Matasa akace manyan gobe, kuma tushen cigaban kowace al’umma. Hakika wannan zancen haka yake, domin kuwa suna da babbar rawar dasuke takawa wajen tafiyar da harkokin yau da kullum. Saidai wani babbar matsala dake tare dasu shine rashin nuna halin ko inkula da gwamnati keyi masu. Rashin sanin muhimmancin matasan yasa haka ko kuwa rashin sanin su wanene matasa? To yadai kamata kowa yasan cewa matasa sune manyan gobe kamar yadda aka sani, kuma suna da babbar gudun muwa da zasu iya bayarwa wajen aikin raya kasa. Shin menene kalmar masata take nufi? Kan wanene hakkin matasa ya rataya? Menene kalmar manyan gobe take nufi, kamar dai yadda akance matasa manyan gobe? Wani irin kalu balene yake gaban su matasan? Menene zai iya faruwa kan irin rikon sakainar kashi da akeyiwa su matasan?
Ita dai kalmar matasa na nufin samari ne wadanda shekarunsu ya fara daga 18-25, kokuma daga 18-30 kamar yadda wadansu suke gani, yakuma ma danganta ne da yadda kowa yake ganin lokacin da yakamata a kira mutum a matashi, wato daga shekara 18 zuwa yadda yasamu. Idan kuma muka duba shin kowane ne hakkin matasa ya rataya akansa, zamu ga cewa hakkin nasu bawai ya rataya akan gwamnati bane kawai, harma da iyaye da sauran al’umma, koda yake ana iya cewa gwamnati ita keda babbar hakki. Abinda gwanmati ya kamata tayi wa matasa shine, samar da ilimi bai daya garesu, tsaro, kula da lafiyan su, sai uwa uba aikin yi domin kuwa wannan hakkine wanda ya rataya akanta. Sukuwa iyaye da sauran al’umma, hakkin sune suga cewa sunba matasa tarbiyya mai kyau, kuma sun basu horon daya dace dasu wajen tafiyar da ayyukansu na yau da kullum. Domin kuwa duk wata al’umma da take son cigaba, sai tabayar da cikakkiyar kulawa ga matasanta da basu kyakkyawar horon daya dace dasu don zama wakilansu na gari bana banza ba a duk inda suka shiga.
Allah sarki! Bahaushe yace wai matasa manyan gobe, kuma ko shakka babu wannan Magana haka take, kamar yadda nace a baya. Domin dai ita kalmar manyan gobe na nufin matasa ne zasu amshi tafiyar da ragamar mulki a duk lokacin da wadanda suke mulkin a yau suka tsufa ko wa adin barin aikin su yayi. Saidai labarin a kasar nan tamu Nijeriya tasha bamban. Domin kuwa, idan aka duba tun daga matakin kananan hukumomi har izuwa ta gwamnatin tarayya, za’a ga cewa duk wadan da shekarun su yafara daga 50-60 koma fiye da haka sune a madafun iko. Ba za’a ga matasa wadanda shekarunsu ya fara daga 35-40 ba, duk dacewa suna da babbar gudun muwar da zasu iya bayarwa wajen ci gaban kasar nan.
Matasa a yau sun zama kashin bayan ci gaban kowace al’umma, batare da la’akari da muhimmancin su a cikin al’umma ba, dakuma rawar da zasu taka ta fannin gina kasa. Hakika wannan yaka mata yazama kalu bale gasu matasan don ganin martabarsu ya karbu a ko ina, ta hanyar kaura cema duk wani aikin ash-sha, shaye-shaye da dai suransu, ganin cewa akwai bata gari acikinsu, kuma bahaushe yace wake daya shi ke bata gari. Saboda haka yaza ma wajibi ga matasa da su gyara kansu, sukuma san cewa dabi’ar banza bazata haifar masu da da mai ido ba. Har ila yau kada matasa su yadda su zama ‘yan bangan siyasa, abin nufi anan shine, kada wasu ‘yan tsirarun mutane su rika amfani dasu wajen tada zaune tsaye don kawai cimma burinsu, wanda bayan su wadannan mutane sun samu abin da sukeso basa yiwa su matasan komai illa su watsar dasu. Matasa susan cewa fa su wakilai ne na samar da zaman lafiya ba hargitsi ba a cikin al’umma. Komai na iya faruwa a duk lokacin da aka tauye ma matasa hakkinsu ko akaci gaba da nuna halin ko inkula dangane da rayuwarsu, musamman ma idan babu cikakken tsaro, ilimi, da uwa uba aikinyi da kuma sauran abubuwan more rayuwa wanda yazama hakkine na hukuma ta samara dasu. Rashin wadan nan abubuwa zai iya jefa matasa a tsaka mai wuya, kamar dai sace-sace, yawon banza da sauran aikin ashsha da baza’a rasaba, wanda kuma bama fatan hakan ya faru ga su manyan goben.
Daga karshe, ya kamata gwamnati da sauran hukumomin da abun yashafa da su san cewa fa matasa ba abin wasa bane a kowace irin al’umma. Musamman ma ganin cewa sune manyan gobe kamr yadda nayi bayani a baya, kuma suna da gudun muwa na cigaba da zasu iya bayarwa. Don haka yana da kyau a rika duba duk wata irin matsaloli dake damunsu, da kuma yin kokarin samar masu da maganinsa. Kana duk wata al’umama ko gwamnati data ga ayyukanta na samun cikas ko rashin ci gaba, to ta waiwaya ta dubi matasanta taga yadda al’amuransu yake tafiya.
Allah yayi mana jagoranci a dukkan ayyukanmu na alhairi amin.
THIS IS THE SITE OF MR.MUNTAKA ABDUL-HADI DABO,WHICH INCLUDES MY HISTORICAL BACKGROUND, SOME OF MY WRITE-UPS THAT ARE PUBLISHED IN THE NATIONAL DAILIES OF NIGERIA AND LOTS MORE...
Sunday, March 8, 2009
Tuesday, March 3, 2009
SHIN MATASALAR RUWA ZAI ZAMA TARIHI A ZARIA?
Budaddiyar Wasika Ga Gwamna Namadi Sambo.
Duk dan adam yana da bukatan abubuwan more rayuwa na yau da kullum kamar su wutan lantarki, hanyoyin sufuri masu nagarta,da dai sauransu.amman saidai a yau akasin hakan ake samu. Koda yake, wasu ma ana iya cewa sun zama dole yin amfani dasu. Misali, koda yake ruwa ba’a ce dashi abin more rayuwa ba, amman dukkan mai numfashi na bukatansa a kulli yaumin domin sha, girki da kuma sauran ayyukan yau da kullum
Kash! Saidai labarin a birnin zariya ba haka yake ba. Domin kuwa ruwa ya zama dan gwal. Saboda a yau duk wanda yazo garin zariya daga wata garin, to babu abinda da zasu fara yi masa maraba face ‘yan garuwa. Wadanda suke sayar da ruwan nasu da dan karan tsada, kuma gashi wasu daga cikinsu ruwan nasu bawai yana da kyau bane. Wanda idan hakan ta daure, to nan gaba ba’a san abinda zai haifarba.
Koda yake wannan matsala na rashin ruwa a birnin zariya bawai sabon lamari ne ba, saidai kawai yadda rashin nasa yake dada tabarbarewa. Na tabbata duk yaron da ke zariya a yau, wanda shekarunsa basu wuce sha takwas zuwa ashirin ba, wallahi bai taba ganin ankawo ruwan famfo a gidansu ba. Wannan matsala kuwa ta wuce duk iya tunanin mutane, domin kuwa kamar yadda nace ne tun farko, al’amarin yana neman wuce gona da iri. Abin ban takaici ne yadda a yau yara kanana cikin dare suke fita ko kuma da subahin fari da sunan suna zuwa neman ruwan da iyayensu zasu yi masu abinci. Wanda hakan kan iya sa yaran shiga wani halin da bai dace ba.
A kwai bukatan hukumomi ko gwamnati data shiga cikin wannan lamari don kawo saukinsa ga al’ummar da suke yiwa shugabanci. Koda yake, mai girma gwamnan kaduna Alhaji Namadi Sambo, ya samar da famfuna masu aiki da hasken rana wadanda zasu iya aiki daga safe har zuwa la’asar ko ace yamma. Saidai labarin ba haka yake ba, domin kuwa famfunan sun zama abin adone kawai a birnin na zariya. Saboda idan famfon yabada ruwa na kamar sa’a uku a rana, to sai yayi kamar mako daya koma fiye da haka bai sake bada ruwa ba duk da cewa da hasken rana yake aiki bada wutan lantarki ba. Wani abin ban haushi ma shine yadda manya da kanan yara ke dambe a wajen diban ruwan, wanda hakan kan haifair da jin raunuka da dama gasu yaran. Koda yake yin damben nasu nada dalili, domin wani bokitinsa takan kwana biyu ko uku a layi, amman lokaci daya wanda yafisu son zuciya sai yazo yace sai ya diba kafin su, wani lokaci kuma sukan tashi a tutan ma’aho. kai yanzuma kalilan daga cikin wadannan famfuna ke aiki. koda yake ana iya cewa nesa tazo kusa, domin kuwa mai girma Gwamna Namadi Sambo yabada kwangilar gyara ruwan Zariya don al'umma su samu saukin wannan hali na mawuyacin ruwa da suke ciki. to amman abin tambay shine: shin wadanda alhakin ya rataya akansu zasuyi aiki tsakani da Allah don kawo karshen wannan hali ganin cewa kusan shekaru goma kenen ake shelar cewa matsalar ruwa a Zariya zata zama tarihi amma har yau shiru akeji kamar Mallam yaci shirwa?
Don haka ya kamata gwamnatin jihar kaduna data karamar hukumar zariya suyi hubbasa wajen magance wannan fitina data addabi jama’ar nasu, ganin cewa ma yana daya daga cikin alkawuran da suka daukan masu yayin yakin neman zabe. Saboda wanna ruwa da ‘yan garuwa ke sayarwa, mafi yawancinsu bamasu kyau bane, kuma shan irin wadannan ruwan na iya haifar da barkewar wata cuta. (Amma bawai ina kashema yan garuwa kasuwa ne ba, a'a gaskiyar lamari ne, kuma nayi bayanin cewa bawai dukkansu ne keda ruwa mara kyau ba.)
Ya kamata mai girma gwamna alhaji namadi sambo, ya sake duba wadan nan famfuna da aka kafa masu aiki da hasken rana don su rika aiki yadda ya kamata, don kada yazamana anyisu amman babu amfani ganin cewa kudin al’umma aka dauka akayi aikin dashi, don haka yakamata suga amfanin yin aikin da dukiyarsu. Har ila yau, mai girma Gwamna yasa ido akan kwangilar aikin ruwan don kada marasa son ci gaban Zariya suyi kafan ungulu a aikin.
.Allah shiyi mana jagora a dukkan ayyukanmu na alhairi amin.
Duk dan adam yana da bukatan abubuwan more rayuwa na yau da kullum kamar su wutan lantarki, hanyoyin sufuri masu nagarta,da dai sauransu.amman saidai a yau akasin hakan ake samu. Koda yake, wasu ma ana iya cewa sun zama dole yin amfani dasu. Misali, koda yake ruwa ba’a ce dashi abin more rayuwa ba, amman dukkan mai numfashi na bukatansa a kulli yaumin domin sha, girki da kuma sauran ayyukan yau da kullum
Kash! Saidai labarin a birnin zariya ba haka yake ba. Domin kuwa ruwa ya zama dan gwal. Saboda a yau duk wanda yazo garin zariya daga wata garin, to babu abinda da zasu fara yi masa maraba face ‘yan garuwa. Wadanda suke sayar da ruwan nasu da dan karan tsada, kuma gashi wasu daga cikinsu ruwan nasu bawai yana da kyau bane. Wanda idan hakan ta daure, to nan gaba ba’a san abinda zai haifarba.
Koda yake wannan matsala na rashin ruwa a birnin zariya bawai sabon lamari ne ba, saidai kawai yadda rashin nasa yake dada tabarbarewa. Na tabbata duk yaron da ke zariya a yau, wanda shekarunsa basu wuce sha takwas zuwa ashirin ba, wallahi bai taba ganin ankawo ruwan famfo a gidansu ba. Wannan matsala kuwa ta wuce duk iya tunanin mutane, domin kuwa kamar yadda nace ne tun farko, al’amarin yana neman wuce gona da iri. Abin ban takaici ne yadda a yau yara kanana cikin dare suke fita ko kuma da subahin fari da sunan suna zuwa neman ruwan da iyayensu zasu yi masu abinci. Wanda hakan kan iya sa yaran shiga wani halin da bai dace ba.
A kwai bukatan hukumomi ko gwamnati data shiga cikin wannan lamari don kawo saukinsa ga al’ummar da suke yiwa shugabanci. Koda yake, mai girma gwamnan kaduna Alhaji Namadi Sambo, ya samar da famfuna masu aiki da hasken rana wadanda zasu iya aiki daga safe har zuwa la’asar ko ace yamma. Saidai labarin ba haka yake ba, domin kuwa famfunan sun zama abin adone kawai a birnin na zariya. Saboda idan famfon yabada ruwa na kamar sa’a uku a rana, to sai yayi kamar mako daya koma fiye da haka bai sake bada ruwa ba duk da cewa da hasken rana yake aiki bada wutan lantarki ba. Wani abin ban haushi ma shine yadda manya da kanan yara ke dambe a wajen diban ruwan, wanda hakan kan haifair da jin raunuka da dama gasu yaran. Koda yake yin damben nasu nada dalili, domin wani bokitinsa takan kwana biyu ko uku a layi, amman lokaci daya wanda yafisu son zuciya sai yazo yace sai ya diba kafin su, wani lokaci kuma sukan tashi a tutan ma’aho. kai yanzuma kalilan daga cikin wadannan famfuna ke aiki. koda yake ana iya cewa nesa tazo kusa, domin kuwa mai girma Gwamna Namadi Sambo yabada kwangilar gyara ruwan Zariya don al'umma su samu saukin wannan hali na mawuyacin ruwa da suke ciki. to amman abin tambay shine: shin wadanda alhakin ya rataya akansu zasuyi aiki tsakani da Allah don kawo karshen wannan hali ganin cewa kusan shekaru goma kenen ake shelar cewa matsalar ruwa a Zariya zata zama tarihi amma har yau shiru akeji kamar Mallam yaci shirwa?
Don haka ya kamata gwamnatin jihar kaduna data karamar hukumar zariya suyi hubbasa wajen magance wannan fitina data addabi jama’ar nasu, ganin cewa ma yana daya daga cikin alkawuran da suka daukan masu yayin yakin neman zabe. Saboda wanna ruwa da ‘yan garuwa ke sayarwa, mafi yawancinsu bamasu kyau bane, kuma shan irin wadannan ruwan na iya haifar da barkewar wata cuta. (Amma bawai ina kashema yan garuwa kasuwa ne ba, a'a gaskiyar lamari ne, kuma nayi bayanin cewa bawai dukkansu ne keda ruwa mara kyau ba.)
Ya kamata mai girma gwamna alhaji namadi sambo, ya sake duba wadan nan famfuna da aka kafa masu aiki da hasken rana don su rika aiki yadda ya kamata, don kada yazamana anyisu amman babu amfani ganin cewa kudin al’umma aka dauka akayi aikin dashi, don haka yakamata suga amfanin yin aikin da dukiyarsu. Har ila yau, mai girma Gwamna yasa ido akan kwangilar aikin ruwan don kada marasa son ci gaban Zariya suyi kafan ungulu a aikin.
.Allah shiyi mana jagora a dukkan ayyukanmu na alhairi amin.
Friday, February 27, 2009
GASKIYA DOKIN KARFE.
Dangane da bayanin dana yi a jaridar aminiya mai taken KAN BATUN RIBADU A TSAKA MAI WUYA, amman jaridar aminiya ta bashi taken dayafi dacewa dashi na HARYANZU INA GOYAN BAYAN RIBADU.kuma aka bugashi a jaridar ranar 20/2/09. a cikin kasidar dai na dada bayyana dalilan da sukasa nayi wancan rubutun mai taken RIBADU A TSAKA MAI WUYA wanda aka buga ranar 19/12/08, kuma shine silar yin wannan kasida na HARYANZU INAGOYAN BAYAN RIBADU sadoda irin korafe korafen da na rika samu daga wadanda sukakaranta waccar kasidar ta farko na ranar 19/12/09.
kamar yadda nasha fadi, gaskiya dai dayace, kuma daga kinta sai bata. gaskiya akace kuma dokin karfe ne. Nayi imani cewa ko bijima ko ba dade, gaskiya zatayi halinta domin Allah ba azzalumin kowa bane.
Nayi farin ciki matuga kan sakwannin waya dana samu wajen wadanda suka karanta wannar kasida na HARYANZU INA GOYON BAYAN RIBADU dakuma wadanda suka bugo waya don bayyana ra'ayinsu kan batun. Allal hakika sakwannin dana samu sun nuna cewa yan Nijeriya da dama sunyi tir da wannan halin tsangwama da akema mallam Nuhu Ribadu duk dacew ya bautawa kasar nan iya bakin kokarinsa. kodayake, ansami wasu kalilan da basu amince da yadda shi Ribadu yayi ayyukansa ba, dama ance ai daidan wani karkataccen wani. Komadai yane, ina matukar godiya ga dukkan wadanda suka dauki lokaci suka aiko da ra'ayinsu.
godiya ta musamman ga wadanda suka aiko da sakwannin waya kamar su Malam Ibrahim dan zariya mazaunin Lagos, Labaran Waziri Darazo, Abubakar Muh.A.K Zabi Auyakari giyade Bauchi mazaunin Jos, Auwal, Bashir Dikko Funtua, Sani Bandy B/Gwari, da sauransu.
har ila yau, ba zan manta da dukkan wadanda suka bugo waya ba kamar su Malam Abubakar Sani daga Kaduna, Wada Isa daga Kano, Idris Suleiman Plateau mazaunin Legos, Mahmud daga Kano, Kawu saleh daga Jos, Abubakar Moh'd daga Kebbi,
zanyi amfani da wanna dama in mika ban hakuri ga wadanda suka aiko da sako ko bugo waya amman basuga sunansu ba, suyi hakuri abin ne da yawa wai mutuwa ta shiga kasuwa. Wasu na manta sunansu da lambarsu, wasu kuma na kasa daukar sakon waya da suka aiko dashi har kuma sakon ya bace. Don Allah ayi hakuri saboda ayyukan sunada yawa.
Allah yayi mana jagora a dukkan ayyukanmu. wassalam.
kamar yadda nasha fadi, gaskiya dai dayace, kuma daga kinta sai bata. gaskiya akace kuma dokin karfe ne. Nayi imani cewa ko bijima ko ba dade, gaskiya zatayi halinta domin Allah ba azzalumin kowa bane.
Nayi farin ciki matuga kan sakwannin waya dana samu wajen wadanda suka karanta wannar kasida na HARYANZU INA GOYON BAYAN RIBADU dakuma wadanda suka bugo waya don bayyana ra'ayinsu kan batun. Allal hakika sakwannin dana samu sun nuna cewa yan Nijeriya da dama sunyi tir da wannan halin tsangwama da akema mallam Nuhu Ribadu duk dacew ya bautawa kasar nan iya bakin kokarinsa. kodayake, ansami wasu kalilan da basu amince da yadda shi Ribadu yayi ayyukansa ba, dama ance ai daidan wani karkataccen wani. Komadai yane, ina matukar godiya ga dukkan wadanda suka dauki lokaci suka aiko da ra'ayinsu.
godiya ta musamman ga wadanda suka aiko da sakwannin waya kamar su Malam Ibrahim dan zariya mazaunin Lagos, Labaran Waziri Darazo, Abubakar Muh.A.K Zabi Auyakari giyade Bauchi mazaunin Jos, Auwal, Bashir Dikko Funtua, Sani Bandy B/Gwari, da sauransu.
har ila yau, ba zan manta da dukkan wadanda suka bugo waya ba kamar su Malam Abubakar Sani daga Kaduna, Wada Isa daga Kano, Idris Suleiman Plateau mazaunin Legos, Mahmud daga Kano, Kawu saleh daga Jos, Abubakar Moh'd daga Kebbi,
zanyi amfani da wanna dama in mika ban hakuri ga wadanda suka aiko da sako ko bugo waya amman basuga sunansu ba, suyi hakuri abin ne da yawa wai mutuwa ta shiga kasuwa. Wasu na manta sunansu da lambarsu, wasu kuma na kasa daukar sakon waya da suka aiko dashi har kuma sakon ya bace. Don Allah ayi hakuri saboda ayyukan sunada yawa.
Allah yayi mana jagora a dukkan ayyukanmu. wassalam.
Monday, February 23, 2009
KARNUKAN 'YAN SANDA SUNFI TALAKA AMFANI!
Ci gaban ko wace kasa da kwanciyar hankali ya danganta ne kan irin tsaron da take dashi. Domin kuwa tsaro na daya daga cikin abubuwan dake kawo ci gaba a ko wace kasa. Duk kasar da babu cikakken tsaro a cikinta, la shakka wannan kasa na cikin fargaba da karuwar barayi da sauran masu aikata miyagun ayyuka.
Hakika hubbasar gwamnatin Nijeriya na sayo karnuka don baiwa rundunar yansanda domin kara inganta harkar tsaro abin a yabane matuka gaya. Domin kuwa hakan zai dada taimakawa jami’an tsaron durkushe ko wani irin gungu na barayi da kuma bata gari. Amma fa akwai alamar tambaya a cikin wannan lamarin. Domin kuwa kudin da gwamnatin tayi ikirarin cewa za’a sayo ko wani kare guda daya ya wuce daukar mai hankali, sannan ga kudin yin masa hidima a kowani ranar Allah ta’ala. Baya ga naira miliyan biyu a kan ko wani kare da za’a sayo, akwai kuma kudin ciyar dashi a kowani rana naira kusan dubu biyu koma fiye da haka. Kenan, kudin abincin ko wani kare a wata ya fi albashin wani dan sanda kenan. Lallai kam Allah ya kawomu wani zamani da a nijeriya dabba yafi dan adam daraja da kuma amfani a wajen gwamnatin kasa.
Alal hakika akwai bukatar gwamnatin nijeriya ta sake lale da kuma duba wannan kudi da aka ware don sayo karnukan nan wadanda akafi sani da POLICE DOG don kaucewa yin almubazzaranci da dukiyar jama’a. Domin kuwa hakan zaizama abin tir da kuma Allah wadai, ganin yadda talaka ke cikin kunci hali, tsadar rayuwa ga rashin ci sau uku a rana amma ace wai an dauki kudin talakawa wuri na gugar wuri har naira miliyan biyu don sayo ko wani kare guda daya.
Bawai wannan na nufin hubbasan da gwamnati keyi na sayo karnuka don inganta harkan tsaro bashi da kyau ba ne, a’a makudan kudin da akeson kashewa ne don sayo karnukan sukayi yawa, musamman ma ganin cewa akwai hanyoyi da yawa da za’a iya inganta harkan tsaro a kasarnana. Alal misali, akwai bukatar sayowa jami’an tsaro kayan aiki na zamani don samun yin gogayya da takwarorinsu na kasashen ketare dakuma samun damar yin ayyukansu ba tare da wani fargaba ba. Domin kuwa sama da kashi tamanin cikin dari na kayan aikinsu tsoffini kuma basu da inganci. Har ila yau, a kawi bukatar turasu yin kwasa-kwasai don kara gogewa da sanin makaman aiki (koda yake gwamnati ta soke zuwa kasahen waje don yin kwas-kwasai sakamakon faduwar darajar man fetur a kasuwar duniya) da dai sauransu. Don haka sayo karnuka ba tare daba jami’ai horon daya kamata ba tamkar yin aikin banzane domin kuwa kwalliya bazata biya kudin sabulu ba.
Waima abin tambaya shine, shin ya dace a kashe wadannan makudan kudin don sayo karnuka kawai? Zai yi kyau sosai idan aka sake duba kasafin da akayi don sayo wadannan karnuka,kuma gwamnati ta rika sara tana duban bakin gatari ba wai a fake da guzma a harbi karsanaba. A gayawa talakawa gaskiyar abinda za’ayi da kudinsu bawai sayo karnuka ba.
Hakika hubbasar gwamnatin Nijeriya na sayo karnuka don baiwa rundunar yansanda domin kara inganta harkar tsaro abin a yabane matuka gaya. Domin kuwa hakan zai dada taimakawa jami’an tsaron durkushe ko wani irin gungu na barayi da kuma bata gari. Amma fa akwai alamar tambaya a cikin wannan lamarin. Domin kuwa kudin da gwamnatin tayi ikirarin cewa za’a sayo ko wani kare guda daya ya wuce daukar mai hankali, sannan ga kudin yin masa hidima a kowani ranar Allah ta’ala. Baya ga naira miliyan biyu a kan ko wani kare da za’a sayo, akwai kuma kudin ciyar dashi a kowani rana naira kusan dubu biyu koma fiye da haka. Kenan, kudin abincin ko wani kare a wata ya fi albashin wani dan sanda kenan. Lallai kam Allah ya kawomu wani zamani da a nijeriya dabba yafi dan adam daraja da kuma amfani a wajen gwamnatin kasa.
Alal hakika akwai bukatar gwamnatin nijeriya ta sake lale da kuma duba wannan kudi da aka ware don sayo karnukan nan wadanda akafi sani da POLICE DOG don kaucewa yin almubazzaranci da dukiyar jama’a. Domin kuwa hakan zaizama abin tir da kuma Allah wadai, ganin yadda talaka ke cikin kunci hali, tsadar rayuwa ga rashin ci sau uku a rana amma ace wai an dauki kudin talakawa wuri na gugar wuri har naira miliyan biyu don sayo ko wani kare guda daya.
Bawai wannan na nufin hubbasan da gwamnati keyi na sayo karnuka don inganta harkan tsaro bashi da kyau ba ne, a’a makudan kudin da akeson kashewa ne don sayo karnukan sukayi yawa, musamman ma ganin cewa akwai hanyoyi da yawa da za’a iya inganta harkan tsaro a kasarnana. Alal misali, akwai bukatar sayowa jami’an tsaro kayan aiki na zamani don samun yin gogayya da takwarorinsu na kasashen ketare dakuma samun damar yin ayyukansu ba tare da wani fargaba ba. Domin kuwa sama da kashi tamanin cikin dari na kayan aikinsu tsoffini kuma basu da inganci. Har ila yau, a kawi bukatar turasu yin kwasa-kwasai don kara gogewa da sanin makaman aiki (koda yake gwamnati ta soke zuwa kasahen waje don yin kwas-kwasai sakamakon faduwar darajar man fetur a kasuwar duniya) da dai sauransu. Don haka sayo karnuka ba tare daba jami’ai horon daya kamata ba tamkar yin aikin banzane domin kuwa kwalliya bazata biya kudin sabulu ba.
Waima abin tambaya shine, shin ya dace a kashe wadannan makudan kudin don sayo karnuka kawai? Zai yi kyau sosai idan aka sake duba kasafin da akayi don sayo wadannan karnuka,kuma gwamnati ta rika sara tana duban bakin gatari ba wai a fake da guzma a harbi karsanaba. A gayawa talakawa gaskiyar abinda za’ayi da kudinsu bawai sayo karnuka ba.
Tuesday, February 17, 2009
DOLE TASA MUGABE YA BA TSVANGARAI PM
Bayan kai ruwa rana da aka dade anayi a rikicin siyasar Zimbabwe tsakanin jam’iyar adawa ta MDC da kuma shugaba Mugabe na zanu PF, a makon jiya ne aka cimma daidaito inda aka rantsar da Morgan Tsvangarai a matsayin prime minister ranar Alhamis 12/2/09 ,bayan ankwashe shekara guda ana neman hanyar sulhu da kokarin kafa gwamnatin hadin kasa. Rantsar da Tsvangarai a wannan matsayi yayi ma kasashen duniya da jama’ar Zimbabwe dadi matuka gaya, domin kuwa suna ganin haka wani mataki ne da zai kawo karshen mulkin kama karya na Mugabe (kamar yadda yan kasar suke ikirari) musamman ma ganin yadda kasashen yamma suka sakawa kasar takunkumi daban daban sakamakon rashin hulda mai nagarta da mugabe keyi da kasashen. Koda yake, a fili yake cewa dole tasa Mugabe ya amince da raba madafan ikon don ganin yadda yake dada samun matsin lamba daga kasashen duniya, ba wai don yanason yin hakan ba.
Zimbabwe dai ta shiga ko ace tana halin kaka na kayi kamar dai matsalar tattalin arziki, faduwar darajar kudin kasan, barkewar cututtuka da dai sauransu. Alal hakika wadannan matsaloli sune zasu zamo kalu balen sabon prime minister don ganin yaba da tasa irin gudun muwar wajen magancesu in har za’a sake masa mara yayi fitsari. Saidai kuma a wani bangaren, masana siyasa na ganin shigar Tsvangariai cikin gwamnatin hadin kasar bazata yi tasiri ba, musamman ma ganin yadda Mugabe ya dauke manyar mukamai kamar su ministan cikin gida, kasahen ketare, da dai sauransu yaba wa yan jam’iyarsa. Har ila yau, jam’iyar dai ta Mugabe ita keda yawan ministoci a cikin gwamnatin.
Koda yake jam’iyar Tsvangarai nada yawan kujerun majalisa, don haka wannnan wata damace ga shi don ganin ba’a tilasta masu bin dokoki ko ka’idojin da ba bisa hanya suke ba. Alal hakika, akwai bukatar Tsvangari ya rika sara yana duban bakin gatari akan aikinsa ganin cewa yana da kima a idon jama’ar kasar sa dama duniya baki daya ta fanin diflomaciyya. Kada ya zama dan amshin shatar Mugabe, domin kuwa kasashe da dama anyi irin wannan gwamnatin hadin kasa amman daga baya sai yan adawa su rikide su manta da akidarsu don neman kawai abin duniya.
Yin aiki tukuru da tsare gaskiya da amanar kasa sune kadai zasu dada kare mutunci da kimar sabon prime minister. Ya kamata ya nesanta kansa da dukkan wasu nau’i na almubazzaranci da dukiyar kasa. Wani babbban abin ban haushi da Allah wadai shine yadda Mugabe ya ware kudi wuri na gugar wuri har sama da dala miliyan dari uku wai don bukin tunawa da ranar haihuwarsa kawai! Wanna aiki da mai yayi kama? Koda yake wanna ba abin mamaki bane, domin kuwa duk shugabannin da suka hau mulki ta hanyar satan kuri’u da murdiya saboda karfin iko, basa tsinanawa talakawansu komai illa nakasa su. Lokaci yayi da shugabanni zasu yi karatun natsuwa ga maganar da shugaban amuruka Barack Obama yayi bayan an rantsar dashi inda yace “ al umma zasu rika tunawa da shugabanninsu kan abubuwan da suka gina masu ne bawai abinda suka lalata masu ba”. Ko shakka babu wannan zancen gaskiya ne, domin kuwa duk wanda yayi al mubazzaranci ko ya sace dukiyar talakawansa, la shakka bazasu taba mantawa dashiba, amman bawai don aikin alheri da yayi ba, a’a don lalata masu da salwantar da arzikinsu da yayi.
Yin kaka gida akan mulki yazama ruwan dare a nahiyar afrika, inda shugabanni keson dawwama a mulki har sai illa masha Allahu, kamar dai yadda ya faru a kasar Kenya-inda nan ma anyi dauki ba dadi tsakanin Kibaki da Odinga, kafin acimma daidai tuwa daga karshe. To yanzu ma hakanne ke faruwa a Zimbabwe don kuwa Mugabe ya rantse mutu ka rabasa da mulkin kasar domin kuwa yace Zimbabwe kasarce, don haka ba gudu ba ja da baya. Yanzudai zabi ya rage ga Tsvangarai na ko ya tsaya yayi aikin da zai ceto kasar daga cikin halin kuncin Da take ciki da kuma kawo sauyi ga salon mulkin kasar, ko kuma akasin hakan. Amman fa karya manta cewa, yanzu talakawan sa da sauran kasashen duniya sunsa masa ido suga irin kamun luddayin da zaiyi, don haka sai yayi duk mai yiwuwa yaba marada kunya.
Zimbabwe dai ta shiga ko ace tana halin kaka na kayi kamar dai matsalar tattalin arziki, faduwar darajar kudin kasan, barkewar cututtuka da dai sauransu. Alal hakika wadannan matsaloli sune zasu zamo kalu balen sabon prime minister don ganin yaba da tasa irin gudun muwar wajen magancesu in har za’a sake masa mara yayi fitsari. Saidai kuma a wani bangaren, masana siyasa na ganin shigar Tsvangariai cikin gwamnatin hadin kasar bazata yi tasiri ba, musamman ma ganin yadda Mugabe ya dauke manyar mukamai kamar su ministan cikin gida, kasahen ketare, da dai sauransu yaba wa yan jam’iyarsa. Har ila yau, jam’iyar dai ta Mugabe ita keda yawan ministoci a cikin gwamnatin.
Koda yake jam’iyar Tsvangarai nada yawan kujerun majalisa, don haka wannnan wata damace ga shi don ganin ba’a tilasta masu bin dokoki ko ka’idojin da ba bisa hanya suke ba. Alal hakika, akwai bukatar Tsvangari ya rika sara yana duban bakin gatari akan aikinsa ganin cewa yana da kima a idon jama’ar kasar sa dama duniya baki daya ta fanin diflomaciyya. Kada ya zama dan amshin shatar Mugabe, domin kuwa kasashe da dama anyi irin wannan gwamnatin hadin kasa amman daga baya sai yan adawa su rikide su manta da akidarsu don neman kawai abin duniya.
Yin aiki tukuru da tsare gaskiya da amanar kasa sune kadai zasu dada kare mutunci da kimar sabon prime minister. Ya kamata ya nesanta kansa da dukkan wasu nau’i na almubazzaranci da dukiyar kasa. Wani babbban abin ban haushi da Allah wadai shine yadda Mugabe ya ware kudi wuri na gugar wuri har sama da dala miliyan dari uku wai don bukin tunawa da ranar haihuwarsa kawai! Wanna aiki da mai yayi kama? Koda yake wanna ba abin mamaki bane, domin kuwa duk shugabannin da suka hau mulki ta hanyar satan kuri’u da murdiya saboda karfin iko, basa tsinanawa talakawansu komai illa nakasa su. Lokaci yayi da shugabanni zasu yi karatun natsuwa ga maganar da shugaban amuruka Barack Obama yayi bayan an rantsar dashi inda yace “ al umma zasu rika tunawa da shugabanninsu kan abubuwan da suka gina masu ne bawai abinda suka lalata masu ba”. Ko shakka babu wannan zancen gaskiya ne, domin kuwa duk wanda yayi al mubazzaranci ko ya sace dukiyar talakawansa, la shakka bazasu taba mantawa dashiba, amman bawai don aikin alheri da yayi ba, a’a don lalata masu da salwantar da arzikinsu da yayi.
Yin kaka gida akan mulki yazama ruwan dare a nahiyar afrika, inda shugabanni keson dawwama a mulki har sai illa masha Allahu, kamar dai yadda ya faru a kasar Kenya-inda nan ma anyi dauki ba dadi tsakanin Kibaki da Odinga, kafin acimma daidai tuwa daga karshe. To yanzu ma hakanne ke faruwa a Zimbabwe don kuwa Mugabe ya rantse mutu ka rabasa da mulkin kasar domin kuwa yace Zimbabwe kasarce, don haka ba gudu ba ja da baya. Yanzudai zabi ya rage ga Tsvangarai na ko ya tsaya yayi aikin da zai ceto kasar daga cikin halin kuncin Da take ciki da kuma kawo sauyi ga salon mulkin kasar, ko kuma akasin hakan. Amman fa karya manta cewa, yanzu talakawan sa da sauran kasashen duniya sunsa masa ido suga irin kamun luddayin da zaiyi, don haka sai yayi duk mai yiwuwa yaba marada kunya.
ZIYARAR SHUGAN KASAR SIN
ZIYARAR SHUGABA HU JIN TAO
La shakka ziyarar da shugaban kasar Sin Mista Hu Jin Tao yakai a wasu kasashe na nahiyar afrika don habbaka dangantakar kasuwanci tsakaninsu abin ayi maraba da shine matuka gaya. Alal hakika wanna ziyara tasa za taba kasashen dama bude sabon babi tsakani su da kasar ta Sin, musamman ma ganin cewa kasashen na Mali, Senegal, Tanzania da kuma Tsibirin Moroshiyos kasashene masu tasowa kuma wadanda basu da karfin tattalin arziki.
Wannan Mataki da shugaba Hu ya dauka duk da cigaba da tabarbarewar tattalin arzikin kasashen duniya, don dada habbaka huldar dangantaka tsakanisu wanda dama tuni suke huldar kasuwanci tare, ya samu karbuwa ga dukkan yan kasashen dama nahiyar afrika baki daya. Tabbas Mista Hu yayi kwakkwarar tunani na zaban wadannan kasashen don ganin sunyi huldar kasuwanci tare, duk kuwa da cewa kasar Sin kasa ce da taci gaba nesa ba kusa ba da wadannan kasahen.
Hakan kuwa zai kawo ci gaba ba karami ba ga akasashen in har duldar tasu tayi karko, dafatan sauran kasashe masu cigaban masana’antu da tattalin arziki zasu dada karfafa huldar cinikayyarsu da sauran kasashen afika don suma su samu su daga.
La shakka ziyarar da shugaban kasar Sin Mista Hu Jin Tao yakai a wasu kasashe na nahiyar afrika don habbaka dangantakar kasuwanci tsakaninsu abin ayi maraba da shine matuka gaya. Alal hakika wanna ziyara tasa za taba kasashen dama bude sabon babi tsakani su da kasar ta Sin, musamman ma ganin cewa kasashen na Mali, Senegal, Tanzania da kuma Tsibirin Moroshiyos kasashene masu tasowa kuma wadanda basu da karfin tattalin arziki.
Wannan Mataki da shugaba Hu ya dauka duk da cigaba da tabarbarewar tattalin arzikin kasashen duniya, don dada habbaka huldar dangantaka tsakanisu wanda dama tuni suke huldar kasuwanci tare, ya samu karbuwa ga dukkan yan kasashen dama nahiyar afrika baki daya. Tabbas Mista Hu yayi kwakkwarar tunani na zaban wadannan kasashen don ganin sunyi huldar kasuwanci tare, duk kuwa da cewa kasar Sin kasa ce da taci gaba nesa ba kusa ba da wadannan kasahen.
Hakan kuwa zai kawo ci gaba ba karami ba ga akasashen in har duldar tasu tayi karko, dafatan sauran kasashe masu cigaban masana’antu da tattalin arziki zasu dada karfafa huldar cinikayyarsu da sauran kasashen afika don suma su samu su daga.
Thursday, February 5, 2009
TRIBUTE TO GOV. MAMMAN BELLO ALI
To Allah we are and to him our return is! Gov Mamman Ali has been call to glory. That’s ordinary of human lives. He died when his contribution is highly needed in his state and indeed the country at large. We all believed that what God has destined to happen no human being on this earth can change it. While he lived, Mamman Ali was a cool headed unassuming person who gave everybody his due respect. A philanthropist, a man who stood for justice, fair play and equity. A hardworking and trustworthy. Yobe state and Nigeria has lost a great man.
It’s our earnest prayer that the almighty Allah will have mercy on him, together with all the muslims who died before him right from the time of prophet Adam (A.S). May he afford us the will and patience to pray for them and bless us with those who will pray for us when we die. We pray to almighty Allah to continue to give the family, relatives and friends the fortitude to bear the irreplaceable lost. We also pray that his gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.
It’s our earnest prayer that the almighty Allah will have mercy on him, together with all the muslims who died before him right from the time of prophet Adam (A.S). May he afford us the will and patience to pray for them and bless us with those who will pray for us when we die. We pray to almighty Allah to continue to give the family, relatives and friends the fortitude to bear the irreplaceable lost. We also pray that his gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.
TRIBUTE TO GOV. MAMMAN BELLO ALI
To Allah we are and to him our return is! Gov Mamman Ali has been call to glory. That’s ordinary of human lives. He died when his contribution is highly needed in his state and indeed the country at large. We all believed that what God has destined to happen no human being on this earth can change it. While he lived, Mamman Ali was a cool headed unassuming person who gave everybody his due respect. A philanthropist, a man who stood for justice, fair play and equity. A hardworking and trustworthy. Yobe state and Nigeria has lost a great man.
It’s our earnest prayer that the almighty Allah will have mercy on him, together with all the muslims who died before him right from the time of prophet Adam (A.S). May he afford us the will and patience to pray for them and bless us with those who will pray for us when we die. We pray to almighty Allah to continue to give the family, relatives and friends the fortitude to bear the irreplaceable lost. We also pray that his gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.
It’s our earnest prayer that the almighty Allah will have mercy on him, together with all the muslims who died before him right from the time of prophet Adam (A.S). May he afford us the will and patience to pray for them and bless us with those who will pray for us when we die. We pray to almighty Allah to continue to give the family, relatives and friends the fortitude to bear the irreplaceable lost. We also pray that his gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.
KAN BATUN RIBADU A TSAKA MAI WUYA!
A cikin watan disamban shekarar data gabata ne na rubuta wata kasida mai taken RIBADU A TSAKA MAI WUYA, kuma jarida Aminiya ta buga a ranar 19/12/2008. kasidar taja hankalin wadanda suka karanta ta da dama, domin kuwa wasu sun kira wasu kuma sun aiko da sakon waya suna masu bayyana ra'ayinsu dangane da kasidar. Alal hakika kowa nada yancin bayyana ra'ayinsa ko tofa albarkacin bakinsa kan lamuranyau da kullum, kamar yadda nima nayi ta hanyar rubuta wannan kasidar.
kusan dukkan sakonnin dana samu da kuma wadanda suka bugo waya, in banda kalilan daga cikinsu,sunyi tir ne da kuma Allah wadai da wannan kasida nawa suna masu cewa bani da tunani. wani bawan Allah cewa yayi "wallahi inajin dadin kasidunka dana ke karantawa , amman ban taba tunanin bakasan abinda kakeyi ba sai a wannan daka rubuta kan Ribadu da kake kiran talakawa wai suyi masa addu'a", wasu sunce dani dan koran Ribadu ne da dai sauransu.
kamar dai yadda nace ne daga farko, kowa nada yancin furta albarkacin bakinsa a kowani irin lamari domin a mulkin dimokaradiyya muke-Nidai bansan wannan bawan Allah (Ribadu) ba, haka shima bai sannin ba. Ban taba ganin sa ido da ido ba, kuma babu wata alaka tsakani na dashi, haka kuma banyi tunanin nan gaba wani abu zai hadani dashiba balle mu hada idanu da shi, don haka maganar cewa ni dan koransa ne duk bata taso ba. kuma bawai na rubuta wannan kasida bane don in faranta ma Ribadu rai ko magoya bayansa ba, a'a ni gaskiyan lamari ne kawai na fadi gwargwadon sanina.
ya kamata mu fahimci cewa gaskiya fa dayace kuma daga kinta sai bata-Ribadu yayi iya bakin kokarinsa, domin kuwa ya sadaukar da kansa da rayuwarsa ya bautawa Nijeriya, don haka inhar baza'a gode masaba, to bai kamata a tsine masaba. Hukumar EFCC karkashin jagorancin Ribadu a wancan lokaci bata ragama kowa ba komai girman mutum a kasar nan in har ankamasa da yin almubazzarancin da dukiyar al'umma, yayi aikinsa batare da nuna sanayyaba, wanda hakan ga dukmaison gaskiya yasan cewa shine adalci, bawai a kyale yan lele surika cin karensu babu babbakaba, wadanda basu da gata kuma a musguna masu. koda yake banyi mamakin masu irin wannan suka marasa ma'ana akan Ribadu ba, domin kuwa kashi casa'in cikin dari na wadanda suka aikomun da ra'ayinsu kan kasidar tawa manya mutane ne a kasarnar, wata kila aikin malam Ribadu ya shafi wasu nasu ne ko su kansu. Amman hakan bai kamata yasa murika take gaskiya mu maidata karya ba, kada son zuciya ta rika dibanmu murika kinyinma kanmu adalci akan lamuran yau da kullum.
Zaiyi kyau idan zamu rika yinma kanmu adalci idan mutum yayi aikin alhei a fadi, haka kuma idan yayi akasin hakan shima a fadi kuma a nuna masa yadda zai gyara. Tayin hakane kawai zamuci gaba bawai ta fadin son rai da suka marasa ma'ana ba. Koda yake, sanin kowane a yau babu wanda za’a nunasa ace dari bisa dari shi tsarkakakkene, ma’ana bai dadan kuskure tare dashi, don haka Ribadu kamar sauran mutane na iya yin kuskure yayin gudanar da aikinsa domin shi dan adamne kuma baifi karfin yin kura kurai ba, amma duk da haka bazaiyi kyau a garemu ba idan muka ce zamu boye ayyukan alheri dayayi a kasar nanba.
Alal hakika wannan hali da Malam Nuhu Ribadu ya shiga ciki abin kunya ne ga Nijeriya, ace mutane kamar su Ribadu wadanda suka sadaukar da rayuwarsu sukayi aiki tukuru an kasa saka masu da alheri sai aibantasu akeyi. Tababs wannna koma bayane ko shakka babu, gwamnatin nijeriya ta gaza wajen kare mutuncin Ribadu da kimarsa. Hakan kuwa manuniyace ga yan baya wadanda keda kudirin bautawa kasarnan da kada ko kusa suyi tunanin yin haka, domin suma nasu zata samesu kamar yadda ake cin zarafin Ribadu duk da irin gudunmuwar daya bayar wajen ci gaban kasrnan.
Hakika suma sarakuna da shugabannin arewa sun gaza matuka gaya kan rashin tsoma bakinsu kan wannan tsangwama da cin zarafi da akema Ribadu. Ya kamata shugabannin arewa suyi kokarin nemarmasa yancinsa na dan kasa kuma suyi kiran a gaggauta dakatar da wannan tsangwama da ake masa, don kare kimarsa a idon duniya. Abin bakin cikine yadda akasamu daya daga cikin shugabannin arewa ya fito fili yana nuna jin dadinsa kan halin da wannan bawan Allah yake ciki.
Daga karshe, zanjawo hankalin masu irn wadannan suka susan cewa bantaba yin kwai naba saida zakara, don haka ya kamata mu ajiye son zuciya a gefe, don samun cigaba. Har ila yau, bazan gaji da kira ga talakawa da masu murajin tabbatar da gaskiya da adalci a kasarnan ba da suci gaba dayin addu’a don Allah ya kubutar da wannan dan mutaliki, adali kuma haziki kan azzaluman mutanen da sukasa shi a gaba. Allah yayi mana jagora, amin.
kusan dukkan sakonnin dana samu da kuma wadanda suka bugo waya, in banda kalilan daga cikinsu,sunyi tir ne da kuma Allah wadai da wannan kasida nawa suna masu cewa bani da tunani. wani bawan Allah cewa yayi "wallahi inajin dadin kasidunka dana ke karantawa , amman ban taba tunanin bakasan abinda kakeyi ba sai a wannan daka rubuta kan Ribadu da kake kiran talakawa wai suyi masa addu'a", wasu sunce dani dan koran Ribadu ne da dai sauransu.
kamar dai yadda nace ne daga farko, kowa nada yancin furta albarkacin bakinsa a kowani irin lamari domin a mulkin dimokaradiyya muke-Nidai bansan wannan bawan Allah (Ribadu) ba, haka shima bai sannin ba. Ban taba ganin sa ido da ido ba, kuma babu wata alaka tsakani na dashi, haka kuma banyi tunanin nan gaba wani abu zai hadani dashiba balle mu hada idanu da shi, don haka maganar cewa ni dan koransa ne duk bata taso ba. kuma bawai na rubuta wannan kasida bane don in faranta ma Ribadu rai ko magoya bayansa ba, a'a ni gaskiyan lamari ne kawai na fadi gwargwadon sanina.
ya kamata mu fahimci cewa gaskiya fa dayace kuma daga kinta sai bata-Ribadu yayi iya bakin kokarinsa, domin kuwa ya sadaukar da kansa da rayuwarsa ya bautawa Nijeriya, don haka inhar baza'a gode masaba, to bai kamata a tsine masaba. Hukumar EFCC karkashin jagorancin Ribadu a wancan lokaci bata ragama kowa ba komai girman mutum a kasar nan in har ankamasa da yin almubazzarancin da dukiyar al'umma, yayi aikinsa batare da nuna sanayyaba, wanda hakan ga dukmaison gaskiya yasan cewa shine adalci, bawai a kyale yan lele surika cin karensu babu babbakaba, wadanda basu da gata kuma a musguna masu. koda yake banyi mamakin masu irin wannan suka marasa ma'ana akan Ribadu ba, domin kuwa kashi casa'in cikin dari na wadanda suka aikomun da ra'ayinsu kan kasidar tawa manya mutane ne a kasarnar, wata kila aikin malam Ribadu ya shafi wasu nasu ne ko su kansu. Amman hakan bai kamata yasa murika take gaskiya mu maidata karya ba, kada son zuciya ta rika dibanmu murika kinyinma kanmu adalci akan lamuran yau da kullum.
Zaiyi kyau idan zamu rika yinma kanmu adalci idan mutum yayi aikin alhei a fadi, haka kuma idan yayi akasin hakan shima a fadi kuma a nuna masa yadda zai gyara. Tayin hakane kawai zamuci gaba bawai ta fadin son rai da suka marasa ma'ana ba. Koda yake, sanin kowane a yau babu wanda za’a nunasa ace dari bisa dari shi tsarkakakkene, ma’ana bai dadan kuskure tare dashi, don haka Ribadu kamar sauran mutane na iya yin kuskure yayin gudanar da aikinsa domin shi dan adamne kuma baifi karfin yin kura kurai ba, amma duk da haka bazaiyi kyau a garemu ba idan muka ce zamu boye ayyukan alheri dayayi a kasar nanba.
Alal hakika wannan hali da Malam Nuhu Ribadu ya shiga ciki abin kunya ne ga Nijeriya, ace mutane kamar su Ribadu wadanda suka sadaukar da rayuwarsu sukayi aiki tukuru an kasa saka masu da alheri sai aibantasu akeyi. Tababs wannna koma bayane ko shakka babu, gwamnatin nijeriya ta gaza wajen kare mutuncin Ribadu da kimarsa. Hakan kuwa manuniyace ga yan baya wadanda keda kudirin bautawa kasarnan da kada ko kusa suyi tunanin yin haka, domin suma nasu zata samesu kamar yadda ake cin zarafin Ribadu duk da irin gudunmuwar daya bayar wajen ci gaban kasrnan.
Hakika suma sarakuna da shugabannin arewa sun gaza matuka gaya kan rashin tsoma bakinsu kan wannan tsangwama da cin zarafi da akema Ribadu. Ya kamata shugabannin arewa suyi kokarin nemarmasa yancinsa na dan kasa kuma suyi kiran a gaggauta dakatar da wannan tsangwama da ake masa, don kare kimarsa a idon duniya. Abin bakin cikine yadda akasamu daya daga cikin shugabannin arewa ya fito fili yana nuna jin dadinsa kan halin da wannan bawan Allah yake ciki.
Daga karshe, zanjawo hankalin masu irn wadannan suka susan cewa bantaba yin kwai naba saida zakara, don haka ya kamata mu ajiye son zuciya a gefe, don samun cigaba. Har ila yau, bazan gaji da kira ga talakawa da masu murajin tabbatar da gaskiya da adalci a kasarnan ba da suci gaba dayin addu’a don Allah ya kubutar da wannan dan mutaliki, adali kuma haziki kan azzaluman mutanen da sukasa shi a gaba. Allah yayi mana jagora, amin.
Subscribe to:
Posts (Atom)