THIS IS THE SITE OF MR.MUNTAKA ABDUL-HADI DABO,WHICH INCLUDES MY HISTORICAL BACKGROUND, SOME OF MY WRITE-UPS THAT ARE PUBLISHED IN THE NATIONAL DAILIES OF NIGERIA AND LOTS MORE...
Sunday, August 24, 2008
RIBADU’S DEMOTION: POLITICS OR WHAT?
On the continuation of this government to eliminate obasanjo loyalist, the police service commission (P.S.C) on Tuesday 05th August 2008, announced the demotion of the former EFCC boss Malam Nuhu Ribadu from Assistant Inspector General of police (AIG) to deputy commissioner of police on grounds that Ribadu did not attained the required courses that will grant him the position of AIG.
RAGEWA NUHU RIBADU MATSAYI: SIYASA KO ME?
A cigaba da tankade da reraya da wannan gwamnatin keyi wa makarraban tsohon shugaban kasa cif Obasanjo ne, hukumar harkokin ‘yan sandan nijeriya a ranar 5 gawatan augusta na wannan shekaran ta bada sanarwan ragewa tsohon shugaban hukumar EFCC malam Nuhu Ribadu, matsayinsa na mataimakin sufeto janar na ‘yan sanda zuwa matsayin mataimakin kwamishinan ‘yan sanda।
Malam Nuhu Ribadu wanda a farkon shekaranan ne gwamnatin kasar nan ta turashi kwas din dole a cibiyar manufofi da dabarun aiki dake kuru a jos, ganin cewa yakai matsayim mataimakin sufeto janar na ‘yan sanda ba tare da halattar kwasakwasan da suka kamata ba. Ribadu wanda ya zama shugaban hukumar EFCC na farko tun lokacin mulkin Obasanjo a lokacin yanada mukamin mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, ya rika samun Karin girma akai-akai har zuwa matsayin mataimakin sufeto janar din batare daya halacci kwas koda guda daya ba a cibiyar manufofi da dabarun aiki na jos ba. Hakan yasa ya rika samun bakin jini a wajen abokan aikinsa, ganin yadda likafansa ta daga a cikin dan lokaci kankani.
Hukumar harkokin ‘yan sanda ko kusa batayi wa malam Nuhu Ribadu adalci ba na rage masa matsayinsa, duk dacewa ya kai wannan matsayi bata hanyar daya daceba. Amman ganin cewa ya fara kwas din da zai halatta masa wannan matasayi nasa na mataimakin sufeto janar, tabbas ya kamata a kyaleshi da matsayin da Allah ya kaishi. Hakan kuwa dasu mahukuntan sukayi bawani abu bane illa siyasa, munafunci da cin amana, domin kuwa bayau ne malam Ribadu ya zama mataimakin sufeto janar ba, don haka me yahanasu kalubalantar wannan matsayi da cif Obasanjo ya bashi tun a wancan lokaci?
Wannan mataki da hukumar kula da harkokin ‘yan sanda ta dauka tabbas zai tilastawa Ribadu dawo wa daga kwas din da yakeyi. Domin kuwa a cewar sufeto janar na ‘yan sanda, masu mukamin kwamishina da fiye da wannan mukami ne kawai zasu iya halattar kwas a cibiyar manufofi da dabarun aikin dake jos. Amma shi sufeto yana mai cewa bazai ce Ribadu ya bar kwas din da yakeyi ba, domin mataimakin shugaban kasane keda hurumin yin haka. Koma dai wakeda hurumin kiran Ribadu nada yabar kwasdinsa, wannan Magana na sufeto ita da banza duk daya suke, domin kuwa kamar yadda yace ne masu mukanin kwamishina da fiye da hakane kawai zasu iya halattar cibiyar, don haka yanzu Ribadu a matsayinsa na mataimakin kwamishina mai zai hadasa da cibiyar?
Tun bayau ba, gwamnatin najeriya ke neman hanyar cin zarafin malam Nuhu Ribadu, inda da farko dai ancire shi daga shugabancin hukumar EFCC, sannan akazo akayi matsa kazafin mallakan gidaje na miliyoyin naira a Dubai da Abuja, a karshe hukumar kula da harkokin ‘yan sanda ta rage matsa mukaminsa, wanda hakan ga dukkan mai son adalci yasan ko kusa ba’ayi ma Ribadu adalci ba. Kodayake, malam Nuhu Ribadu ya tabka kura kurai lokacin aikin sa a karkashin tsohon shugaba Obasanjo, amman bai kamata a ce haryanzu ana kallonsa da wannan laifi da yayi ba, domin shi dan adam ne kuma baifi karfin yin kure a rayuwarsa ba. Abin ma dai tambaya a nan shine, wai malam Nuhu Ribadu shine kadai wanda gwamnati taga ya dace a rage matsa matsayin nasa? Ko dayake bashi kadai ne akayiwa wannan tsiyan ba, amman nasane yafi muni, kuma tabbas kowa yasan cewa Ribadu shine salsalan yin wannan tankade da rerayar da akayi ma ‘yan sanda saboda kawai anki jininsa.
Zaiyi kyau, idan gwamnati ta sake tunani akan matakin da ta dauka tare da hukumar kula da harkokin ‘yan sanda a kan malam Nuhu Ribadu na ganin anmaida masa da mukaminsa na mataimakin sufeto janar don kare masa mutuncinsa, kima da daraja a idon jama’a. shikuma mataimakin shugaban kasa Goodluck Jonathan ya nuna halin dattaku, kada ya dakatar da Ribadu daga kwas din da yakeyi a matsayinsa na wanda zai iya yin hakan. Kuma yayi duk mai yiwuwa don amaida ma malam Nuhu Ribadu mukaminsa, kamar dai yadda wasu mambobin kwamintin kula da harkokin ‘yan sanda na majalisar dattawa suka bukata hakan. Ya kamata tun yanzu ma gwamnati tasan cewa wannan matakin da suka dauka tare da hukumar kula da harkokin yan sanda haramtacciya ne, domin kuwa ko ina a cikin kasar nan harma da majalisar wakilai ta tarayya sai tur da tofin ala tine akeyi da wannan irin danyen matakin. Don haka wannan wani kwakkwarin dalili ne ma da yakamata gwamnati tayi amfani dashi wajen maidon da Ribadu kan mukaminsa, domin kuwa al’ummar kasan nan na kaunarsa. Wannan ne kawai gwamnatin zatayi ta kare kanta daga dukkan zargin da akeyi mata na hannu dumu dumu a wannan gurguwar matakin da aka dauka a kan malam Nuhu Ribadu.
Malam Nuhu Ribadu wanda a farkon shekaranan ne gwamnatin kasar nan ta turashi kwas din dole a cibiyar manufofi da dabarun aiki dake kuru a jos, ganin cewa yakai matsayim mataimakin sufeto janar na ‘yan sanda ba tare da halattar kwasakwasan da suka kamata ba. Ribadu wanda ya zama shugaban hukumar EFCC na farko tun lokacin mulkin Obasanjo a lokacin yanada mukamin mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, ya rika samun Karin girma akai-akai har zuwa matsayin mataimakin sufeto janar din batare daya halacci kwas koda guda daya ba a cibiyar manufofi da dabarun aiki na jos ba. Hakan yasa ya rika samun bakin jini a wajen abokan aikinsa, ganin yadda likafansa ta daga a cikin dan lokaci kankani.
Hukumar harkokin ‘yan sanda ko kusa batayi wa malam Nuhu Ribadu adalci ba na rage masa matsayinsa, duk dacewa ya kai wannan matsayi bata hanyar daya daceba. Amman ganin cewa ya fara kwas din da zai halatta masa wannan matasayi nasa na mataimakin sufeto janar, tabbas ya kamata a kyaleshi da matsayin da Allah ya kaishi. Hakan kuwa dasu mahukuntan sukayi bawani abu bane illa siyasa, munafunci da cin amana, domin kuwa bayau ne malam Ribadu ya zama mataimakin sufeto janar ba, don haka me yahanasu kalubalantar wannan matsayi da cif Obasanjo ya bashi tun a wancan lokaci?
Wannan mataki da hukumar kula da harkokin ‘yan sanda ta dauka tabbas zai tilastawa Ribadu dawo wa daga kwas din da yakeyi. Domin kuwa a cewar sufeto janar na ‘yan sanda, masu mukamin kwamishina da fiye da wannan mukami ne kawai zasu iya halattar kwas a cibiyar manufofi da dabarun aikin dake jos. Amma shi sufeto yana mai cewa bazai ce Ribadu ya bar kwas din da yakeyi ba, domin mataimakin shugaban kasane keda hurumin yin haka. Koma dai wakeda hurumin kiran Ribadu nada yabar kwasdinsa, wannan Magana na sufeto ita da banza duk daya suke, domin kuwa kamar yadda yace ne masu mukanin kwamishina da fiye da hakane kawai zasu iya halattar cibiyar, don haka yanzu Ribadu a matsayinsa na mataimakin kwamishina mai zai hadasa da cibiyar?
Tun bayau ba, gwamnatin najeriya ke neman hanyar cin zarafin malam Nuhu Ribadu, inda da farko dai ancire shi daga shugabancin hukumar EFCC, sannan akazo akayi matsa kazafin mallakan gidaje na miliyoyin naira a Dubai da Abuja, a karshe hukumar kula da harkokin ‘yan sanda ta rage matsa mukaminsa, wanda hakan ga dukkan mai son adalci yasan ko kusa ba’ayi ma Ribadu adalci ba. Kodayake, malam Nuhu Ribadu ya tabka kura kurai lokacin aikin sa a karkashin tsohon shugaba Obasanjo, amman bai kamata a ce haryanzu ana kallonsa da wannan laifi da yayi ba, domin shi dan adam ne kuma baifi karfin yin kure a rayuwarsa ba. Abin ma dai tambaya a nan shine, wai malam Nuhu Ribadu shine kadai wanda gwamnati taga ya dace a rage matsa matsayin nasa? Ko dayake bashi kadai ne akayiwa wannan tsiyan ba, amman nasane yafi muni, kuma tabbas kowa yasan cewa Ribadu shine salsalan yin wannan tankade da rerayar da akayi ma ‘yan sanda saboda kawai anki jininsa.
Zaiyi kyau, idan gwamnati ta sake tunani akan matakin da ta dauka tare da hukumar kula da harkokin ‘yan sanda a kan malam Nuhu Ribadu na ganin anmaida masa da mukaminsa na mataimakin sufeto janar don kare masa mutuncinsa, kima da daraja a idon jama’a. shikuma mataimakin shugaban kasa Goodluck Jonathan ya nuna halin dattaku, kada ya dakatar da Ribadu daga kwas din da yakeyi a matsayinsa na wanda zai iya yin hakan. Kuma yayi duk mai yiwuwa don amaida ma malam Nuhu Ribadu mukaminsa, kamar dai yadda wasu mambobin kwamintin kula da harkokin ‘yan sanda na majalisar dattawa suka bukata hakan. Ya kamata tun yanzu ma gwamnati tasan cewa wannan matakin da suka dauka tare da hukumar kula da harkokin yan sanda haramtacciya ne, domin kuwa ko ina a cikin kasar nan harma da majalisar wakilai ta tarayya sai tur da tofin ala tine akeyi da wannan irin danyen matakin. Don haka wannan wani kwakkwarin dalili ne ma da yakamata gwamnati tayi amfani dashi wajen maidon da Ribadu kan mukaminsa, domin kuwa al’ummar kasan nan na kaunarsa. Wannan ne kawai gwamnatin zatayi ta kare kanta daga dukkan zargin da akeyi mata na hannu dumu dumu a wannan gurguwar matakin da aka dauka a kan malam Nuhu Ribadu.
YINWA SOJOJI GARANBAWUL YA JAWO JUYIN MULKI A MAURITANIYA
Mauritaniya kasa ce wadda za’a iya cewa ta koma ta firkin dimokradiiya ne a shekaru biyu da suka wuce bayan halataccen zaben da aka yima Abdullahi Sidi ould cheikh. Kuma yaci gaba da jan ragamar mulkin kasan har farkon watan agusta na wannan shekara sa’ad da sojoji suka kifar da gwamnatin nasa.
Koda yake, sojojin sunbada dalilansu na kifar da gwamnatin na Abdullahi inda suka ce hambararren shugaban yana neman jefa kasar cikin wata mummunar rikicin siyasa da kuma rashin mutunta hafsoshin sojan kasar, ga kuma rashin iya gudanar da aiki yadda ya kamata. Dama dai, tuni su manyan dakarun kasar suka rika yi masa hannunka mai sanda kan yadda yake tafiyar da harkokin kasar da kuma yadda rikicin siyasa ya fara maimaye kasar, amman yayi kunnin uwar shegu dasu.
Takai a karshe ma inda shi hambararren shugaban yace yayi ma dukkan manyan hafsoshin tsaron kasar ritaya daga aiki batare da yaba da kwakkwaran dalilin yin hakan ba. Turkashi! Duk wanda yasan irin hubbasa da hafsoshi keyi dakuma irin gudunmuwar da suke bayar wa wajen kare al’umma da samar da tsaro a kasa ba zaiyi irin wannan makauniyar aiki da shugaba Abdullahi yayi ba.
Wannan mataki da shi Abdullahi ya dauka wanda kowa yasan cewa yayi babban kuskure, shine babban abinda ya tunzura sojoji yin juyin mulki a mauritaniya, inda sukace shugaba Abdullahi yanason kawo rudani a cikin harkan tsaron kasar. Wannan dai hali da hambararren shugaban ya sami kansa a ciki ana iya cewa shi ya tura kansa, domin kuwa gurguwar matakin daya dauka bata haifar masa da da mai ido ba.
Saidai kuma, sojojin dake jan ragamar mulkin kasar sunyi alwashin gudanar da zabe nan bada daewa ba ganin yadda majalisar dinkin duniya, kungiyar tarayyar afrika, da amurka (yar sandan duniya) da sauran kasashen duniya keta tir da wannan juyin mulkin daya gudana a mauritaniya.
Abinda za’ayi fata kawai shine, su sojojin dake jan ragamar kasar a halin yanzu su gudanar da zabe na adalci batare dayin magudi ba. Duk wanda ya sami nasara a bashi, kada suyi son zuciya su daura wanda suke ra’ayi akan mulki. Dafatan zasu gaggauta sako hambararren shugaban kamar yadda suka saki firamistan kasar.
Koda yake, sojojin sunbada dalilansu na kifar da gwamnatin na Abdullahi inda suka ce hambararren shugaban yana neman jefa kasar cikin wata mummunar rikicin siyasa da kuma rashin mutunta hafsoshin sojan kasar, ga kuma rashin iya gudanar da aiki yadda ya kamata. Dama dai, tuni su manyan dakarun kasar suka rika yi masa hannunka mai sanda kan yadda yake tafiyar da harkokin kasar da kuma yadda rikicin siyasa ya fara maimaye kasar, amman yayi kunnin uwar shegu dasu.
Takai a karshe ma inda shi hambararren shugaban yace yayi ma dukkan manyan hafsoshin tsaron kasar ritaya daga aiki batare da yaba da kwakkwaran dalilin yin hakan ba. Turkashi! Duk wanda yasan irin hubbasa da hafsoshi keyi dakuma irin gudunmuwar da suke bayar wa wajen kare al’umma da samar da tsaro a kasa ba zaiyi irin wannan makauniyar aiki da shugaba Abdullahi yayi ba.
Wannan mataki da shi Abdullahi ya dauka wanda kowa yasan cewa yayi babban kuskure, shine babban abinda ya tunzura sojoji yin juyin mulki a mauritaniya, inda sukace shugaba Abdullahi yanason kawo rudani a cikin harkan tsaron kasar. Wannan dai hali da hambararren shugaban ya sami kansa a ciki ana iya cewa shi ya tura kansa, domin kuwa gurguwar matakin daya dauka bata haifar masa da da mai ido ba.
Saidai kuma, sojojin dake jan ragamar mulkin kasar sunyi alwashin gudanar da zabe nan bada daewa ba ganin yadda majalisar dinkin duniya, kungiyar tarayyar afrika, da amurka (yar sandan duniya) da sauran kasashen duniya keta tir da wannan juyin mulkin daya gudana a mauritaniya.
Abinda za’ayi fata kawai shine, su sojojin dake jan ragamar kasar a halin yanzu su gudanar da zabe na adalci batare dayin magudi ba. Duk wanda ya sami nasara a bashi, kada suyi son zuciya su daura wanda suke ra’ayi akan mulki. Dafatan zasu gaggauta sako hambararren shugaban kamar yadda suka saki firamistan kasar.
Wednesday, June 4, 2008
TEN YEARS REMEMBRANCE OF LATE GENERAL SANI ABACHA
TEN YEARS REMEMBRANCE OF LATE GENERAL SANI ABACHA
june 8,2008, will exactly be 10years that Almighty Allah deemed it fit to take back the life of gen. Sani abacha.
the death of general abacha is a graet lost not only to his family, but to the entire nation-because he was a great patriot and a brave general who dedicated himself to the service of his country.
history will always remember general abacha as a hero who did his best for his country. we pray to Almighty Allah to continue to give the family, friends and well wishers the fortitude to bear the irreplaceable lost.
we also pray that your gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.
Abacha we are still with you in spirit and we love you, but God loves you more.
june 8,2008, will exactly be 10years that Almighty Allah deemed it fit to take back the life of gen. Sani abacha.
the death of general abacha is a graet lost not only to his family, but to the entire nation-because he was a great patriot and a brave general who dedicated himself to the service of his country.
history will always remember general abacha as a hero who did his best for his country. we pray to Almighty Allah to continue to give the family, friends and well wishers the fortitude to bear the irreplaceable lost.
we also pray that your gentle soul shall continue to abode in aljanna firdaus.
Abacha we are still with you in spirit and we love you, but God loves you more.
SHEKARA
SHEKAR GOME KENAN DA GWARZON NAMIJI YA KWANTA DAMA
Kwanci tashi babu wuya inji malam bahaushe। A ranar 8 ga watan yuni na wannan shekaran ne tsohon shugaban mulkin sojan kasarnan marigayi janar sani abacha ke cika shekara goma da rasuwa।
Alal hakika rasuwar janar abacha ya girgiza dukkan alahirin yan nijeriya, musamman ma ganin yadda a wancan lokacin yayi yun kurin farfado da tattalin arzikin kasan nan, da kuma biyan basukan da kasashen ketare ke bin mu, amman hakan batayiwu ba sai mai kowa mai komai ya dauki abinsa.
Duk dan nijeriya mai bibiyar yadda al’amurra suka rika kaiwa da komowa a wannan kasa lokacin mulkin marigayi janar abacha, yasan cewa shine shugaban da al’ummar nijeriya baza su taba mantawa da shiba. Domin kuwa a lokacin mulkin sane yayi shelar cewa duk kasashen ketare da ke bin kasarnan bashi za’a biyasu kuda densu ba tare da bata wani lokaci ba, amman saboda butulci, yaudara,mugunta da keta irin na nasara sai sukayi kememe suka ki amsar kudaden nasu wai saboda wa’adin da aka ba nijeriya na data biya wadannan basukan basu cika ba. Gashi a yau kuwa basukan sai kara karuwa sukeyi kuma da dukkan alamun babu ranar biyansu..
Har ila yau, janar abacha ya kasance shugaban nijeriya na farko da yaki bada kai bori ya hau ga kasashen yammacin turai da sauransu, musamman ma ganin yadda yafi mai da hankali ga kasashen afrika wajen gudanar da harkokin mulkinsa. Hakan kuwa yasa kasashe da dama suka rika sanya ma nijeria takunkumi, wai suna masu cewa tarayyar nijeriya nada shugaba mai mulkin kama karya. Wannan furuci nasu kuwa ba komai ya kawo shiba illa kin yarda da janar abacha yayi nadasu shigo kasar nan su rika cin karensu babu babbaka-kamar dai yadda labarin yake a yanzu, domin kuwa yanzu kowa yasan cewa kasashen yamma na taka rawa sosai kan yadda ake gudanar da mulki ko harkokin kasannan. Wanda a wancan lokaci janar abacha yaki yarda da hakan.
Saboda rashin fahimtar salon mulkin janar abacha, wasu yan nijeriya da dama suka bi sahun kasashen ketare wajen yin tir da gwamnatin nasa suna masu cewa wai kasarnan tana fama da talauci,yunwa ,rashin aikin yi, rashin tsaro da dai sauran korafe korafe da dama.
Da madai ance dan adan ba’a iya masa face ubangijin daya halicceshi, duk kokarin da marigayi janar abacha yayi a lokacin mulkinsa na ganin yan nijeriya sunji dadin wannan gwamnatin, duk jama’a basu ganiba sai tsinema mulkinsa aka rika yi ana Allah wadai da ita. Kodayake gaskiya tananan a gaskiyarta, domin kuwa a yanzu al’ummar kasannan sun fahimci irin hangen nesan da janar abacha ya rika yi da kuma irin gyara kasannan dayaso yayi. Domin kuwa yanzu sun dawo suna kewarsa.
Ba komai yasa suka gane hakan ba illa irin halin da suka tsinci kansu daga farkon shekarar 1999, wanda hakan yasa yan nijeriya yanzu sun gane cewa tabbas janar abacha gwarzon shugabane kuma mai kishin kasar san e da nahiyar afrika. Duk da irin tonon sililin da tsohuwar gwamnatin kasarnan ta rika yiwa iyalan janar abacha baisa yan nijeriya yin nadama da kewar da sukeyi na shi abachan ba, illa karamasu karfin gwuiwa. Domin kuwa kowa yasan kahon zukar da gwamnatin tasa ga iyalan janar abacha siyaye kawai, domin so suke su bata mas suna a idon duniya…dayake Allah ba azzalumin kowa bane sai gashi yau itama waccan gwamnatin data rika kwance wa iyalan janar abacha zani a kasuwa goguwar ya koma kanta, kuma dukkan abinda da akace ana zargin gwamnatin data shude haka yake babu ko tantama. Koda yake nasan yan nijeriya sunsan abinda nake nufi, kuma sune suka fi dacewa dasu fadi hakan don sunsan irin halin da suka tsinci kansu cikin shekaru takwas da suka gabata.
Daga karshe, babu abinda zamuce illa allah ya gafartama janar abacha, ya kyautata kwanci, yaba iyalansa da abokan arziki kara jure wanna babbar rashi, yasa aljanna firdaus makoma, mu kuma idan tamu tazo yasa mu cika da imani. Sukuma shugaban ninmu Allah yasa suyi kishi irin na marigayi janar abacha, kuma yabasu ikon sauke nauyin dake kasnsu.
Kwanci tashi babu wuya inji malam bahaushe। A ranar 8 ga watan yuni na wannan shekaran ne tsohon shugaban mulkin sojan kasarnan marigayi janar sani abacha ke cika shekara goma da rasuwa।
Alal hakika rasuwar janar abacha ya girgiza dukkan alahirin yan nijeriya, musamman ma ganin yadda a wancan lokacin yayi yun kurin farfado da tattalin arzikin kasan nan, da kuma biyan basukan da kasashen ketare ke bin mu, amman hakan batayiwu ba sai mai kowa mai komai ya dauki abinsa.
Duk dan nijeriya mai bibiyar yadda al’amurra suka rika kaiwa da komowa a wannan kasa lokacin mulkin marigayi janar abacha, yasan cewa shine shugaban da al’ummar nijeriya baza su taba mantawa da shiba. Domin kuwa a lokacin mulkin sane yayi shelar cewa duk kasashen ketare da ke bin kasarnan bashi za’a biyasu kuda densu ba tare da bata wani lokaci ba, amman saboda butulci, yaudara,mugunta da keta irin na nasara sai sukayi kememe suka ki amsar kudaden nasu wai saboda wa’adin da aka ba nijeriya na data biya wadannan basukan basu cika ba. Gashi a yau kuwa basukan sai kara karuwa sukeyi kuma da dukkan alamun babu ranar biyansu..
Har ila yau, janar abacha ya kasance shugaban nijeriya na farko da yaki bada kai bori ya hau ga kasashen yammacin turai da sauransu, musamman ma ganin yadda yafi mai da hankali ga kasashen afrika wajen gudanar da harkokin mulkinsa. Hakan kuwa yasa kasashe da dama suka rika sanya ma nijeria takunkumi, wai suna masu cewa tarayyar nijeriya nada shugaba mai mulkin kama karya. Wannan furuci nasu kuwa ba komai ya kawo shiba illa kin yarda da janar abacha yayi nadasu shigo kasar nan su rika cin karensu babu babbaka-kamar dai yadda labarin yake a yanzu, domin kuwa yanzu kowa yasan cewa kasashen yamma na taka rawa sosai kan yadda ake gudanar da mulki ko harkokin kasannan. Wanda a wancan lokaci janar abacha yaki yarda da hakan.
Saboda rashin fahimtar salon mulkin janar abacha, wasu yan nijeriya da dama suka bi sahun kasashen ketare wajen yin tir da gwamnatin nasa suna masu cewa wai kasarnan tana fama da talauci,yunwa ,rashin aikin yi, rashin tsaro da dai sauran korafe korafe da dama.
Da madai ance dan adan ba’a iya masa face ubangijin daya halicceshi, duk kokarin da marigayi janar abacha yayi a lokacin mulkinsa na ganin yan nijeriya sunji dadin wannan gwamnatin, duk jama’a basu ganiba sai tsinema mulkinsa aka rika yi ana Allah wadai da ita. Kodayake gaskiya tananan a gaskiyarta, domin kuwa a yanzu al’ummar kasannan sun fahimci irin hangen nesan da janar abacha ya rika yi da kuma irin gyara kasannan dayaso yayi. Domin kuwa yanzu sun dawo suna kewarsa.
Ba komai yasa suka gane hakan ba illa irin halin da suka tsinci kansu daga farkon shekarar 1999, wanda hakan yasa yan nijeriya yanzu sun gane cewa tabbas janar abacha gwarzon shugabane kuma mai kishin kasar san e da nahiyar afrika. Duk da irin tonon sililin da tsohuwar gwamnatin kasarnan ta rika yiwa iyalan janar abacha baisa yan nijeriya yin nadama da kewar da sukeyi na shi abachan ba, illa karamasu karfin gwuiwa. Domin kuwa kowa yasan kahon zukar da gwamnatin tasa ga iyalan janar abacha siyaye kawai, domin so suke su bata mas suna a idon duniya…dayake Allah ba azzalumin kowa bane sai gashi yau itama waccan gwamnatin data rika kwance wa iyalan janar abacha zani a kasuwa goguwar ya koma kanta, kuma dukkan abinda da akace ana zargin gwamnatin data shude haka yake babu ko tantama. Koda yake nasan yan nijeriya sunsan abinda nake nufi, kuma sune suka fi dacewa dasu fadi hakan don sunsan irin halin da suka tsinci kansu cikin shekaru takwas da suka gabata.
Daga karshe, babu abinda zamuce illa allah ya gafartama janar abacha, ya kyautata kwanci, yaba iyalansa da abokan arziki kara jure wanna babbar rashi, yasa aljanna firdaus makoma, mu kuma idan tamu tazo yasa mu cika da imani. Sukuma shugaban ninmu Allah yasa suyi kishi irin na marigayi janar abacha, kuma yabasu ikon sauke nauyin dake kasnsu.
Saturday, March 22, 2008
MATSALAN RUWA A BIRNIN ज़रिया: इन MAFITA
Duk dan adam yana da bukatan abubuwan more rayuwa na yau da kullum kamar su wutan lantarki, hanyoyin sufuri masu nagarta,da dai sauransu.amman saidai a yau akasin hakan ake samu. Koda yake, wasu ma ana iya cewa sun zama dole yin amfani dasu. Misali, koda yake ruwa ba’a ce dashi abin more rayuwa ba, amman dukkan mai numfashi na bukatansa a kulli yaumin domin sha, girki da kuma sauran ayyukan yau da kullum
Kash! Saidai labarin a birnin zariya ba haka yake ba. Domin kuwa ruwa ya zama dan gwal. Saboda a yau duk wanda yazo garin zariya daga wata garin, to babu abinda da zasu fara yi masa maraba face ‘yan garuwa. Wadanda suke sayar da ruwan nasu da dan karan tsada, kuma gashi wasu daga cikinsu ruwan nasau bawai yana da kyau bane. Wanda idan hakan ta adaure, to nan gaba ba’a san abinda zai haifarba.
Koda yake wannan matsala na rashin ruwa a birnin zariya bawai sabon lamari bane, saidai kawai yadda rashin nasa yake dada tabarbarewa. Na tabbata duk yaron da ke zariya a yau, wanda shekarunsa basu wuce shabiyar zuwa sha bakwaiba, wallahi bai taba ganin ankawo ruwan famfo a gidansu ba. Wannan matsala kuwa ta wuce duk iya tunanin mutane, domin kuwa kamar yadda nace ne tun farko, al’amarin yana neman wuce gona da iri. Abin ban takaici ne yadda a yau yara kanana cikin dare suke fita ko kuma da subahin fari da sunan suna zuwa neman ruwan da iyayensu zasu yi masu abinci. Wanda hakan kan iya sa yaran shiga wani halin da bai dace ba.
A kwai bukatan hukumomi ko gwamnati data shiga cikin wannan lamari don kawo saukinsa ga al’ummar da suke yiwa shugabanci. Koda yake, mai girma gwamnan kaduna alhaji namadi sambo, ya samar da famfuna masu aiki da hasken rana wadanda zasu iya aiki daga safe har zuwa la’asar ko ace yamma. Saidai labarin ba haka yake ba, domin kuwa famfunan sun zama abin adone kawai a birnin na zariya. Saboda idan famfon yabada ruwa na kamar sa’a uku a rana, to sai yayi kamar mako daya koma fiye da haka bai sake bada ruwa ba duk da cewa da hasken rana yake aiki bada wutan lantarki ba. Wani abin ban haushi ma shine yadda manya da kanan yara ke dambe a wajen diban ruwan, wanda hakan kai haifair da jin raunuka da dama gasu yaran. Koda yake yin damben nasu nada dalili, domin wani bokitinsa takan kwana biyu ko uku a layi, amman lokaci daya wanda yafisu son zuciya sai yazo yace sai ya diba kafin su, wani lokaci kuma sukan tashi a tutan ma’aho.
Don haka ya kamata gwamnatin jihar kaduna data karamar hukumar zariya suyi hubbasa wajen magance wannan fitina data addabi jama’ar nasu, ganin cewa ma yana daya daga cikin alkawuran da suka daukan masu yayin yakin neman zabe. Saboda wanna ruwa da ‘yan garuwa ke sayarwa, mafi yawancinsu bamasu kyau bane, kuma shan irin wadannan ruwan na iya haifar da barkewar wata cuta.
Ya kamata mai girma gwamna alhaji namadi sambo, ya sake duba wadan nan famfuna da aka kafa masu aiki da hasken rana don su rika aiki yadda ya kamata, don kada yazamana anyisu amman babu amfani ganin cewa kudin al’umma aka dauka akayi aikin dashi, don haka yaka mata suga amfanin yin aikin da dukiyarsu.
Amma daga karshe inason fa a fahimceni, bawai ina kashema ma ‘yan garuwa kasuwa ne, a’a gaskiyar lamarine nake fadi, kuma a baya ma nace bawai dukkansu ne ke da ruwa mara kyau ba.
Allah shiyi mana jagora a dukkan ayyukanmu na alhairi amin.
Kash! Saidai labarin a birnin zariya ba haka yake ba. Domin kuwa ruwa ya zama dan gwal. Saboda a yau duk wanda yazo garin zariya daga wata garin, to babu abinda da zasu fara yi masa maraba face ‘yan garuwa. Wadanda suke sayar da ruwan nasu da dan karan tsada, kuma gashi wasu daga cikinsu ruwan nasau bawai yana da kyau bane. Wanda idan hakan ta adaure, to nan gaba ba’a san abinda zai haifarba.
Koda yake wannan matsala na rashin ruwa a birnin zariya bawai sabon lamari bane, saidai kawai yadda rashin nasa yake dada tabarbarewa. Na tabbata duk yaron da ke zariya a yau, wanda shekarunsa basu wuce shabiyar zuwa sha bakwaiba, wallahi bai taba ganin ankawo ruwan famfo a gidansu ba. Wannan matsala kuwa ta wuce duk iya tunanin mutane, domin kuwa kamar yadda nace ne tun farko, al’amarin yana neman wuce gona da iri. Abin ban takaici ne yadda a yau yara kanana cikin dare suke fita ko kuma da subahin fari da sunan suna zuwa neman ruwan da iyayensu zasu yi masu abinci. Wanda hakan kan iya sa yaran shiga wani halin da bai dace ba.
A kwai bukatan hukumomi ko gwamnati data shiga cikin wannan lamari don kawo saukinsa ga al’ummar da suke yiwa shugabanci. Koda yake, mai girma gwamnan kaduna alhaji namadi sambo, ya samar da famfuna masu aiki da hasken rana wadanda zasu iya aiki daga safe har zuwa la’asar ko ace yamma. Saidai labarin ba haka yake ba, domin kuwa famfunan sun zama abin adone kawai a birnin na zariya. Saboda idan famfon yabada ruwa na kamar sa’a uku a rana, to sai yayi kamar mako daya koma fiye da haka bai sake bada ruwa ba duk da cewa da hasken rana yake aiki bada wutan lantarki ba. Wani abin ban haushi ma shine yadda manya da kanan yara ke dambe a wajen diban ruwan, wanda hakan kai haifair da jin raunuka da dama gasu yaran. Koda yake yin damben nasu nada dalili, domin wani bokitinsa takan kwana biyu ko uku a layi, amman lokaci daya wanda yafisu son zuciya sai yazo yace sai ya diba kafin su, wani lokaci kuma sukan tashi a tutan ma’aho.
Don haka ya kamata gwamnatin jihar kaduna data karamar hukumar zariya suyi hubbasa wajen magance wannan fitina data addabi jama’ar nasu, ganin cewa ma yana daya daga cikin alkawuran da suka daukan masu yayin yakin neman zabe. Saboda wanna ruwa da ‘yan garuwa ke sayarwa, mafi yawancinsu bamasu kyau bane, kuma shan irin wadannan ruwan na iya haifar da barkewar wata cuta.
Ya kamata mai girma gwamna alhaji namadi sambo, ya sake duba wadan nan famfuna da aka kafa masu aiki da hasken rana don su rika aiki yadda ya kamata, don kada yazamana anyisu amman babu amfani ganin cewa kudin al’umma aka dauka akayi aikin dashi, don haka yaka mata suga amfanin yin aikin da dukiyarsu.
Amma daga karshe inason fa a fahimceni, bawai ina kashema ma ‘yan garuwa kasuwa ne, a’a gaskiyar lamarine nake fadi, kuma a baya ma nace bawai dukkansu ne ke da ruwa mara kyau ba.
Allah shiyi mana jagora a dukkan ayyukanmu na alhairi amin.
Monday, January 7, 2008
सियासर AFURKA
A kullum akatashi yin Magana akan mulkin dimokradiyyar nahiyar afurka sai ace da ita jaririya. To wai yaushe ne zata girma? Ma’ana ta tashi daga jaririya zuwa mai hankali.
Alal hakika a nahiyar afurka anyi mummunar fahimtar abinda ake nufi da dimokradiyya. Koda yake bakomai ya haifar da haka ba illa rashin akidar kasa daya al’umma daya. Mafi yawancin yan siyasan yanzu sunfi maida hankali ne kan addini ko kabila kafin su nunawa duk wani mai neman madafun iko goyan baya. Wani abin muni ma shine yadda a nahiyar afurka aka maida mulkin dimokaraddiya gado. Saikaga dama kasauka, inma kasauka kana iya zaba ma al’ummar kasan wandan zai gajeka mai maikonsu su zabi wanda sukeso.
Koda yake, ina ganin katsalandan din da kasashen turawa sukeyi ga nahiyar afurka na daya daga cikin abubuwan dake haifar da rudani a nahiyar musamman ma dai ‘yar sandan duniya wato kasar amurka. Alal misali idan muka dauki kasar Kenya, wanda akema kallon uwa mabada mama akan sha’anin mulkin dimokradiyya amman a halin yanzu rikicin zaben da yasake ba shugaba Mwai KIBAKI wani wa’adin mulki ya dabaibayeta, zamu ga cewa mafi yawancin kasashen afurka basu amince da zabenba, amman kasar amurka itace kasa ta farko da ta taya shugaba KIBAKI murnan wai samun nasara da yayi, amma kuma daga baya tazo tace ta janye wannan taya murna data yiwa shi KIBAKI saboda annami manci irin na amurka.
Koda yake, ganin yadda al’amura ke sake yamutsewa a kasar ta Kenya, shugaba KIBAKI yasha alwashin gudanar da sabon zaben amman fa in har kotun kasar taki amincewa da sakamakon zaben, kamardai yadda tun farko abokin adawar nasa Raila Odinga ya bukaci da ayi. Amma ana iya cewa wannan furuci na KIBAKI zancen banzane domin kuwa shi yake da iko da kotunar kasar nasa, kuma zai iya tube duk alkalin da baiyi masa yadda yake so ba. Kamar dai yadda takwaransa na Pakistan yakeyi.
Idan muka duba nijeriya kuwa, wanda itama tayi fama da nata rikicin zaben shekarar da ta wuce, zamuga cewa duk kanwar jane. Domin kuwa duk da korafe korafen da masu sa ido na kasa da kasa sukayi cewa zaben na cike da magudi, amurka ita tafara taya mista yar’adua murna kan wai nasaran daya samu. Kai bada dadewa ba bayan kama madafun iko (mista yar’adua) aka gayyace shi taron G8, kana yakai ziyara kasashe da dama.
A kwanakin baya ne mista yar’adua yaki amincewa da sojojin hadin guiwan amurka wato AFRICOM amma nanda nan suka gayyaceshi zuwa kasar ta amurka inda suka kwaba masa kana ya amince. Aman bayan yadawo gida sai yayi amai ya lashe, domin kuwa yace waishi bai amince da bukatun na amurka ba.
Tabbas idan nahiyar afurka sukace wai komai kasashen yammaci dana turai ne zasu rika yanke masu iko, musaman ma kan batun zabubbuka domin duk sanda wata daga cikin kasashen yammaci turai musamman ma amurka tace ta amince da yadda akayi zabe, sai suma al’umman kasar su amince wai don kada a samasu takunkumi, to lashakka suna cikin mummunar tsaka mai wuya wanda kafin su fice daga cikinta sai sunyi da gaske.
Idan muka dubi kasar Pakistan kuwa, zamu ga cewa har ila yau ita dai wannan la’antacciyar kasar ne wato amurka ke daurewa shuga pervez musharraf gindi yake cin karesa ba babbaka. Domin kuwa ko kadan amurka batayi allah wadai da kisan gillar da akayi wa tsohuwar fira ministan kasar kuma shugaban adawa madam Bhutto ba, saboda shi shugaba musharraf yaron tane (amurka). Wani abin ban haushi shine yadda ita amurkan ke ikirarin yaki da ta’addanci,kuma shirye take ta taimakawa duk wata kasa dake da shirin yaki da ta’addancin. Amman sai gashi labarin yasha banban, domin kuwa wadanda suka kasha madam Bhutto sanannune, kuma ansan da zaman wadanda sukayi. Saidai kawai aki yin adalci wajen fidda sakamakon kwamintin dake bincike akan kisan.
To wai abin tambaya a nan shine, yaushe al’ummar nahiyar afurka zasu farka gada barcin da sukeyi ne don su san cewa fa kasashen nahiyar turai ba komai suke tsinana masu ba illa rigingimu da tashe tashen hankula. Kana basa basu wata gudunmuwar alheri sai dai idanfa sunga zasu ci riba da abinda suke basu. Yaka mata ga duk kasashen dake nahiyar afurka su game kansu wuri guda suyi bori ga wannan sansani da amurka keso ta kafa na AFRICOM a nahiyar. Tabbas, duk kasar da tabari akayi mata wannan sansanin, to saidai muce allah yakaresu daga sharrin amurka. Domin kuwa watarana za’ace suna da makamin kare dangi kamar yadda sukace wai kasar iraq nada shi, amman harsuka gama yakinsu da kasar koda makami daya na kare dangin da sukayi ikirarin iraq na dashi basu nunawa duniya ba.
Allah ya taimaki nahiyar afurka, yakuam hade kawunan shugabanin ta baki daya.
Alal hakika a nahiyar afurka anyi mummunar fahimtar abinda ake nufi da dimokradiyya. Koda yake bakomai ya haifar da haka ba illa rashin akidar kasa daya al’umma daya. Mafi yawancin yan siyasan yanzu sunfi maida hankali ne kan addini ko kabila kafin su nunawa duk wani mai neman madafun iko goyan baya. Wani abin muni ma shine yadda a nahiyar afurka aka maida mulkin dimokaraddiya gado. Saikaga dama kasauka, inma kasauka kana iya zaba ma al’ummar kasan wandan zai gajeka mai maikonsu su zabi wanda sukeso.
Koda yake, ina ganin katsalandan din da kasashen turawa sukeyi ga nahiyar afurka na daya daga cikin abubuwan dake haifar da rudani a nahiyar musamman ma dai ‘yar sandan duniya wato kasar amurka. Alal misali idan muka dauki kasar Kenya, wanda akema kallon uwa mabada mama akan sha’anin mulkin dimokradiyya amman a halin yanzu rikicin zaben da yasake ba shugaba Mwai KIBAKI wani wa’adin mulki ya dabaibayeta, zamu ga cewa mafi yawancin kasashen afurka basu amince da zabenba, amman kasar amurka itace kasa ta farko da ta taya shugaba KIBAKI murnan wai samun nasara da yayi, amma kuma daga baya tazo tace ta janye wannan taya murna data yiwa shi KIBAKI saboda annami manci irin na amurka.
Koda yake, ganin yadda al’amura ke sake yamutsewa a kasar ta Kenya, shugaba KIBAKI yasha alwashin gudanar da sabon zaben amman fa in har kotun kasar taki amincewa da sakamakon zaben, kamardai yadda tun farko abokin adawar nasa Raila Odinga ya bukaci da ayi. Amma ana iya cewa wannan furuci na KIBAKI zancen banzane domin kuwa shi yake da iko da kotunar kasar nasa, kuma zai iya tube duk alkalin da baiyi masa yadda yake so ba. Kamar dai yadda takwaransa na Pakistan yakeyi.
Idan muka duba nijeriya kuwa, wanda itama tayi fama da nata rikicin zaben shekarar da ta wuce, zamuga cewa duk kanwar jane. Domin kuwa duk da korafe korafen da masu sa ido na kasa da kasa sukayi cewa zaben na cike da magudi, amurka ita tafara taya mista yar’adua murna kan wai nasaran daya samu. Kai bada dadewa ba bayan kama madafun iko (mista yar’adua) aka gayyace shi taron G8, kana yakai ziyara kasashe da dama.
A kwanakin baya ne mista yar’adua yaki amincewa da sojojin hadin guiwan amurka wato AFRICOM amma nanda nan suka gayyaceshi zuwa kasar ta amurka inda suka kwaba masa kana ya amince. Aman bayan yadawo gida sai yayi amai ya lashe, domin kuwa yace waishi bai amince da bukatun na amurka ba.
Tabbas idan nahiyar afurka sukace wai komai kasashen yammaci dana turai ne zasu rika yanke masu iko, musaman ma kan batun zabubbuka domin duk sanda wata daga cikin kasashen yammaci turai musamman ma amurka tace ta amince da yadda akayi zabe, sai suma al’umman kasar su amince wai don kada a samasu takunkumi, to lashakka suna cikin mummunar tsaka mai wuya wanda kafin su fice daga cikinta sai sunyi da gaske.
Idan muka dubi kasar Pakistan kuwa, zamu ga cewa har ila yau ita dai wannan la’antacciyar kasar ne wato amurka ke daurewa shuga pervez musharraf gindi yake cin karesa ba babbaka. Domin kuwa ko kadan amurka batayi allah wadai da kisan gillar da akayi wa tsohuwar fira ministan kasar kuma shugaban adawa madam Bhutto ba, saboda shi shugaba musharraf yaron tane (amurka). Wani abin ban haushi shine yadda ita amurkan ke ikirarin yaki da ta’addanci,kuma shirye take ta taimakawa duk wata kasa dake da shirin yaki da ta’addancin. Amman sai gashi labarin yasha banban, domin kuwa wadanda suka kasha madam Bhutto sanannune, kuma ansan da zaman wadanda sukayi. Saidai kawai aki yin adalci wajen fidda sakamakon kwamintin dake bincike akan kisan.
To wai abin tambaya a nan shine, yaushe al’ummar nahiyar afurka zasu farka gada barcin da sukeyi ne don su san cewa fa kasashen nahiyar turai ba komai suke tsinana masu ba illa rigingimu da tashe tashen hankula. Kana basa basu wata gudunmuwar alheri sai dai idanfa sunga zasu ci riba da abinda suke basu. Yaka mata ga duk kasashen dake nahiyar afurka su game kansu wuri guda suyi bori ga wannan sansani da amurka keso ta kafa na AFRICOM a nahiyar. Tabbas, duk kasar da tabari akayi mata wannan sansanin, to saidai muce allah yakaresu daga sharrin amurka. Domin kuwa watarana za’ace suna da makamin kare dangi kamar yadda sukace wai kasar iraq nada shi, amman harsuka gama yakinsu da kasar koda makami daya na kare dangin da sukayi ikirarin iraq na dashi basu nunawa duniya ba.
Allah ya taimaki nahiyar afurka, yakuam hade kawunan shugabanin ta baki daya.
Thursday, December 13, 2007
TRIBUTE TO A MAN OF PEOPLE
Chief Sunday Awoniyi,has been called to glory. That is ordinary of human lives. The death of awoniyi is a great lost not only to the family,but to the entire nation. Yes! To the entire nation because he was a great patriot who dedicated himself to the service of humanity.
While he lived, awoniyi was a cool-headed unassuming person who gave everybody his due respect. A philanthropist, a man who stand for justice, fair play and equity.he was a lover of mankind. Awoniyi was complete gentleman,trustworthy and honest to the core. The family, indeed the nation has lost a very good man. The family,friends and well wishers he has left behind will fell the vacuum he has left.
But we all know that what Almighty God has destined we cannot change but we leave it to him to take care of his soul.His departrure no doubt will show the gap he must have left behind.
We pray to Almighty God to give the family,friends and well wishers the fortitude to bear the irreplaceable lost.
While he lived, awoniyi was a cool-headed unassuming person who gave everybody his due respect. A philanthropist, a man who stand for justice, fair play and equity.he was a lover of mankind. Awoniyi was complete gentleman,trustworthy and honest to the core. The family, indeed the nation has lost a very good man. The family,friends and well wishers he has left behind will fell the vacuum he has left.
But we all know that what Almighty God has destined we cannot change but we leave it to him to take care of his soul.His departrure no doubt will show the gap he must have left behind.
We pray to Almighty God to give the family,friends and well wishers the fortitude to bear the irreplaceable lost.
Subscribe to:
Posts (Atom)