa da alhairi ko a yaba masa ba, to bai kamata a tsine masa ba ko a musguna masa ba. Wallahi kasarnan na bukatar irin su Ribadu don kaiwa ga tudun mun tsira, amman saboda yanayin azzaluman shugabannin da muke dasu wadanda basa son gaskiya hakan yasa da wuya a yanzu a sake ba Ribadu dammar ya zo yaci gaba da bautawa kasarnan kamar yadda yayi a baya don samun ci gaba. Domin kuwa tun bayar barinsa hukumar EFCC, har yanzu babu wasu kwararan nasarori da aka samu kaarkashin hukumar kamar yadda aka samu a lokacinsa.
Hakika ya kamata madam Waziri ta zauna tayi ma kanta karatun natsuwa ta kuma rika banbance tsakanin gaskiya da karya a al’amuran aikinta na shugabar EFCC. Dan gane kuma da bayanin da tayi cewa Ribadu na da matsala da hukumar da’ar ma’aikata, to ai wannan ba lamari ne da ya shafeta ba domin ba’a hukumarta abin yake ba, don haka shiru shine nata ta barshi su karata da hukumar da’ar ma aikata. Har yanzu ‘yan Nijeriya na kaunar Ribadu saboda yadda ya sadaukar da kansa yayi aiki tukuru, kuma suna fatan watan wata rana gaskiya zatayi halinta, duk wannan bita da kulli da akeyi masa zata kare. Fatarsu shine kasarnan ta samu shugabanni na gari masu son gaskiya wadanda tafiyarsu zatayi daidai da irin tafiyar su malam Nuhu Ribadu adali kuma haziki, kuma Allah ya kubutar da shi daga azzaluman mutanen da suka sashi a gaba.
Allah yayi mana jagorancin a dukkan ayyukanmu na alhairi. Kuma yaci gaba da karemu gami da tsaremu dayi mana Katanga ga dukkan abin da muke shakkunsa na zahiri da badili, amin.

Friday, November 20, 2009

NADA GWAMNA IBRAHIM SHEKARAU A MATSAYIN SARDAUNAN KANO: RIBAR SIYASA?


Tuwon girma akace miyan nama inji masu iya Magana, kuma yabon gwani akace ya zama dole. Nadin mai girma Gwamnan Kano mallam Ibrahim Shekarau a matsayin sardaunan Kano da mai martaba sarkin Kano Alhaji Dakta Ado Bayero yayi masa ya jawo ce-ce-ku-ce a ciki da wajen jihar inda wasu ke alas an barka da wannan saraudar da kaba limamin adaidaita sahu, wasu kuwa akasin hakan ne ke fitowa daga bakinsu.
Alal hakika mai girma sarkin Kano Alhaji Dakta Ado Bayero yayi kyakkyawar hange wajen zaben Mallam Ibrahim Shekarau a matsayin sardaunan Kano kuma a lokacin daya dace, musamman ma ganin yadda shi sardaunan na Kano ke ci gaba da ayyukan raya jihar gami da gina al’ummarta ta fannoni daban daban. Alal misali gina madatsan ruwa na tamburawa da akayi wanda duk nahiyar afrika babu kamarsa ya sawwake radadin azabar rashin ruwa da mutanen Kano suka dade suna fama dashi na shekara da shekarau, samar da aikin yi ga matasa, bada tallafi ga nakasassu, ga kuma fadada hanyoyin jihar da akeyi a halin yanzu don rage cunkoso a titunan garin da kuma inganta hanyoyin sufuri, sai kuma uwa uba wutar lantarki wanda yanzu haka a makwanni uku da suka wuce jihar Kano tafara samun cikakken hasken wutar lantarki a ko wane rana ba kakkautawa wanda hakan zai dada karfafa aikin masana’antu, da dai sauran ayyukan ci gaban jihar da dama.
Sadaukar da kai da yin aiki tukuru ba tare da gajiyawa ba da mai girma gwamna Mallam Ibrahin Shekarau keyi tare da baiwa kowa hakkinsa ba tare da nuna banbancin addini, siyasa ko kabila ba, gami da gina al’umma tare da yin ayyuka don ci gaban jihar Kano dama Kasa baki daya sune suka kai ga baiwa limamin adaidaita sahu sarautar sardaunan Kano. Domin kuwa, hatta jihohin kasar nan sun yaba da ayyukan gina kasa da mai girma gwamna Shekarau keyi wanda hakan yasa aka bashi sarautar Onwa Na-Etiri oha 1 na Ehaalumono a kudancin kasar nan. A zahirin gaskiya, mai girma gwamnan kano kuma limamin adaidaita sahu ya cancanci a kirasa da magajin sardaunan sokoto, domin kuwa kyawawan halayensa na kishin jama’arsa da son ci gabansu yayi daidai dana marigayi sardaunan sokoto Alhaji Sir Ahamadu Bello.
Sanin kowa ne Jihar Kano tun bayan kirkirota bata samu cigaban da ta samu a shekaru shida da suka wuce ba karkashin jagorancin adalin gwamna Dakta Ibrahim Shekarau. Wannan kuwa wani babban nasara ne da al’ummar jihar Kano ya kamata suyi tunkaho dashi, kuma suyi godiya ga Allah madaukakin Sarki daya tarfawa garinsu nono ya albarkace su da gwamna mai son cigabansu musamman ma ganin yadda a kullum sai kara kwasan ribar dimokuradiyya sukeyi ba kakkautawa. Don haka babu abinda mai girma gwamna Mallam Dakta Ibrahim Shekarau limamin adaidaita sahu, garkuwan Ilimi, sardaunan Kano, Onwa Na-Etiri oha 1 na Ehaalumono, kuma magajin sardaunan sokoto ke bukata face ayi masa addu’ar Allah yaja kwana kuma ya biya masa dukkan bukatunsa na alkhairi da yasa a gaba kuma ya basa ikon sauke nauyin da ya rataya a kansa tare kuma da Addu’ar ALLAH YA KAI DAMO GA HARAWA! Amin.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.