Thursday, June 4, 2009

HEART BREAK !!!


I've been thru hell
Trying to get you out of my life
But after all this time
I can't help myself but miss you.

Now, all alone
Thinking of my life once again
My past is passing me by
I feel a lot of pains
I shed a lot of tears
As I remember all we’ve been through.

You’re once a dream that came true
An illusion that turned to reality
But suddenly, things turned differently.

You give me sleepless night
Coz you keep staying on my mind
I can’t stop crying
Coz I’m missing you…

My life will never be the same again
Now that you’re gone
I will be trapped in this loneliness forever.

I thought this was a poem I would never have to write
I hope my tongue was something I could bite
But realized it’s just something I cannot do
I’m still so in Love with you, after all this time.

Your heart is now with someone else
I’m so jealous
I can’t bear these bullets anymore
The pain of losing you is still fresh in my brain
Every day my heart feels the pain
Will things ever be same again?...

I want you to know I’m heartbroken
I want you to know I’m hurt
But please….
I don’t want you to look at the tears in my eyes as I cry…

Wednesday, May 20, 2009

TEN YEARS OF CIVILIAN RULE..


Its now exactly ten years since the return of civilian rule in Nigeria, but Nigerians have not witness any development over these years. things are even getting more worst than before: no constant electricity power supply, poor roads,falling standards of education, our hospitals are in critical conditions, economic meltdown, nigerian stock exchange is not looking good and there is a problem of unemployment in the country. this adminstaration is nothing but a set back, becouse one of the so called 7-points agenda have not been actualised.
Yar’adua should as a matter of urgency address these issues once and for all to avoid further escalation of the problem. It is very unfortunate that despite the vast natural resources that God in his infinite mercy endow Nigeria with, the resources are mismanaged by a very few and the masses are left in squalor and poverty. The national cake is being looted and squandered by few out of Whims and Fancies to the detriment of the majority.
Anyway, Nigerians, happy ten years of civilian rule not democracy!

Thursday, May 7, 2009

Jang Vs Fula

FULANI SUMA YAN NIGERIA NE:

Budaddiyar wasika ga gwamna Jonah Jang
zaman lafiya da ci gaban ko wace kasa ko al'umma ya dangana ne ga yadda shugabanninsu ke tafiyar da mulkin su ba tare da nuna banbanci kabila, addini ko siyasa ba. Yin hakane kawai zai kawo ci gaban kasa da kuma al’umma. Hukunci da gwamnatin jihar filato ta dauka na Koran Fulani a jihar wani mataki ne da ka iya tada zaune tsaye, musamman ma ganin yadda jihar tayi kaurin suna kan rikice-rikice kama daga na kabilanci, addini, siyasa da dai sauransu.
Sanin kowa ne dokar kasa taba duk dan kasa damar zama inda yake so ba tare da tsangwama ba. Don haka ya kamata gwamna Jang ya gane cewa fulanin filato na da ‘yancin zama a ko ina cikin kasarnan kamar yadda sauran kabilu ke zaune a jihar ba tare da an takura masu ba. Har yanzu dai matsalar dan kasa da bako bata mutu a filato ba, don kuwa in ba haka ba babu dalilin da za’ace za’a kori fulanin dake filato a halin yanzu. Filato, jihar da ake yi mata take da jihar zaman lafiya, yawon bude ido da shakatawa yanzu ana iya cewa ta koma jihar rashin zaman lafiya sanadiyyar shugabanni marasa kishin ci gabanta da take dasu, sai dai kuma yawon bude ido da shakatawan ko yananan ko babu Allah kadai ya sani.
Ba komai ya kawo wannan gurguwar mataki da gwamna Jang ya dauka na Koran fulanin jihar ba illa rashin daukar kwakkwaran mataki da gwamnatin tarayya takiyi kan shi gwamnan bisa rikicin da ya faru na baya bayan nan a jihar inda aka rasa dimbin rayuka, wanda hakan shi ya sake ba gwamnan karfin guiwar kawo wata sabuwar salon da ka iya haifar da rudani a jihar da ma kasa baki daya. Alal hakika, tilastawa Fulani barin filato wani babban lamari ne da ka iya haifar da komai matuka mahukuntan da abin ya shafa basu sa baki ba. Abin bakin cikine yadda gwamnatin tarayya tayi bakan taki cewa uffan kan wannan lamari wanda barazana ne ga zaman lafiya ta fanin tsaro. Wai ma abin tambaya shine; me yasa irin wadanan matsaloli basa faruwa a sauran jihohin kasar nan sai jihar filato kawai? Shin itace kadai jihar da take da kabilu masu dimbin yawa? Tabbas akwai bukatar shugaba yar’adua ya dauki matakan ladabtar da gwamna Jang don ganin bai wuce makadi da rawa ba in har ya dage kan wannan danyen mataki da ya dauka na korar Fulani, domin babu wanda ya fi karfin doka, kuma duk wanda ya nemi yin karan tsaye ga dokokin kasa, la shakka yana bukatar ladabtarwa don ya zama darasi ga ‘yan baya.
Lokaci yayi da shugabanni ya kamata su rika mulkin adalci ga al’ummar da suke mulka ba tare da nuna banbancin addini, kabila, siyasa, fifita wasu bisa wasu, ko asali ba, tayin hakane kawai za’a samu zaman lafiya, ci gaba da daurewar shugabanci na gari.
Alal hakika, akwai bukatar gwamnatin tarayya ta gaggauta daukan mataki kan wannan kazamin aiki da gwamna Jang keson aikatawa don dakile duk wata hargitsi daka iya kunno kai don samun zaman lafiya a jihar da ma kasa baki daya. Watan wata rana kowa zaiyi bayanin yadda ya tafiyar da shugabancin talakawansa a gaban mai duka, don haka kalu balen ku shugabanni.
Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukanmu na alhairi, amin.

Friday, April 17, 2009

ZIYARAR MU ZUWA MALUMFASHI.

Da sanyin safiyar ranar alhamis ne 16-4-09 na bar zariya zuwa katsina don halartar taron karawa juna sani da wayar da jama'a kan yawan mutuwan mata masu juna biyu da kananan yara wanda sashen hausa na muryar amurka ta shirya. Dayake bansan inda za'ayi taron ba a birnin na dikko , hakan yasa na tsaya a malumfashi don tuntubar yan uwa kamar su kabir sakaina, Mohammad dandattijo da dai sauransu. isana keda wuya sai naci karo da Zaidu Bala wanda dama tuni akasanar dani cewa ya iso malumfashi don zuwa wannan taro. nan muka hadu muka sada zumunci tsakanin mu mukayi dan raha da ba'a rasa ba, wanda daga baya muka dunguma da ni da zaidu bala da usman adamu aleiro zuwa katsina don halartar wanna taro. hakika mutanen malumfashi sun karbe mu hannu bib-biyu, sunyi mana shatara na arziki tamkar munsan juna tun kafin wanna rana, koda yake zan iya cewa munsan juna amman ta hanyar waya kawai, domin kuwa ranar ne a iya saninan muka san junanmu fuska da fuska.
Alal hakika irin wanna karamci da Mohammed Usman dandattijio, Kabir sakaina, Abdurra'uf Abdulkadir da sauran yan uwa suka nuna mana abin yabawa ne matuka, domin kuwa hakan ya dada donkon zumuncin tsakani mu dasu, kuma ina fatan zata daure har muddun rai. suma mutanen garin katsina ba a barsu a bayaba, domin kuwa Comm Bashir Dauda, Ali jauro mai gidan wanka, tare da sauran tawagarsu suma sunyi mana babban maraba , domin kuwa da muka tashi dawowa basu barmu hakanan ba saida suka saya mana kayan tsotse tsotse, kamar dai yadda mutanen malumfashi sukayi mana da zamu tafi. Gaskiya nayi farin ciki da wannan rana matuka da irin wannan tarba da mutanen garin malumfashi da katsina sukayi mana, domin kuwa sun nuna mana kauna kwarai da gaske, hakika katsinawa sun amsa sunan su na 'dakin kara' domin kuwa mun gani kuma mun shaida hakan. Bani da in gantaccen kalmaomi da zan yabamasu ko gode masu saidai in ce Allah ya saka masu da alheri kuma ya barmu tare.
Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukan mu na alheri, amin.

(Engr.)MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
ANGUWAR FATIKA, ZARIA
080-36397682

Tuesday, April 14, 2009

GWAMNA ISA YUGUDA: KAZA NE TA JA ZAKARA!


kace kuce dai ta kare a batun ko malam isa yuguda (gwamnan jihar bauchi) zai koma jam'iyar PDP ko a'a. domin kuwa a yau ne 14-4-09 ya bar jam'iyar ANPP da ta kaishi ga mukamin da yake zuwa PDP wanda a wancan lokaci ta kwance masa zani a kasuwa. Alal hakika malam isa yuguda yaci amanar talakawarsa, musamman ma ganin yadda sukayi ruwa sukayi tsaka a lokacin zabe suka hana kansu barci har saida aka tabbatar masu da nasarar dan takararsu wato malam isa yuguda bayan abinda su 'yan jihar suka kira mulkin kama karya na PDP ya ishesu shiyasa suka kawo canji.
wani abin ban haushi da ke tattare da wannan lamari shine, yadda malam isa yuguda yace "na koma jam'iyar PDP ne don samar da ci gaban jama'ar bauchi" kuma ya kara da cewa wai zai iya barin kujerarsa don kare maradu tare da ciyar da jama'ar bauchi. ko kusa wadanan kalamai nasa ba abin a duba bane, musamman ma inda yace wai komawarsa PDP zata taimaka wajen gina asibitin koyarwa da madatsar ruwa ta kafin zaki da samun manyan ayyuka daga gwamnatin tarayya, wadanda acewarsa, idan bai koma PDP ba, saidai suci gaba da zama a takarda baza su tabbata ba, hakanne yasa ya bar ANPP ya koma PDP don ci gaban talakawan jihar bauchi. to ayar tambaya anan shine sauran gwamnoni dake ANPP basa iya aiwatar da nasu ayyukan kenen tunda basu koma PDP ba? ko kuwa kana yin tallane ga suaran takwarorinka na ANPP da su dawo PDP domin suma su samu damar aiwatar da ayyukan da zasu kawo ci gaban al'ummar su?
a fili yake kowa yasan cewa komawar gwamna yuguda bata da wani nasaba da cigaban al'ummar jihar bauci saidai kawai don biyan bukatar kansa. abin kunya ne yau a kasarnan yadda 'yan siyasa ke canja jam'iyyu don kawai neman abin duiya wanda suka maida shi gaba da bukatun talakawan da suka zabe su. domin kuwa canjin sheka ya zama ruwan dare a kasarnan. wai ma abin tambaya anan shine, shin malam isa yuguda ya mance da irin cin zarafin da jam'iyar PDP tayi masane karkashin jagorancin gwamna adamu mu'aza a wancan lokaci? gaskiya ya kamata ace koda kamshin wannan jam'iya malam isa yuguda yayi, to yayi Allah wadai da ita sakamakon irin wulakanta shi da akayi ba wai ma yayi tunanin komawa cikinta ba. koda yake komawarsa baizo da mamaki ba, don kuwa yanzu munsan kusan 'yansiyasar namu sun koma yan jari hujja, don haka wanna ba abin ayi mamaki bani ganin yadda wasu lamura suka faru a baya,sai dai kawai muce kaza ne ta ja zakara.
yanzu dai ta riga ta kare, amman saura da me? malam isa yuguda sai kajira sakamakon ka, domin Allah sai ya sakama talakawanka da suka baka amana amma kaci amanarsu.

MUNTAKA ABDUL-HADI DABO
ANGUWAR FATIKA, ZARIA
080-36397682

Monday, April 6, 2009

DEMOCRACY @10: Success or Failure?


A DECADE SINCE THE RETURN OF DEMOCRACY IN NIGERIA : Success or Failure?

Day in, day out, a wise man says that a year is just akin to (like) a day. It is now a decade for the return of civilian and democratic rule or government in Nigeria and simultaneously the incumbent president, Alhaji Umar Musa Yar’adua, is now in his second year in office after stepping into the shoes of the former president Mathew Aremu Olusegun Obasanjo who spent a complete good eight years steering the mantle of leadership in Nigeria as its number one citizen from 1999 to 2007.

It is now desirable for Nigerians, especially those at the grass roots level, to look back and cogitate over this period of decade of democratic rule in Nigeria on what dividend or developments do they achieve or experience. Though they have since expressed their dismay over the catastrophic conditions they had found themselves during the eight years of draconian rule of Mr. Obasanjo.Those conditions/situations of unemployment, high cost of living, melting down industries and factories, e.t.c during those eight years of Obasanjo were some of the reasons that necessitated Nigerians to come out during the 2007 General elections (in order) to bring changes and thereby find a lasting panacea to their worries. Unfortunately for them that dream and wishes has just ended a mirage.

Few Nigerians expect that there could be a meaningful change on the ground of the mannerism of leadership of Yar’adua at the inception or assumption of office by trying to legitimatize his government to the Nigerians in particular and the whole world in general. This is clearly because he is fully aware that the election that brought him into office was characterized by an unprecedented election malpractices in the history of Nigeria . Respect for the rule of law, independence of the judiciary, unity government, zero-tolerance to corruption, and the like, are some of the reasons why some Nigerians welcomed the Yar’adua’s government. He (Yar’adua) actually delivered the goods with respect to the independence of the judiciary. This is corroborated from the fact that he remained mute when the election Tribunals and Courts were busy nullifying the elections of P.D.P candidates at the various level of government on the ground of electoral malpractices. Yar’adua has, without any iota of doubt, shown a sense of maturity in that respect which was not obtained in the Obasanjo’s era.

The recognition of the autonomy of the judiciary and that of the other branches of government by the Yar’adua’s administration had crucially changed the minds of many Nigerians from expecting to the hoping that a new messiah has come to save Nigeria and Nigerians from the shackles of squalor and poverty which they found themselves in during the Obasanjo’s era. Up to now, one out of the so-called 7 points agenda has not been actualized, despite the fact that he has been in the mantle of leadership for two years the problem of incessant power failure which has been plaguing the country for quite a long time and which is one of the 7 point agendas is getting from bad to worst by day and many businesses have collapsed simple because one cannot cope with fuelling a generator. During Obasanjo’s regime, many committees were constituted to address the issue but with little to show. Billions of Naira have been spent fruitlessly. Yar’adua’s administration has also constituted the committees for the same purpose but with little or no success at all. Many problems are still deeply rooted in the country ranging from lack of potable water, defective health system, educational degradation, lack of security and agricultural backwardness, to mention but a few.

Yar’adua needs to institutionalize drastic measures to counter the current global economic crises that is currently affecting the globe. If care is not taken Nigeria like any other under-developed countries is going to be affected negatively this can be seen from the sharp increase in US dollar against Naira and in the fall of price of oil in the world market, looking at the value of Naira in 1999 which is 120 Naira against US Dollar compared with its value today which is 163 Naira against US Dollar one can simply conclude that Yar’adua administration is nothing but a set back. Nigerian stock exchange is also not looking good and there is the problem of unemployment in the country. Yar’adua should as a matter of agency address these issues once and for all to avoid further escalation of the problem. It is very unfortunate that despite the vast natural resources that God in his infinite mercy endow Nigeria with, the resources are mismanaged by a very few and the masses are left in squalor and poverty. The national cake is being looted and squandered by few out of Whims and Fancies to the detriment of the majority.

In some instances the money is spend not in the right way as in the case where dogs were transported into the country at the price of 2 millions naira. What a madness! Now the question is what is the benefit derivable from the Nigerian democracy, is it a dividend or a loss? Infact there is nothing tangible to show which Nigerians can be said to have been benefited in the fast ten years of democratic rule. Indeed the poor remain poorer and the reach remain reacher by day. This is therefore a challenge to the Yar’adua’s government to do something concrete before the remaining two years elapse and it then become too late to cry.

SHEKARA GOMA NA MULKIN DIMOKRADIYYA: Riba ko Asara?

Kwanci tashi ba wuya, shekara kuma kwana ne inji masu iya magana. Yau shekara goma kenen da mulkin dimokradiyya ya sake dawowa a kasarnan, yayin da kuma shugaba Umaru Musa ’Yar’adua ke cika shekaru biyu a gadon mulki bayan ya gaji Obasanjo wanda ya kwashe shekaru takwas yana mulkin Nijeriya.

Shekaru goma da aka kwashe ana mulkin dimokradiyya lamari ne daya dace ‘yan Nijeriya musamman ma talakawa suyi waiwaye suga irin ribar da suka samu a wadannan shekaru. Koda yake, tuni ‘yan Nijeriya suka bayyana rashin jin dadinsu da irin bala’i da halin kaka-ni-kayi da suka shiga a karkashin mulkin Obasanjo na shekaru takwas wanda yakare ba tare da sun amfanu ba. Irin wannan hali da talakawa suka samu kansu a lokacin mulkin Obasanjo na rashin aikin yi, tsadar rayuwa, tabarbarewar masana’antu, da sauran matsananci hali yasa sukayi tururuwa don kawo sauyi a lokacin zaben 2007 amma hakarsu bata cimma ruwa ba, don kuwa wanda Obasanjo keso ne ya gaje shi.

Kasancewar ‘Yar’adua shugaban kasa yasa wasu kalilan daga cikin yan Nijeriya tunanin cewa za’a samu sauyi don ganin yadda shi ‘Yar’adua ya dauko salon shugabancin da farko inda ya fara neman halasta gwamnatinsa a idon yan kasa dama duniya baki daya, domin kuwa yasan cewa zabensa cike yake da magudi. An fara maraba da ‘Yar’adua ne bayan ya bayyana aniyarsa na yin aiki da kowa inda ya fara neman goyon bayan ‘yan adawa dasu shiga a dama dasu don ci gaban Nijeriya, yayi kuma alkawarin sakin mara ga fannin shari’a batare da yi masu katsalandan ba da dai sauransu. Hakan kuwa ya fito fili ne yayinda alkalai suka rika yiwa masu rike da mukaman siyasa karkashin jam’iyar PDP kamar gwamnoni, yan majalisu, da dai sauransu wadanda aka halasta masu zaben da basu sukayi nasara ba tsirara a kotunan zabe, kuma shugaba ‘Yar’adua baice uffan ba, sabanin yadda Obasanjo ya rika cin karensa ba babbaka a kotunan zabe lokacin mulkinsa. ‘Yar’adua yayi hakan ne don samun goyon bayan yan Nijeriya don su amince dashi.

Baiwa fannin shari’a cin gashin kanta da ‘Yar’adua yayi da sauran hukumomi ya sauya tunanin yan Nijeriya kan ‘Yar’adua inda kowa ya fara yabamasa da cewa za’a samu kyakkyawar sauyi a gwamnatinsa da kuma kawo karshen halin da yan Nijeriya suka tsinci kansu a zamanin mulkin uban gidansa Obasanjo. Har yau, manufofin gwamnatin ‘Yar’adua guda bakwai babu wanda aka cimma ko aka aiwatar, gashi shekara biyu sun wuce saura biyu kawai suka rage masa.

Idan aka dubi fannin wutar lantarki, wanda shine uwa uba, kuma sanadiyyar sa masana’antu da dama sun durkushe,lamarin ba’a cewa komai. Lokacin Obasanjo ba irin kwamiti da ba’a kafa ba don samun saukin abun amman duk abanza, domin kuwa ankashe biliyoyin naira lokacin Obasanjo amman kwalliya bata biya kudin sabulu ba. Shi kanshi ‘Yar’adu ya kafa kwamitoci har guda uku akan wutar lantarki amman har yanzu labarin bai canza ba. Har yau, anada matsalar rashin kyakkyawar ruwan sha, rashin kwakkwaran tsarin kula da lafiyar yan Nijeriya, tabarbarewar tsarin ilimi, rashin tsaro, fannin noma ma duk bata canja zani ba.

Tilasa ‘Yar’adua sai yayi da gaske kan tashin gwauron zabi da dalar amurka keyi akan naira. Bayan hawan Obasanjo mulki a shekara 1999, naira ta daga ta kai #120 a darajar dalar amurka daya, inda dukkan yan Nijriya suka yi tir da wannan lamari. Amma yanzu karkashin mulkin ‘Yar’adua, dalar amurka daya itace daidai da #180. Kasuwar hannun jarin Nijeriya shima ba’a barshi a baya ba, don kuwa sai kara durkushewa takeyi a kullum, rashin aikinyi ya gallabi yan kasa. Hakika wadanan lamari ne da suke bukatar gaggawar maida hankali akansu. Hakan kuwa na nuna cewa mulkin ‘Yar’adua na neman ya zarce na Obasanjo a sukurkucewa.

Kullum dai abin sai kara tabarbarewa sukeyi duk kuwa da irin arzikin da Allah yayi wa Nijeriya, koda yake arzikin kan komane aljihunan kalilan daga cikin yan kasa sauran kuma a kashesu ta hanyar da bazasu amfani al’umma ba. Kamar dai yadda akeso a sayo wai karnuka kan naira miliyan biyu akan ko waani kare guda daya! Wanna lamari da mai yayi kama?

To wai a tsawon wadannan shekaru suwa suka amfana ko sukaci ribar mulkin dimokradiyyar nan? Shin anci riba ne ko asara akayi? Alal hakika babu abinda ‘yan Nijeriya a yau zasuce sunci ribarsa a tsawon shekaru goma da suka wuce. Talaka bai amfana ba ta ko ina kuma baici ribar dimokradiyya ba don kuwa har yanzu yana nan yana ci gaba da dandana kudarsa da ta samo asalin tun mulkin Obasanjo, ba’a aiwatar da ayyukan ci gaban kasa ba, masana’antu sai kara durkushewa sukeyi, ga rashin aiki ga matasa, da dai sauransu. Don haka, wannan wani kalu bale ne ga shugaba ‘Yar’adua na ganin yayi kokarin aiwatar da manufofinsa a cikin shekaru biyu da suka rage masa.
Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukan mu na alhairi, amin.

kaji kadan..

Wednesday, April 1, 2009

YUNKURIN HALLAKA GWAMNAN YOBE

watanni biyu bayan rasuwar gwamnan jihar yobe, senata Mamman Bello Ali, sai gashi sabon gwaman jihar Alhaji Geidam na fuskantar barazanar kisa. hakan kuwa ya fito filine lokacin da akayi zargin an samasa guba a abinci, kuma da aka ba karnuka abincin, sunci sun mutu nan take. haka ya haifar da rudani a jihar ta yobe da hukumomin jihar baki daya. saidai kuma wata majiya daga fadar gwamnatin ta karyata wannan labari, inda sukace gwamnan na nan cikin koshin lafiya babu kuma wani yunkuri na hallakashi.