Monday, December 28, 2009

SHEKARA DAYA BAYAN KISAN PALASDINAWA: INA AKA KWANA?

Harin bama bamai da israela ta kaddamar a karshen watan disamban shekarar 2008 zuwa farkon shekarar 2009 a yankin zirin Gaza ya cika shekara daya yanzu haka ba tare da an gurfanar da wadanda suke da hannu a cikan wannan mummunar ta’asar ba a kotun hukunta masu laifukan yaki na duniya. Wannan fitina da ta afku abin ayi tir da kuma Allah wadai da ita ne. Domin kuwa yakin ya jefa palasdinawa cikin halin kaka nakayi na rashin abinci, ruwan sha, wutar lantarki da dai sauransu baya ga hasaran rayuka da dukiyoyi, duk a sakamakon amfani da makamai masu kazamin guba da bani yahudun sukayi. Hatta harkar sadarwa ta yanke a lokacin saboda rashin wutan lantarki, wadanda kuma suka jikkata a lokacin basu samun cikakken kula a asibiti ba, wanda hakan yasa suka mutu daga karshe. Wannan danyen aiki da Isra’ila ta aikata a Zirin Gaza ya kai intaha, domin kuwa yayi sandiyyar maida yara da dama marayu, wasu matan sun rasa mazajensu, a wani bangaren kuma maza sun rasa matayensu da ‘ya ‘yansu, gidajen jama’a sun salwanta da kuma dukiyoyi inda jama’a da dama suka rika gararanba a gari suna neman wajen tsugunawa duk a sanadiyyar wannan kazamin fada.
Wani abin ban haushi da takaici shine yadda majalisar dinkin duniya ta nuna halin ko inkula ga mummunar ta’adin da Isra’ila ta aikatawa palasdinawa, tayi gum taki cewa komai. Hakan kuwa bai dace ba domin kuwa majalisar dinkin duniya tana da cikakken ikon tsawatarwa Isra’ila don dakatar da lugudan wuta da harin bama bamai da takaiwa palasdinawa, amma taki yin hakan. Yanzu ya fito fili kuma kowa ya fahimta, musamman ma ganin yadda yar sandan duniya wato kasar amuruka taki cewa uffan a lokacin da Isra’ila ta rika yima palasdinawa kisan kiyashi, da kuma halin ko oho da majalisar dinkin duniya ta nuna cewa suna da ra’ayi akan lamarin. Domin kuwa, hakkin majalisar dinkin duniya ne ta sasanta kasashen cikin lumana da diflomaciyya, amman taki yin hakan ta zurawa Isra’ila ido ta ci karenta ba babbaka a Zirin Gaza. Akwai bukatan majalisar dinkin duniya ta sake salon yadda take tafiyar da lammuranta, ma’ana ta rikayin adalci da kuma cin gashin kanta ba sai ta jira wata kasa ta bata umurni ba. Kodayake, kin daukan mataki da majalisar tayi a kan Isra’ila wani umurni ne daga Amurka a karkashin mulkin kama karya na George Bush. Domin kuwa Amurka ce ke tafiyar da harkokin majalisar dinkin duniya, har ila yau hedkwatar majalisar na kasar Amurka, don haka shiyasa Amurka ke taka rawar da taga dama sakamakon sake da nuna rashin iya aiki da majalisar dinkin duniya tayi.
Yin biris kuwa da kasashen larabawa sukayi kan wannan lamari, suka ki taimakawa palasdinawa don tsoron kada Amurka tasa masu takunkumi ko ta kirasu yan ta’adda wallahi yazamo babban abin kunya da kuma hasara garesu. Domin kuwa Isra’ila ba ita kadai ta aikata wannan kisan kiyashin da tayi a zirin Gaza ba, tasamu taimako amma su larabawa sunkasa taimakawa yan uwansu don neman suna a gun Amurka. Tabbasa dole a jinjinawa kasashen masar da faransa kan namijin kokarin da sukayi lokacin da yakin yaki ci yaki cinyewa, domin kuwa sune sukayi kokari wajen ganin an kawo karshen wannan zibda jini da akayi. Hakika kiran dakatar da ruwan bama bamai a zirin Gaza da kasashen biyu sukayi a lokacin da Isra’ila ke faman lugudan wuta a yankin zirin Gaza, dakuma kiran a zauna a teburin shawarwari abin a yaba masu ne matuka gaya.Domin kuwa hakan ya haifar da da mai idon inda Isra’ila ta tsagaita wannan danyen aiki data kwashe kwana da kwanaki tana aikatawa a zirin Gaza. Babban abin ban mamaki shine yadda majalisar dinkin duniya da kuma wadanda ke da alhakin gurfanar da masu laifin yaki a kotun duniya sukayi kememe sukaki sammacin wadanda suka jagoranci wannan ta’asa a Zirin Gaza, amman sai gashi a watan maris na wannan shekarar ta 2009 kotun masu laifukan yaki dake birnin Hague tayi sammacin shugaban kasar Sudan Omar Hassan Al-bashir ya gurfana a gabanta don amsa laifukan kisan kare dangi a Sudan da ake zargin wai yana da hannu dumu dumu a cikin. Sanin kowa ne, sai dai aki fadin gaskiya, rikicin kasar Sudan bakowa ya haifar dashi ba illa kasar Amurka, sakamakon rashin samun damar ta taka rawa kan al’amurar man fetur da allah ya albarkaci kasar Sudan dashi.
To babbar ayar tambaya itace, shin majalisar dinkin duniya da kotun kasa da kasa dake hukunta msau laifukan yaki na tsoron cafkewa da kuma gurfanan da wadanda suka aikata kisan kare dangi a zirin Gaza ne? ko kuwa su ‘yan lele ne baza a yi sammacinsu don su fuskanci shari’a ba? Wani hujja suke dashi nakin gurfanar da wadannan azzalumai a gaban kuliya? Shin ta hakane za a rika kawo karshen rashin jituwa tsakanin kasashen masu gaba da juna ta kin ladabtar da mai laifi don ya zama darasi ga ‘yan baya? Wani mataki majalisar dinkin duniya take dauka a halin yanzu kan ci gaba da shiga yankin palasdinawa da bani yahudu keyi don ganin wannan mummunar rikici tsakanin bangarorin biyu bai sake afkuwa ba? Wadannan kadan ne daga cikin dimbobin tambayoyin day a kamata majalisar dinkin duniya ta amsa don sanin matsayin al’ummar palasdinawa a idonta dama duniya baki daya.
Hakika al’ummar palasdinawa sun shiga wani hali na kunci, rashi da kuma tausayi duk sakamakon wannan bala’in da Isra’ila ta jefasu ciki. Don haka muna tayasu addu’ar allah ya dada karesu da karewarsa, ya tsaresu da tsarewarsa, ya kuma fidda su daga cikin wannan halin kunci da suka samu kansu a cikin skekara daya da ta wuce tare da fatan Allah SWT zai mayarmasu da dukiyoyin da sukayi asara a wannan lokaci.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.

Friday, December 18, 2009

FOUR YEARS REMEBRANCE...

December 18, 2005 will remain unforgettable to our family. It was on the early hours of that fateful day that our beloved father Justice Abdul-Hadi Dabo left this sinful world to rest in the bosom of Allah. Four years has gone now, but you are still fresh in our memory as if it was just yesterday you departed.
You came to earth with nothing and left with nothing, but rather left a legacy that others resisted. You triumphed over hard work which has been our watchword.
The eyes cannot see you, the nose cannot sense you, the mouth neither can talk to you, but what about the ears, they both cannot hear you...
Prayers cannot awaken you from the deep slumber you have fallen; it will only elevate you to the most high and bury your past earthly mistakes.
It's our prayers that the Almighty Allah will have mercy on your soul, together with all the muslims who died before you right from the time of prophet Adam (A.S). May He afford us the will and patience to pray for them and bless us with those who will pray for us when we die...
May Allah's infinite mercy shower you an infinitum forgiveness of your past mistakes. May He also grant you the eternal rest. Ameen... Continue to rest in peace till we meet in ALJANNA FIRDAUSI...

Friday, December 4, 2009

YABO GA RUNDUNAR YAN SANDAN JIHAR KADUNA

Yabon gwani akace ya zama dole, kuma kowa yayi aiki na gari dole a yaba masa. Hakan yasa ya zama dole a jinjina ma hukumar ‘yan sandan Jihar Kaduna karkashin jagoranci kwamishinan ‘yan sanda agogo sarkin aiki Alhaji Tambari Yabo Muhammed, ganin yadda jami’an shi ke aiki tukuru ba dare ba rana don ganin sun fatattaki miyagun da ke addabar jihar Kaduna dakuma kare rayuka da dukiyar al’ummar ta jihar Kaduna.
Murkushe shirin fashi da makami a jajibirin sallah da ta gabata a hanyoyin Kaduna zuwa Birnin Gwari da kuma Kaduna zuwa Zaria da ‘yan sanda sukayi abin a yaba masu ne matuka, domin kuwa baicin daukin gaggawa da jami’an suka kawo da Allah kadai yasan irin barnar da ‘yan fashin zasu yi a hanyoyin ganin cewa jama’a da dama na ribibin komawa kauyukansu don yin sallah tare da iyalansu dakuma ‘yan uwa da abokan arziki. Harkar tsaro dai a jihar Kaduna kullum sai kara karuwa takeyi saboda kyakkyawar kulawa da maigirma gwaman jihar Alhaji Namadi Sambo yaba fannin tsaro tare da samar da kayan aiki. Domin kuwa jihar Kaduna ta zarce sauran takwarorinta a fannin tsaro, don haka ya zama dole a yabama wannan hubbasa da mai girma gwamna keyi don ganin tsaro ya inganta a jihar Kaduna. Suma ‘yan sanda dole a dada yaba masu ganin yadda suka dage wajen dakule duk wata hatsaniya da shirin aikin ‘yan zauna gari banza da bata gari keyi don ganin Jihar Kaduna ta zama abin koyi ga suaran jihohi.
Don haka ya kamata hukumomin da abin ya rataya a kansu su dada samar da kayan aiki ga jami’an tsaro don suji dadin sauke nauyin daya rataya a kansu a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, kuma a ci gaba da basu horo tare da turasu kwasa kwasai cikin gida da kasashen ketare don dada gogewa a aikinsu da kuma yin gogayya da takwarorinsu na waje. Sukuma jama’an gari suci gaba da ba ‘yan sanda hadin kai a duk lokacin da bukatar hakan ta taso tare da basu muhimman bayanai kan duk wani mutum da basu gamsu da take takensa ba. Da fatan sauran jihohi zasuyi koyi da jihar Kaduna don samar da cikakken tsaro a jihohinsu.

Sunday, November 22, 2009

Hukumar EFCC: Ba girin girin ba....


Shugabar hukumar EFCC madam faida waziri ta fito tayi wasu maganganu da suka ja hankalin ‘yan kasar nan da dama kan malam Nuhu Ribadu, ciki kuwa hardani. Duk da cewa banso cewa komai ba kan maganganun da tayi, amman ya zama dole don ganin yadda ta rika hawa tanasauka gami da kushe duk wani irin nasara da malam Nuhu Ribadu ya samu lokacin aikinsa. A sanin ‘yan Nijeriya dai babba da yaro, tsoho da matashi ya san cewa hukumar EFCC na yaki ne da masu almubazzaranci da ta’annati da dukiyar kasa ne. yaki da masu wawushe dukiyar talakawa zuwa aljihunansu yana daya daga cikin ayyukan hukumar na EFCC kamar yadda kowa ya sani. Don haka yin aiki akasin haka ya sabama manufofin wannan hukumar.
Amma da dukkan alamu wannan hukuma ta EFCC a halin yanzu bata aikinta yadda ya kamata, domin kuwa shugabar hukumar tayi wani maganganu wadanda suka bada mamaki matuka, domin inda wani ne yayi wannan Magana ba ita shugabar EFCC dinba, to a iya cewa saboda baisan aikin hukumar ta EFCC ne yasa haka. Madam Farida Waziri ta fito fili ta shaidawa duniya a wani shiri da akayi da ita a sashen hausa na muryra Amurka mai suna sai bango ya tsage, ranar 19-11-2009 cewa “ muna neman malam Nuhu Ribadu ne saboda ya je yana bata min suna da sunan Nijeriya a kasashen waje saboda yanajin haushina, kuma yace duk shugabannin Nijeriya masu rashawa ne……..” wannan dalilai ne yasa a cewar madam Waziri ya zama tilas ga hukumarta ta damke malam Nuhu Ribadu in har sunyi tozali das hi. Amman da akayi mata tambayar cewa mai zaisa baza su tuhumi Ibrahim Lamorde ba, tsohon shugaban hukumar ta EFCC daya gaji malam Nuhu Ribadu kafin zuwan ita madam Waziri, gogar taku sai ta sake kada baki tace “ ai shi Lamorde ba za mu kamashi ba ko mu bincikeshi ba domin yayi shiru bai zagi kowa ba, shikuwa Ribadu sai bata min suna kawai yakeyi domin an bani mukaminsa” wadannan kalamai na Madam Waziri cike suke da ban mamaki, domin kuwa bai kamace ta a matsayinta na wacce tasan aikin taba (in harta sanin ma kenan) ta fito tana irin wadannan maganganun cewa hukumarta zata kama Nuhu Ribadu ne kan wai yana bata mata suna! Wannan bayanai nata na nuni da cewa kenan zasu kama Ribadu ba kan yana da laifin cin hanci da rashawa ba ke nan. To, abin tambaya a nan shine, shin hukumar EFCC ta daina yaki da cin hanci da rashawa ne ta koma farauta masu batama Nijeriya suna a kasashen duniya? Lallai wannan tambaya ne da madam Waziri ya kamata ta amsashi don ‘yan Nijeriya su san alkiblar da EFCC ta nufa yanzu idan ta canza ne daga damkewa da cafko masu karya tattalin arzikin kasa.
Har ila yau, madam Waziri tayi ikirarin cewa malam Nuhu Ribadu ya shirya manakisan hanasu yin wani taro da sukayi a can kasar Amurka. Don Allah jama’a kuji irin wannan Magana fa, ta yaya mutumin daba dan kasar Amurka ba zaiyi tattaki zuwa Amurka har ya tara yan zauna gari banza don su hana madam Waziri da sauran tawagarta gudanar da taronsu? Amurka fa bata da ‘yan zauna gari banza kamar yadda ake dasu a Nijeriya, idan ma akwaisu ta ya Ribadu zai iya tarasu domin su hana wannan taron da madam Waziri tayi ikirarin cewa yayi makarkashiyar hanawa?
Ya kamata madam Waziri taji tsoron Allah tayi aiki tsakani da Allah, idan mutum baici ba bai shaba, to kada a rika yi masa bita da kulli. Kada a dauki tsanan duniyannan a daura masa idan anga yana samun ci gaba a rayuwarsa. Ba zai kyautu ba in har madam Waziri tayi amfani da kujeranta don musgunama malam Nuhu Ribadu kan laifin da baiji ba bai gani ba. Gaskiya dai daya ne, kuma daga kinta sai bata. Kowa a kasarnan yasan irin yadda wannan bawan Allah Ribadu ya sadaukar da kansa ya bautawa kasarna, don haka in har baza’a sakamasa da alhairi ko a yaba masa ba, to bai kamata a tsine masa ba ko a musguna masa ba. Wallahi kasarnan na bukatar irin su Ribadu don kaiwa ga tudun mun tsira, amman saboda yanayin azzaluman shugabannin da muke dasu wadanda basa son gaskiya hakan yasa da wuya a yanzu a sake ba Ribadu dammar ya zo yaci gaba da bautawa kasarnan kamar yadda yayi a baya don samun ci gaba. Domin kuwa tun bayar barinsa hukumar EFCC, har yanzu babu wasu kwararan nasarori da aka samu kaarkashin hukumar kamar yadda aka samu a lokacinsa.
Hakika ya kamata madam Waziri ta zauna tayi ma kanta karatun natsuwa ta kuma rika banbance tsakanin gaskiya da karya a al’amuran aikinta na shugabar EFCC. Dan gane kuma da bayanin da tayi cewa Ribadu na da matsala da hukumar da’ar ma’aikata, to ai wannan ba lamari ne da ya shafeta ba domin ba’a hukumarta abin yake ba, don haka shiru shine nata ta barshi su karata da hukumar da’ar ma aikata. Har yanzu ‘yan Nijeriya na kaunar Ribadu saboda yadda ya sadaukar da kansa yayi aiki tukuru, kuma suna fatan watan wata rana gaskiya zatayi halinta, duk wannan bita da kulli da akeyi masa zata kare. Fatarsu shine kasarnan ta samu shugabanni na gari masu son gaskiya wadanda tafiyarsu zatayi daidai da irin tafiyar su malam Nuhu Ribadu adali kuma haziki, kuma Allah ya kubutar da shi daga azzaluman mutanen da suka sashi a gaba.
Allah yayi mana jagorancin a dukkan ayyukanmu na alhairi. Kuma yaci gaba da karemu gami da tsaremu dayi mana Katanga ga dukkan abin da muke shakkunsa na zahiri da badili, amin.

Friday, November 20, 2009

NADA GWAMNA IBRAHIM SHEKARAU A MATSAYIN SARDAUNAN KANO: RIBAR SIYASA?


Tuwon girma akace miyan nama inji masu iya Magana, kuma yabon gwani akace ya zama dole. Nadin mai girma Gwamnan Kano mallam Ibrahim Shekarau a matsayin sardaunan Kano da mai martaba sarkin Kano Alhaji Dakta Ado Bayero yayi masa ya jawo ce-ce-ku-ce a ciki da wajen jihar inda wasu ke alas an barka da wannan saraudar da kaba limamin adaidaita sahu, wasu kuwa akasin hakan ne ke fitowa daga bakinsu.
Alal hakika mai girma sarkin Kano Alhaji Dakta Ado Bayero yayi kyakkyawar hange wajen zaben Mallam Ibrahim Shekarau a matsayin sardaunan Kano kuma a lokacin daya dace, musamman ma ganin yadda shi sardaunan na Kano ke ci gaba da ayyukan raya jihar gami da gina al’ummarta ta fannoni daban daban. Alal misali gina madatsan ruwa na tamburawa da akayi wanda duk nahiyar afrika babu kamarsa ya sawwake radadin azabar rashin ruwa da mutanen Kano suka dade suna fama dashi na shekara da shekarau, samar da aikin yi ga matasa, bada tallafi ga nakasassu, ga kuma fadada hanyoyin jihar da akeyi a halin yanzu don rage cunkoso a titunan garin da kuma inganta hanyoyin sufuri, sai kuma uwa uba wutar lantarki wanda yanzu haka a makwanni uku da suka wuce jihar Kano tafara samun cikakken hasken wutar lantarki a ko wane rana ba kakkautawa wanda hakan zai dada karfafa aikin masana’antu, da dai sauran ayyukan ci gaban jihar da dama.
Sadaukar da kai da yin aiki tukuru ba tare da gajiyawa ba da mai girma gwamna Mallam Ibrahin Shekarau keyi tare da baiwa kowa hakkinsa ba tare da nuna banbancin addini, siyasa ko kabila ba, gami da gina al’umma tare da yin ayyuka don ci gaban jihar Kano dama Kasa baki daya sune suka kai ga baiwa limamin adaidaita sahu sarautar sardaunan Kano. Domin kuwa, hatta jihohin kasar nan sun yaba da ayyukan gina kasa da mai girma gwamna Shekarau keyi wanda hakan yasa aka bashi sarautar Onwa Na-Etiri oha 1 na Ehaalumono a kudancin kasar nan. A zahirin gaskiya, mai girma gwamnan kano kuma limamin adaidaita sahu ya cancanci a kirasa da magajin sardaunan sokoto, domin kuwa kyawawan halayensa na kishin jama’arsa da son ci gabansu yayi daidai dana marigayi sardaunan sokoto Alhaji Sir Ahamadu Bello.
Sanin kowa ne Jihar Kano tun bayan kirkirota bata samu cigaban da ta samu a shekaru shida da suka wuce ba karkashin jagorancin adalin gwamna Dakta Ibrahim Shekarau. Wannan kuwa wani babban nasara ne da al’ummar jihar Kano ya kamata suyi tunkaho dashi, kuma suyi godiya ga Allah madaukakin Sarki daya tarfawa garinsu nono ya albarkace su da gwamna mai son cigabansu musamman ma ganin yadda a kullum sai kara kwasan ribar dimokuradiyya sukeyi ba kakkautawa. Don haka babu abinda mai girma gwamna Mallam Dakta Ibrahim Shekarau limamin adaidaita sahu, garkuwan Ilimi, sardaunan Kano, Onwa Na-Etiri oha 1 na Ehaalumono, kuma magajin sardaunan sokoto ke bukata face ayi masa addu’ar Allah yaja kwana kuma ya biya masa dukkan bukatunsa na alkhairi da yasa a gaba kuma ya basa ikon sauke nauyin da ya rataya a kansa tare kuma da Addu’ar ALLAH YA KAI DAMO GA HARAWA! Amin.
Allah ya kara tsaremu, karemu, kiyayemu tare da yi mana garkuwa ga dukkan abubuwan da muke gudunsu, shakkunsu ko tsoronsu a zahiri da badili, tare kuma da rokon Allah ya kara shigemana gaba da yimana jagoranci a dukkan ayyukanmu nayau da kullum, amin.

Wednesday, October 7, 2009

BETWEEN ASUU AND THE FEDERAL GOVERNMENT


The continuation of eye lingering between the federal government and ASUU is very annoying, because governments on their own part are not showing any concern about the issue. It’s quite unfortunate that education sector is not given all the necessary attention and this is due to the fact that the children of UNE (United Nigerian Elite) are schooling abroad, and only the less privilege ones are suffering from this strike. Imagine our counterparts that go to Dubai, Malaysia, India and so on are acquiring a degree in just 3 to 4 years while here in Nigeria you spent almost 6 to 7 years to acquire the same degree due to this kind of strike and so on. It’s high time for this government to look into the needs of these people so as to bring an end to this long term strike in order to allow students continue with their studies. Also they (government) should know that any country that lacks qualitative and standard education, that country will never develop in any way….Allah ya sauke!

Thursday, October 1, 2009

NIGERIA @ 49: WHO'S TO BLAME?


I wonder why many nigerians are celebrating the 49th years of independence when things in the country are getting worst day by day. foristance, our universities are on strike for the fast 3 months and govermnent are not showing any concern about it, imagine our president going to saudia to commission a university as a special guest while his own universities are closed over a minor issue wchich can be solved within a week.it is better we celebrate 49 years of power failure, insecurity (becouse kidnapping is becoming rampant in this country), fallen standard of education, unemployment, collapse of industries,poor medical facilities,...to mention but few. no hope for the masses, everything is getting out of hand. but do we fold our hands and keep watching for things to continue like this? what devidend did nigerians derived from the so called 49 years of independence? up to now we can not differentiate between yestarday and tomorrow, for God sake is there any cause for celebration? our leaders have totally failed in all round. it's high time now for our leaders to wake from their deep slumber before it becomes too late for them to cry

Sunday, September 27, 2009

BIRNIN KANO YA DAUKI BAKUNCIN TARON GIZAGO KARO NA FARRKO


A jiya asabar ne 26/9/09 akayi taron gizago karon farko na kasa baki daya a birin kano. Assalamu alaikum yan uwa maza da mata na wanna dandali, ina mai mika godiya ta da farinciki gareku baki daya da kuka sami damar halartar babban taron wannan kulob namu na GIZAGO SOCIAL AND CULTURAL. hakika yadda maza da mata mambobin wannan kungiya suka amsa kira tareda masu mata fatan alahiri sukayi cincirondo zuwa wannan taro kwansu da kwarkwatansu daga sassa daban daban na kasar nan, wata kila ma harda makwabta abin farin cikine kwarai da gaske, kuma wata alamace ta cimma burinmu.
godiya ta musamman ga Dr. Bala Muahammed, sheik aminu daurawa, malam bashir yahuza malumfashi, aburrahaman haruna(dodo) da sauran manayan baki maza da mata da sukaa sami zarafin halartar wannan taro duk kuwa da irin aikin da ke gabansu. bani da ingantacciyar kalmar da zan iya gode maku illa ince allah yasaka da alhairi kuma yabar zumunci amin. Suma wadanda suka gabatar da shirin, Ado ahmad gidan dabino da Mk Adam muna jinjina masu sosai. haka shima malam nura adamau yayi namijin kokarin yadda ya rinka kaiwa da komowa, ga su shafi'u imam, da dai sauran mutane da dama.
haku suma manbobin kungiyar nan kun cancanci yabo, musamman ma malam Mk Adam, agogo sarkin aiki, buldoza, aiki ga maiyinka, hakika yayi kokari domin tun kwana uku kafin buki ya iso kano don ganin shirye shirye ya kankama yadda ya kamata. itama shugabar mata ta kasa hajiya aisha lawal, da mataimakiyar ma'aji haiya huawa ahmed sunyi aiki kwarai da gaske, Allah ya saka da alhairi. sauran mambobi maza da mata daga dukkan jihohin da suka iso wanna taron ina maku godiya ta musamman da fatan kowa ya koma gidansa lafiya.
ina mai farin cikin shaida maku cewa in Allah ya yarda taro na gaba kamar yadda nayi bayani tun farko, za'ayi sane na garin gwamna, cibiyar ilimi, kasar balaraben sarki, bugu da kari sarkin sarakuna.
nagode Allah yasaka da alhairi, ya bar zumunci. wassalam
MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
NATIONAL CHAIRMAN,
GIZAGO SOCIAL AND CULTURAL CLUB
080-36397682
http://anguwarfatikaonline.blogspot.com